Sashe 37
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ginin qasa ne wanda yasha shafen sumunti da makuba,qofar katako irin ta da ta katako sosai maqale da katangar gida wanda ke nuna ta nan zaka shiga zuwa ainihin gidan,kallo daya zaka yiwa gidan kasan cewa ba sabon gini bane,kowanne idanunsa kan gidan suka isa bakin qofar,asma'u ce ta dubi dan rakiyar
"Kaga malam basai kayi wahalar saka muqulli ka bude wannan rubabbiyar qofar ba,da qafa ma budeta zamuyi" ta qarasa fada tana daga qafarta ta daki qofar,qasa da qura suka biyo qofar suka yo kanta,hakan ya sanya tayi saurin ja da baya,ita kanta mamaki take cikin zuciyarta,sam batayi tsammanin talaucin yaron oga yakai har haka bama,wani bacin rai ya sake lullubeta da haushinsa,yasan haka yake har ya zubda mata ajinta ta jera da shi?,ta hada muhallin zama da shi,lallai iya zaman da yasa tayi da shi ba qaramar cutarta ma yayi ba,batasan mutane nawa ne da suka santa suka kuma sanshi suka gansu tare ba,ta tabbata wasu sun mata dariya.
Da qyar ya iya samu qofar ta bude ya tura kai ciki suka biyo bayanshi,tsukakke kuma dogon soro suka fara taraswa mai dauke da rufin azara irin ta da,idan kaci gaba da jumurin cusa kai zuwa cikin gidan kuwa,tsakar gida ne mai fadi da yalwa wanda aka yiwa daben qasa,duqurqushin bandaki jere kusa da kitchen,sai dakuna manya falle biyu
"Ummm....indo ba'a manta gida ba" cewar anty halima,daga kai kawai inna laraba tayi ta kalleta ta dauke kanta....wato shi dan qauye ba mutum ba?...tana da yaqinin harga Allah daddy baisan duka wainar da ake toyawa ba,duk da cewa bata gidan amma tana katarin riskar wasu abubuwan,ta yaya aysha yarinyar da tayi jami'a take zaune cikin birni shekara da shekaru zatayi aure cikin wannan gidan ta kuma zauna a ciki?,ta ina zata iya taimakawa rayuwarta ta fidda ta?
"Hhhhhh,ai tazo inda ya dace da ita" cewar asma'u tana yarfa hannu tare da takawa cikin gidan tana qare masa kallo.
Ba abinda dan rakiyar yace saboda ba'a umarceshi da cewa komai ba,kuma ya tabbatar duk abinda ke wakana boss din sa yana ji kuma yana gani,bai furta komai din ba har suka gama isgilancinsu suka gama suka tako zasu fita ya rufa musu baya,yana maida muqullin zai rufe asma'u ta dubeshi
"Kana wahalar da kanka ne kawai....banda abinka wai meye abun qwaqumawa wannan kangon kwado kayita wani rufeshi,da ka barshi ma a bude don baida maraba da kango" kallo daya yayi mata ya maida kansa yana ci gaba da ruge gidan,ranshi fal da mamakin me ya hada boss da wannan gidan me zaiyi da shi?,sannan kuma meye gaminsa da wadan nan matan?,ko da ya gama rufe gidan tuni sun hau kwalta sunyi gaba abinsu.
Cikin motar ma zancan gidan sukeyi,kowa na tofa albarkacin bakinsa,anty lubabatu ce tace
"Anya ko asma'u wannan plan din baiyi worst ba....talaucin mutumin nan fa kamar yayi yawa" dan tsaki ta ja saboda sakuwarta ce
"Kinjiki kema da wani irin zance....to daga ina ita din ta fito?....ina cewa irin wannan gidan anan taci ta sha,banda ma tsaurin ido irin na talaka daga an riqeka a waje sai kace lallai sai kayi rayuwa irin tasu?,kuma wa ya hanata musanta zancan tun yana farkonshi...wai ita saliha a dole baiwar Allah.....munafuka inaga ma kyanshi ta gani ta kasa cewa bata sonshi....so ni banga wani worst ba da yayi,ungulu ce kawai zata koma gidanta na tsamiya" tabe baki anty halima tayi,sai a sannan tayi magana
"Lubabatu a yadda yarinyar nan take gani tana da kyau idan ta auri wani kan mage ne zai waye,uban kowa ma neman taka shi zatayi,irinsun nan ki gansu haka haka ba qananun 'yan iska bane idan suka samu waje...Allah ne kadai yasan manufar jaki da bai bashi qaho ba....daddy nema haka kawai ba dangin dangiro kaje ka jajubo yarinyar mutane....ta gama abinda ya kawotan ma maimakon ka maidata a'ah ka daukama ranka saika aurar da ita....bayan ko uwarta bata ta tata saikai" ta qarashe maganar da tsaki
"Shi yasa nakesonki anty halima....kinfi kowa fahimta"
"Mu ai da yake jakai ne ko?" Lubabatu ta fada tana hararta,dariya tayi tana cewa
"Bance ba".
Nannuyar ajiyar zuciya ya saki ya soma latsa system din bayan ya gama gani da jin duk abinda ya gudana tun daga qofar gidan shigarsu ciki zuwa barinsu unguwar,tunani ne cikin qwaqwalwarsa kala daban daban,mamakin baqar zuciya da mugunta irin ta wasu mutanen,buri da fatan jefaka a rana koda baka takawa kowa komai ba,aysha dai aysha ba'a son ci gabanta a rayuwa kwata kwata?,shikam wanne irin gata zaiyi mata daya dace da ita wanda zai bada mamaki ya girgiza zukatan maqiya
[1/14, 1:37 PM] Om Muhammadiyya: Mamakin abinda aysha tayi wanda ya tsarewa asma'u a rai yake,me tayi mata mai zafi da taketa yunqurin daqile duk wani ci gabanta,wacce irin macace asma'un?,bama ita kadai ba,hatta da 'yan uwanta ya fuskanci haka suke,ta ina suka gado wannan halayya?,wato da da gaske shi din haka yake zasu fi kowa farincikin dawwamarta cikin wahala kenan?.
Kusan wunin ranar baki daya abinda ke masa kai kawo kenan a zuciya,har sanda yake zaune gaban anni yake cin abinci abunda ke tsinkulinsa kenan
"Muhammadu lafiya dai?gajiya ko kuma aikin?" Dan murmushi yayi sannan a nutse ya bata labarin dukkan abinda ya faru,kai take jinjinawa cike da mamaki da.nazari
"Muhammadu yarinyar nan tana buqatar wani ginshiqi da zai tallafeta....inama ace kana mata soyayya mai qarfi wadda zata zame mata jigo?....saidai duk da haka ina jin qaunar zama da ita...sai nake jin kamar a maida daurin auren gobe ka dauketa daga cikinsu,me yasa mutane zuciyoyinmu suke ciki da kishi qyashi da hassada?...Allah ka shiryamu ka gyara mana zukatanmu"ta furta cikin sanyin jiki
"amin ya Allah....amin"
_kuyi haquri da wannan don Allah_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*DB*
23
Tunda suka dawo babu zancan da suke sai na gidan ayshan mommy na ji bata dai tanka komai nata ciki ba,a sannan anty safiyya ta dawo daga kai al'amin asibiti,ganin ta gama da wuri sai ta zarto gida,nan ta taras da su ta kuma ji duk abinda suke fadi din,babu wanda ta cewa uffan sai tayi ma kamar batasan me yake faruwa ba,har suka gama sha'aninsu kowacce ta wuce gidanta suka bar safiyyan a gidan
"Ke yaushe zaki wuce...kowa ya tafi ya barki?"
"Mommy dukansu fa sun riga ni zuwa,kuma ma sai nayi sallar isha'i abban al'amin zaizo mu wuce tare"
"Ai shikenan..." Ta fada tana ci gaba da aikin gabanta.
A nan tayi sallar isha'i taci abinci,bata jima da kammalawa ba daddy ya shigo gidan,mintina goma ta bayar ta kwantar da al'amin sannan ta wuce zuwa falon daddyn.
Yana zaune saman kujera sanye da jallabiya,da alama daga wanka ya fito yayi shirin cin abinci,da murmushi a fuskarshi suke gaisawa,saboda duk cikin yaransa bayan asma'u itace ta biyu a wadanda yake so,itama asma'un don itace auta shi yasa ta rigashi zuwa,tana da halaye irin nashi,sauqin kai da fahimta gami da rashin daukar komai da zafi
"Amma ace tun safe kima gidan nan me mike baki koma gidanki ba safiya?" Murmushi tayi tana dubansa sannan tace
"Magana nakeso nayi da kai ne daddy" ta qarashe maganar yana dan satar kallon mommy,bisa dukkan alamu batason yin maganar tana wajen kenan,ya fahimceta,hakan ya sanya ya dubi mummy dake kici kicin zuba masa abincin darenshi wanda aysha ce ta girka yace
"Jeki hadamin coffe sa'adatu"
"Toh" tace tana aje serving spoon din hannunta ba tare data fahimci komai ba ta miqe ta fice.
Sai data gama fita din daddy ya kalli safiyya
"Ina jinki safiya ya akayi?"
"Daddy.....kasan wanda aysha ta kawo zata aura kuwa baida wani qarfi?...daddy kaman ma dai bazai iya riqeta nake gani"
"Indai zai iya bata ci da sha da suttura da muhallin zama ya kiyaye haqqoqinta da mutuncinta da lafiyarta safiya shi ake bida a aure,amma duk da haka akwai wani abu da larabawa ke cewa khafa'a wato dacewa da juna ta wajen aure,ko musulunci ya yadda da khafaa'ah....nasan halayen yaro kuma na binciki lamarinsa naga yana da ikon da zai iya riqe mace....yana da aiki duk da qarqashin wani yake,na gamsu da bincike na shi yasa na bashi ita" lallai daddy qila akwai abinda bai fahimta ba ko ya shige masa duhu,hakan ya sanya ta sake hada nutsuwarta tace
"Daddy....yaufa aka je ganin gidan da aysha zata zauna daddy...gidan qasa fa?" Shuru yayi yana nazarin maganarta,sai yaji shima bai gamsu data zauna a gidan ba,don idan yayi hakan tamkar baiyi adalci ba
"Gidan qasa safiya?..." Ya sake tambayarta don tabbatarwa
"Eh daddy" shuru ya sake shi da ita ba wanda ya sake cewa wani abu,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace
"Da kanta ta kawo yaron tana sonshi bata yadda za'ayi na hanata wanda take so,idan nayi mata haka kaman banyi mata adalci bane,amma shikenan babu komai...ki tashi kije Allah yayi miki albarka....zanga yaron zanyi wani abu akai in sha Allahu"
"Na gode daddy....Allah ya qara girma" ta fada tana miqewa,dai dai sanda mommy ta dawo dauke da coffen,hakan ya sanya daddy ya sake basar da zancan
"Ina abokina ne...ko kin soma barinshi gida shima?" Dariya tayi mummy ta amsa masa
"Yau abokinka ba lafiya,haqori ya sakoshi gaba...yana daki yana bacci"
"Ashsha...Allah ya sawwaqe,a gaida babanshi"
"Zaiji in sha Allahu....mummy ni zan wuce,sai da safe"
"Ki gaida gida da sauran yaran" da haka ta fito daga falon daddyn tana jin dadi har cikin ranta,tana jin kamar ta sauke wani nauyi,sam tana jin bai dace subar aysha ta rayu cikin gidan qasa ba ba adalci bane sam,batasan me yasa duk yadda yarinyar ke da hankali da nutsuwa ba basa gani
"Allah ya kyauta" ta fada tana amsa wayar abban al'amin daya kirata ta fito su tafi.
Yayi mamakin ganin kiran daddy da kanshi kan cewa yana son ganinshi,a ladabce ya amsa mishi,saidai yace ya bashi uzuri zuwa gobe,ya fadi hakanne saboda a ranar yaje abuja za' dauki hoton yatsunshi zai sauya passport dinsa.
******************
"Kaga malam basai kayi wahalar saka muqulli ka bude wannan rubabbiyar qofar ba,da qafa ma budeta zamuyi" ta qarasa fada tana daga qafarta ta daki qofar,qasa da qura suka biyo qofar suka yo kanta,hakan ya sanya tayi saurin ja da baya,ita kanta mamaki take cikin zuciyarta,sam batayi tsammanin talaucin yaron oga yakai har haka bama,wani bacin rai ya sake lullubeta da haushinsa,yasan haka yake har ya zubda mata ajinta ta jera da shi?,ta hada muhallin zama da shi,lallai iya zaman da yasa tayi da shi ba qaramar cutarta ma yayi ba,batasan mutane nawa ne da suka santa suka kuma sanshi suka gansu tare ba,ta tabbata wasu sun mata dariya.
Da qyar ya iya samu qofar ta bude ya tura kai ciki suka biyo bayanshi,tsukakke kuma dogon soro suka fara taraswa mai dauke da rufin azara irin ta da,idan kaci gaba da jumurin cusa kai zuwa cikin gidan kuwa,tsakar gida ne mai fadi da yalwa wanda aka yiwa daben qasa,duqurqushin bandaki jere kusa da kitchen,sai dakuna manya falle biyu
"Ummm....indo ba'a manta gida ba" cewar anty halima,daga kai kawai inna laraba tayi ta kalleta ta dauke kanta....wato shi dan qauye ba mutum ba?...tana da yaqinin harga Allah daddy baisan duka wainar da ake toyawa ba,duk da cewa bata gidan amma tana katarin riskar wasu abubuwan,ta yaya aysha yarinyar da tayi jami'a take zaune cikin birni shekara da shekaru zatayi aure cikin wannan gidan ta kuma zauna a ciki?,ta ina zata iya taimakawa rayuwarta ta fidda ta?
"Hhhhhh,ai tazo inda ya dace da ita" cewar asma'u tana yarfa hannu tare da takawa cikin gidan tana qare masa kallo.
Ba abinda dan rakiyar yace saboda ba'a umarceshi da cewa komai ba,kuma ya tabbatar duk abinda ke wakana boss din sa yana ji kuma yana gani,bai furta komai din ba har suka gama isgilancinsu suka gama suka tako zasu fita ya rufa musu baya,yana maida muqullin zai rufe asma'u ta dubeshi
"Kana wahalar da kanka ne kawai....banda abinka wai meye abun qwaqumawa wannan kangon kwado kayita wani rufeshi,da ka barshi ma a bude don baida maraba da kango" kallo daya yayi mata ya maida kansa yana ci gaba da ruge gidan,ranshi fal da mamakin me ya hada boss da wannan gidan me zaiyi da shi?,sannan kuma meye gaminsa da wadan nan matan?,ko da ya gama rufe gidan tuni sun hau kwalta sunyi gaba abinsu.
Cikin motar ma zancan gidan sukeyi,kowa na tofa albarkacin bakinsa,anty lubabatu ce tace
"Anya ko asma'u wannan plan din baiyi worst ba....talaucin mutumin nan fa kamar yayi yawa" dan tsaki ta ja saboda sakuwarta ce
"Kinjiki kema da wani irin zance....to daga ina ita din ta fito?....ina cewa irin wannan gidan anan taci ta sha,banda ma tsaurin ido irin na talaka daga an riqeka a waje sai kace lallai sai kayi rayuwa irin tasu?,kuma wa ya hanata musanta zancan tun yana farkonshi...wai ita saliha a dole baiwar Allah.....munafuka inaga ma kyanshi ta gani ta kasa cewa bata sonshi....so ni banga wani worst ba da yayi,ungulu ce kawai zata koma gidanta na tsamiya" tabe baki anty halima tayi,sai a sannan tayi magana
"Lubabatu a yadda yarinyar nan take gani tana da kyau idan ta auri wani kan mage ne zai waye,uban kowa ma neman taka shi zatayi,irinsun nan ki gansu haka haka ba qananun 'yan iska bane idan suka samu waje...Allah ne kadai yasan manufar jaki da bai bashi qaho ba....daddy nema haka kawai ba dangin dangiro kaje ka jajubo yarinyar mutane....ta gama abinda ya kawotan ma maimakon ka maidata a'ah ka daukama ranka saika aurar da ita....bayan ko uwarta bata ta tata saikai" ta qarashe maganar da tsaki
"Shi yasa nakesonki anty halima....kinfi kowa fahimta"
"Mu ai da yake jakai ne ko?" Lubabatu ta fada tana hararta,dariya tayi tana cewa
"Bance ba".
Nannuyar ajiyar zuciya ya saki ya soma latsa system din bayan ya gama gani da jin duk abinda ya gudana tun daga qofar gidan shigarsu ciki zuwa barinsu unguwar,tunani ne cikin qwaqwalwarsa kala daban daban,mamakin baqar zuciya da mugunta irin ta wasu mutanen,buri da fatan jefaka a rana koda baka takawa kowa komai ba,aysha dai aysha ba'a son ci gabanta a rayuwa kwata kwata?,shikam wanne irin gata zaiyi mata daya dace da ita wanda zai bada mamaki ya girgiza zukatan maqiya
[1/14, 1:37 PM] Om Muhammadiyya: Mamakin abinda aysha tayi wanda ya tsarewa asma'u a rai yake,me tayi mata mai zafi da taketa yunqurin daqile duk wani ci gabanta,wacce irin macace asma'un?,bama ita kadai ba,hatta da 'yan uwanta ya fuskanci haka suke,ta ina suka gado wannan halayya?,wato da da gaske shi din haka yake zasu fi kowa farincikin dawwamarta cikin wahala kenan?.
Kusan wunin ranar baki daya abinda ke masa kai kawo kenan a zuciya,har sanda yake zaune gaban anni yake cin abinci abunda ke tsinkulinsa kenan
"Muhammadu lafiya dai?gajiya ko kuma aikin?" Dan murmushi yayi sannan a nutse ya bata labarin dukkan abinda ya faru,kai take jinjinawa cike da mamaki da.nazari
"Muhammadu yarinyar nan tana buqatar wani ginshiqi da zai tallafeta....inama ace kana mata soyayya mai qarfi wadda zata zame mata jigo?....saidai duk da haka ina jin qaunar zama da ita...sai nake jin kamar a maida daurin auren gobe ka dauketa daga cikinsu,me yasa mutane zuciyoyinmu suke ciki da kishi qyashi da hassada?...Allah ka shiryamu ka gyara mana zukatanmu"ta furta cikin sanyin jiki
"amin ya Allah....amin"
_kuyi haquri da wannan don Allah_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*DB*
23
Tunda suka dawo babu zancan da suke sai na gidan ayshan mommy na ji bata dai tanka komai nata ciki ba,a sannan anty safiyya ta dawo daga kai al'amin asibiti,ganin ta gama da wuri sai ta zarto gida,nan ta taras da su ta kuma ji duk abinda suke fadi din,babu wanda ta cewa uffan sai tayi ma kamar batasan me yake faruwa ba,har suka gama sha'aninsu kowacce ta wuce gidanta suka bar safiyyan a gidan
"Ke yaushe zaki wuce...kowa ya tafi ya barki?"
"Mommy dukansu fa sun riga ni zuwa,kuma ma sai nayi sallar isha'i abban al'amin zaizo mu wuce tare"
"Ai shikenan..." Ta fada tana ci gaba da aikin gabanta.
A nan tayi sallar isha'i taci abinci,bata jima da kammalawa ba daddy ya shigo gidan,mintina goma ta bayar ta kwantar da al'amin sannan ta wuce zuwa falon daddyn.
Yana zaune saman kujera sanye da jallabiya,da alama daga wanka ya fito yayi shirin cin abinci,da murmushi a fuskarshi suke gaisawa,saboda duk cikin yaransa bayan asma'u itace ta biyu a wadanda yake so,itama asma'un don itace auta shi yasa ta rigashi zuwa,tana da halaye irin nashi,sauqin kai da fahimta gami da rashin daukar komai da zafi
"Amma ace tun safe kima gidan nan me mike baki koma gidanki ba safiya?" Murmushi tayi tana dubansa sannan tace
"Magana nakeso nayi da kai ne daddy" ta qarashe maganar yana dan satar kallon mommy,bisa dukkan alamu batason yin maganar tana wajen kenan,ya fahimceta,hakan ya sanya ya dubi mummy dake kici kicin zuba masa abincin darenshi wanda aysha ce ta girka yace
"Jeki hadamin coffe sa'adatu"
"Toh" tace tana aje serving spoon din hannunta ba tare data fahimci komai ba ta miqe ta fice.
Sai data gama fita din daddy ya kalli safiyya
"Ina jinki safiya ya akayi?"
"Daddy.....kasan wanda aysha ta kawo zata aura kuwa baida wani qarfi?...daddy kaman ma dai bazai iya riqeta nake gani"
"Indai zai iya bata ci da sha da suttura da muhallin zama ya kiyaye haqqoqinta da mutuncinta da lafiyarta safiya shi ake bida a aure,amma duk da haka akwai wani abu da larabawa ke cewa khafa'a wato dacewa da juna ta wajen aure,ko musulunci ya yadda da khafaa'ah....nasan halayen yaro kuma na binciki lamarinsa naga yana da ikon da zai iya riqe mace....yana da aiki duk da qarqashin wani yake,na gamsu da bincike na shi yasa na bashi ita" lallai daddy qila akwai abinda bai fahimta ba ko ya shige masa duhu,hakan ya sanya ta sake hada nutsuwarta tace
"Daddy....yaufa aka je ganin gidan da aysha zata zauna daddy...gidan qasa fa?" Shuru yayi yana nazarin maganarta,sai yaji shima bai gamsu data zauna a gidan ba,don idan yayi hakan tamkar baiyi adalci ba
"Gidan qasa safiya?..." Ya sake tambayarta don tabbatarwa
"Eh daddy" shuru ya sake shi da ita ba wanda ya sake cewa wani abu,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace
"Da kanta ta kawo yaron tana sonshi bata yadda za'ayi na hanata wanda take so,idan nayi mata haka kaman banyi mata adalci bane,amma shikenan babu komai...ki tashi kije Allah yayi miki albarka....zanga yaron zanyi wani abu akai in sha Allahu"
"Na gode daddy....Allah ya qara girma" ta fada tana miqewa,dai dai sanda mommy ta dawo dauke da coffen,hakan ya sanya daddy ya sake basar da zancan
"Ina abokina ne...ko kin soma barinshi gida shima?" Dariya tayi mummy ta amsa masa
"Yau abokinka ba lafiya,haqori ya sakoshi gaba...yana daki yana bacci"
"Ashsha...Allah ya sawwaqe,a gaida babanshi"
"Zaiji in sha Allahu....mummy ni zan wuce,sai da safe"
"Ki gaida gida da sauran yaran" da haka ta fito daga falon daddyn tana jin dadi har cikin ranta,tana jin kamar ta sauke wani nauyi,sam tana jin bai dace subar aysha ta rayu cikin gidan qasa ba ba adalci bane sam,batasan me yasa duk yadda yarinyar ke da hankali da nutsuwa ba basa gani
"Allah ya kyauta" ta fada tana amsa wayar abban al'amin daya kirata ta fito su tafi.
Yayi mamakin ganin kiran daddy da kanshi kan cewa yana son ganinshi,a ladabce ya amsa mishi,saidai yace ya bashi uzuri zuwa gobe,ya fadi hakanne saboda a ranar yaje abuja za' dauki hoton yatsunshi zai sauya passport dinsa.
******************