← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 114

Sashe 33

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Satin da suka dawo kwana hudu tsakani aka soma shirin amsar lefen asma'un,ko ba'a fada ba mai karatu yasan waye a gaba idan ba hanci ba,tun ana sauran kwana biyu a kawo lefen aka hana ayshan tsugunnawa,tamkar wasu jinin hurul ini ne zasu zo haka ake tsara komai,a randa zasu zo din kuwa kayan masu kawo lefe kawai da aka hada abun a tsaya a kalla ne,komai cikin girma harma da nuna fariya a lamarin haka aka jibge musu kaya ana jiran isowarsu.

Tabbas hamid yayi lefe irin wanda ya dace da tsarin asma'u,akwati talatin ne cif,goma pink,goma purple,goma brown,kowanne danqare yake da sutura ta alfarma,sai kayan sakun lalle,kama ga buhunhunan shinkafa,suger gero da sauran kaya,'yan uwan asma'u kaman su taka rawa banda anty safiyya data kama kanta tun sanda taga yadda 'yan uwan hamid ke bubbuda hanci suna kallon ko ina da kowa d'ai d'ai,don ko zama ma basuyi ba atsaye akayi komai,tukuicin kuwa da aka basu cewa sukayi sun gode basu amsa ba,wanda kana ganin yadda sukayi din sun raina ne,saidai da anty safiyyan ta fada asma'un rigima ta saka tace dama can bata qaunarta ita da hamid shine yanzu zata yiwa 'yan uwanshi sharri,ita ta rasa me yasa tana 'yar uwarta bata qaunarta,ta lura da da hali canzata zatayi da ayshan don ta lura tafi sonta da ita,sai abun yaso ya koma kaman ashan ce tayi da yake tafi rainata akan kowa,shuru kawai tayi musu daga qarshe saboda yadda taga sun dauki zancan tsakanin asma'un dasu anty halima,babu ma wanda ya kula da abinda ita tace ta hango din,duk idanunsu ba wannan yake kalla ba,abinda kawai suka dubawa dukiyar da aka jibgowa asma'un.

A sannan aysha na falon ta zuba ma anty halima da anty kubra abinci ta aje musu,saboda basu tafi ba har isha'i suna falon suna hirar yawan kayan da kyansu tare da yi musu d'ai d'ai suna sake kalla,tana shirin juyawa anty kubra tace
"Ke yaushe ne kawo naki lefen?naji har yau baki ce komai ba" Kanta a qasa tana murza tafin hannunta tace
"Idan zai kawo din zai fada.....dama ya riga daya gayamin zaiyi bakin qoqarinsa ne idan sun samu,saboda ranar bikin da aka sama tayi mishi gajartar da zai iya shiryawa a tsukin" wani mugun tsaki anty halima ta saki sanda take kai lomar abincin bakinta
"Kema kubra da neman magana kike wallahi.....har wani lefe kike jira a kawo mata....saikiyita jira ai....ke tashi ki bamu waje" ta fada tana hade rai gami da kafeta da ido,asma'u dake zaune gefe ta samu nayi,dariya ta dinga harda qyaqyatawa
"Yaron oga ne fa,sai abinda oga ya gutsuro ya bashi da shi zaiyi hidiman bikin,ku bishi dai a hankali kar ya fece,dai dai ruwa dai dai qurji"
"arziqi da talauci dai duka na Allah ne,kuma zaman lpy da mutunta juna ake nema ba tarin dukiya ba"cewar anty safiyya aysha ta jiyota tana fada,a sannan tuni ta isa qofar kitchen tayi shigewarta abinta,itakam ko cikin tunaninta bata wani saqa zancan lefe,mata masu 'yanci suke bidar lefe,ita wani abu ne ya rage mata,sam bama shine damuwarta ba a yanzu.

Washegari da daddare daddy na falonshi zaune ana nuna masa kayan,asma'un na zaune gefenshi suna kallo tare,duban mummy yayi
"Banga aishatu ba yau....ina tayi ne?" Baki mummyn ta tabe
"Allah dai ya kusa raba yari da barawo" ta furta a ranta
"Tana ciki.....ka santa gwanar zama a daki sam batason zaman falo bansan me ya sa ba" asma'u ya kalla
"Jeki kira min ita" hakanan ba don taso ba ta miqe ta tafi kiran ayshan,sanda taje ayshan na kwance rub da ciki saman gadonta tana karanta wani littafin addu'o'i,ta qara yawan haddar addu'o'inta sosai saboda kariya da ingantuwar tata rayuwar
"Saiki taso kizo....kwarkwasa fidda mai giji" ta fada tana watsa mata harara sannan ta juya ta koma,a nutse ta miqe ta sanya hijabinta sannan ta zura slippers ta fito.

Cike da nutsuwa tayi sallama hannunta dauke da jug na glass wanda ke cike da lemon guava data hadashi dazun nan,fuskar daddyn ce kawai qunshe da murmushi,ta isa gabanshi ta aje cikin nutsuwa
"Daddy sannu da hutawa"
"Yauwan indon baffale....sannu kadai" ya furta yana duba jug din
"Yau kuma me na samu?" Murmushi ta saki tana sunkuyar da kanta sanda take komawa da baya tana lalubar mazauni,da kanshi ya zuba sannan ya soma kurba yana kallon kayan da asma'u ke dagawa daya bayan daya,ganin shuru daddyn baiyi magana ya sanyata fara yunqurin miqewa a zatonta ba wani abu bane sai ya dakatar da ita har sai da suka gama kallon kayan tsaf,duk da aysha jifa jifa take daga kai ta kalla ta maida kanta qasa ta saddar.

"Ma sha Allah....yanzu sai biki kenan gaba daya ran ashirin ga wata" dif sukai daga mummyn har asma'un saboda anzo wajen,anzo wajen da ba zasu yarda daddy ya hada musu biki da ayshan ba,ko komai sun daure basa jin zasu haqura da wannan din
"Daddy" aysha ta kirashi cikin sanyin nan nata
"Na'am aishatu..."
"Daddy don Allah ina neman alfarma..."
"Tame indo?" Dan jim tayi kadan sannan tace
"Ina neman alfarmar idan babu damuwa a qyale anty asma'u tayi nata bikin ashirin ga wata din...ni ranar litinin din da aka gama bikinta ina son na tafi qauye ayi nawa bikin a can,daddy......" sai kuma ta danyi jim
"Inason idan an tashi daukoni a daukoni daga tushena...inda na girma na kuma rayu a can".

Shiru daddy yayi yana auna kalamanta,yarinyar nada nutsuwa sanin da kamata,ya tabbata da wata ce cikin 'yammatan zamanin nan masu son abun duniya son qyale qyale da qyamatar tushe babu abinda zai sanyasu yin zancan asalin nasu ma bare akai ga batun zuwa can biki
"Kin tabbatar haka kikeso,baki kuma da matsala da hakan?" Daddy ya tambayeta yana dubanta
"Eh daddy.." Ta fada tana gyada kai alamun tabbatarwa
"Shikenan to,babu damuwa" kanta ta duqar qasa
"Na gode daddy...Allah ya saka da alkhairi ya qara girma"
"Amin amin aishatu" ya amsa yana jin dadin addu'o'inta,ficewa tayi ta barsu a nan.

Tana shirin tada sallar wutiri bayan ta gama shafa'i wayarta ta dauki tsuwwa,dakatawa tayi don bata riga ta tayar din ba ta duba mai kiran,Aliya ta gani...take hannunta ya fara kakkarwa tana kokawar daga kiran kamar wadda ke dambe da wani tsabar rudewa da jin dadi,lallai Aliyar tazo mata a dai dai sanda tafi buqatarta fiye da kowanne lokaci
"Aliya.."
"Aysha" suka kira sunan juna a tare,qatuwar ajiyar zuciya aysha ta sauke,sannan cikin mutuwar jiki ta koma gefan gadonta ta zauna tana cewa
"Haba Aliya...haba..ya zakimin haka don Allah fisabilillahi.....bayan kinsan duk duniya bani da abokin shawara..kin tafi a lokaci mai tsada da muhimmanci a rayuwata kinyi dif kamar baki duniya...?" Ta qarashe fada lafuzanta na bayyana tsantsar damuwar dake maqare a zuciyarta
"Kiyi haquri sashin...wallahi dake nake kwana nake tashi...saboda ke naqi zama a nijer,kin ganni shigowata gida kenan ko zama wallahi Allah banyi ba na soma da kiranki....gayamin meke faruwa?"ajiyar zuciya ta sauke,cikin karaya tace
"meye ma bai faru ba,babu abinda ma bai faru ba sashin" idanu Aliya ta zaro kamar tana wajen cikin fargaba
"Me ya faru dake 'yar uwa gayamin"
"Wai aure zanyi,aure na ya kusa"
"Kaman yaya?,how comes?...labarin daya cancanci ace ni zan bada shi ni ake baiwa....aysha ban fahimceki ba....wanne irin aure?ina fatan babu cutarwa a ciki" dan qaramin murmushi daya fidda sauti ta saki,duk da cewa tsoro fargaba da alhini ne danqare a qasan zuciyarta
"Maganar tafi qarfin waya Aliya.....idan kin samu lokaci kyazo"
"Wanne lokaci ne zan samu?...ki jirayeni gobe da sassafe in sha Allahu"
"Allah ya nuna mana....ki gaida mama"
"Zata ji" da haka sukai sallama,aysha ta jima zaune riqe da wayar tana kallonta,jifa jifa tana sauke ajiyar zuciya,haka kawai take jin nauyin da take ji a qirjinta ya dan ragu duk da bata ce komai ba,lallai ba shakka rashin abokin shawara(aboki na gari mai addini) ba qaramin nakasu bane a rayuwar mutum.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*KO KUMA*

07067124863

*DB*

21

Goma na safiya ta kammala duk abinda take,saboda ta sani tsaf zata iya ganin Aliya a lokacin,cikin dakinta ta zauna tana 'yan gyare gyaren da suke maganin zaman banza da kuma hana kai tunani,don babu wani abu qwaya daya dake buqatar gyara cikin dakinta,tana da bala'in tsari komai nata a jere yake daki daki,tana da tsafta komai nata kal yake kaman ba'a zama cikin dakin,tun da can tana da son tsafta,koda bata da sabulun wanki ko wanka,haka zata dibi toka tayi wanka,ta sake saka tokar ta sabe kayan sawarta duk da cewa ba wai fita suke ba amma tana rage dauda,kuma tana jin dadin sanyasu a jikinta a hakan.

Sha daya na safe wayarta dake aje gefanta ta dauki ringing,da sauri ta duba aliya ce
"Ina bakin gate zo ki shigo da ni..."haka ta fada mata,yawancin lokuta indai tazo din ayshan take kira tazo ta shiga da ita duk don kada wai su hadu da asma'u tayi mata kallon banza da wofi,don ba qyaleta zata yi ba.
Chapter 33 · 0% Book details