Sashe 88
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi ya fara shiga sashen,ya fada saman kujera ya ware hannayensa kan makarin kujerar yana dubanta sanda take shigowa,gab da zata wuceshi ya sanya mata qafa take ta harde tayo kanshi gaba daya,hannunshi yasa ya tallafeta cikin jikinsa
"Me zaki wuce ciki kiyi?,kefa kika ce tausa zaki yimin ko?" Cikin mutsu mutsu ta girgixa kanta tana son qwatar kanta saboda riqon tsauri da yayi mata
"Ohk,yanxu kuma don kinga babu idanunsu zaki canza magana kenan?"
"Kai ka sani na dinga musu haka"boyayyen murmushi ya saki
"Over act kikayi,tunda kuma kika sakamin rai saikin yi,dama am too tired" dage mata yayi kan sai tayi masa idan ba haka ba shi zaiyi mata,da qyar ta kubuta bayan data fake masa da bata karanta komai ba,bedroom ta gudu,ta jima zaune a can sai data dai daita mode dinta sannan ta fito,kanta na a qasa tace
"System dina pls ta rannan..."
"Wadda na kamaki kina kallon fina finan soyayya?" Ya tambayeta ba tare daya dubeta ba,saita kasa amsa mishi
"Nayi seezing,bana so ki sake amfani da ita" mamaki ne ya kamata,me tayi da zai mata seeizing na system?,itakam bata sani ba,saidai koma meye yafi gaban haka saboda haka batace komai ba kawai ta juya ta samu wani guri can daban ta xauna tana duba abinda ya kamata ta karanta.
Sha biyu saura na dare ta tura qofar bedroom din,ga mamakinta saita sameshi zaune dirshan saman gadon da system a gabanshi,tayi tsammani yayi bacci ne,taqi shigowa da wuri don kada abinda ya faru jiya wanda batasan ya akayi ya faru ba ya sake maimaituwa,ta farka ne kawai ta ganta cikin jikinshi,wanda kuma da alama itace ta baro side dinta ta dawo nashi.
A hankali take takowa har zuwa bakin gadon,ba abinda zata yi sai kwanciya kawai,don haka ta aje litafanta kan bedside din dake daura da ita,ta zauna a side dinta ta hada tafukan hannunta ta soma addu'ar kwanciya bacci,bayan ta gama ta hura ta shafe jikinta sannan ta maida duka qafafunta saman gadon,gyaran murya taji yayi wanda ya danja hankalinta,saidai bata juyo ta dubeshi ba
"Bacci zakiyi?" Ya tambayeta yana ci gaba da aikinshi,kanta ta gyada sannan tace
"Eh"
"Gobe zaki koma,hira ya kamata muyi" ya furta a dake kaman bashi yayi maganar ba,dan boyayyen murmushi ta saki
"Cikin wannan satin nima zan koma so ba lallai mu sake haduwa kafin sannan din" ya kuma yin maganar yana kashe system din,rasa amsar sa zata bashi ya sanyata yin shuru,bai sake cewa komai ba shima sai daya kammala komai ya dauke daga wajen sannan ya jingina bayanshi sosai da fuskar gadon bayan ya kara pillow
"Dame dame kike da buqatar tafiya dashi?"
"Babu komai,ina da komai" ta fada cikin sanyin muryarta data bada wani amo da salo ma daban saboda shurun dare da yanayin duhu duhun dakin,wanda hasken wayarshi daya haske fuskarshi mai saye da gilashin qarawa ido gani ya haska fuskarshi sosai,dan yatsanshi ya saka ya gyara glass din sosai sannan yace
"Come closer" daga kanta tayi ta dubeshi,yanzun ma kamar bashi ne yayi maganar ba hankalinsa nakan wayarshi,tsahon sakan goma kafin ta matsa kadan ta rage tazarar dake tsakaninsu ba mai yawa ba can,pillow din dake gefanshi ya dauko ya maida side din da take sannan ya nuna mata inda yake nufi da yatsa ba tare da yace komai ba,a hankali ta zauna inda yace din,tana gab dashi don tana iya jiyo fitar numfashinsa,wanzuwar pillow din a wajen kawai shiya hana cinyoyinsu gogar juba,wayar hannunshi yayi mata nuni da ita saita maida kallonta kai,tana kallonshi ya tafa (www.rahamalls.com) ya shiga,ba dadewa link din ya bude,jerin kayan da store din na rahamalls suke saidawa ya bude,kaya ne babu wanda babu a kai,yaci gaba da dubawa har yazo bangaren computers
"Dubamin...wacce ce tafi kyau?" Ya fada yana scrolling down,da ido ta dinga bin hotunan system din tana kallo,dukka bata banxa ba wadda batayi kyau ba,dai dai kan wata ash tace
"Irinta maman hunaifa...."sai kuma tadan kame bakinta batasan cewa a fili ta fada ba
"ohkey"ya fada yana shiga page din gaba wanda dinkakkun kayan maza suka bayyana,yayi order din wanda zaiyi ya kashe data dinsa,har a lokacin tana zaune a wajen
"bayan na tafi?,me zaki dinga tunawa dani?" So take ta daga kanta ta kalleshi tada da wanne yanayi yayi maganar,amma nauyi da kwarjinin idanunsa dake bisa kanta sun hanata dagowa,a sanyaye tace
"Babu"
"Ni kuma akwai" ya fada kana yayi shuru yana ci gaba da dubanta,batasan sanda ta furta lafazin
"Mene shi?"
"Yanzu nake so ki barmin abu daya da idan na tuna zaici gaba da debemin kewa duk tsahon lokaci" hannunshi ya miqa mata sannan ya kafeta da idanunshi sai ta dan tsaya tana kallon hannun nashi,ya qagu yaji dumin jikinta mai dadi,tunda ya taba dandanashi sau daya har yau feelings din yaqi barin jiki da qwaqwalwarsa.
A hankali ta dora tafin hannun nata itama saman nashi kamar yadda ya buqata,sosai ya rintse hannun kafin ya jawota ta fada jikinsa yasa hannayensa ya rufeta ruf yans jin dumi gami da shaqar daddad'an qamshin turarenta dake tashi a jikinta,dukkaninsu kowanne yana iya jiyo bugun zuciyar kowa,ba wanda yake wani qwaqwwaran motsi a cikinsu kowa yayi luf jikin dan uwanshi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A kunyace take hada dan abinda tasan tana buqata wanda dashi zata tafi wudil,ta rasa me ya fisgeta jiya har ta amsa tayin khalipha,duk inda yabi saita kaicewa ganinsa,har ya kammala uzurinsa cikin dakin ya rigata fita,batasan meye manufarshi ba akanta shima me yake nufi?,abu guda ta sani har sukayi aure suna kallon juna ne a matsayin wa qanwa.
Riga da skert ne a tamfa a jikinta,qafarta plat takalmi ne mai igiya wanda mahadi ne da jakar hannunta mai azabar kyau da tsari,hijani ta sanya mai hannu iya gwiwa,wanda yake hade da niqab,saita saka glass din da kanyi amfani dashi lokaci zuwa lokaci domin ado,harabar gidan take takowa bayan sunyi sallama da anni,yau duka cikin mutanen nata babu wacca ta gani,kodon da wuri ta fito oho.
Motocin khalipha ta gani jere a harabar gidan,tayi zaton wani guri zashi shima,saita dan tsaya tana duba ta inda zata hangi malam shehu,don wani lokaci shi ko haidar dama wani ke kaita.
Dai dai lokacin khaliphan ya fito da dan sassarfa daga sashen ma'aikatan gidan,da alama wata 'yar ganawa yayi dasu,yana tafe yana duba agogonshi,caraf ya kamata tana satar kallonshi,ta kalleshi ita kanta batasan yakai sau nawa ba,shigarsa ta yau ba qaramin kyau tayi masa ba,haka uwa uba take jin wani ba dadi gami da wassafa adadin kwanakin da zata dauka kafin ta sake ganinshi.
Dauke kanta tayi ita ala dole saita tayi pretending kan cewa bashi take kallo ba,wani sashen na gidan daban ta maida kanta tana kalla,saidai haka kawai zuciyarta taqi biyota,ji tayi an riqe jakar hannunta,abinda ya sanyata waiwayo kenan ba tare data shirya ba,yana tsaye gabanta ita yake kalla,saidai fuskarsa a dinke take,ya mata kwarjini sosai,hakan ya sanya gabanta faduwa,da hannu ya mata nuni data wuce,jakar daya riqe ta kalla alamun ya sakar mata,sai ya dage kafadu yana gaya mata ina ruwanta,sakin jakar kawai tayi tayi gaba,da sauri nasir yaronshi dake riqe masa muhimman abubuwanshi duk sanda zasu fita ya matso da sauri zai karba saiya dakatar dashi.
Gab da zasu isa wajen motocin haidar ya faka tashi motar ya fito,tuni ya riskesu,cikin girmamawa ya gaida khalipha
"Barka da safiya yaya"
"Barkanka....ina fata ka kammala yadda ya dace?"
"In sha Allahu" ya amsa yana murmushi yana duban aysha sai ya kallo khalipha
"Na fito da motane na kaita?"
"Na hutashsheka yau" ya fada yana bude mata murfin motar da kanshi
"Yaya ni nake kaita dama ai,yauma bansan da wuri zata koma bane shi yasa na fita" tsayawa yayi da abinda yake ya zubawa haidar ido,shakka ta dan shigeshi,don khalipha ba daga nan ba wajen kwarjini,ko dan uwanshi namiji ya zubawa ido sai yaji ya a jikinsa
"Sorry yaya...." Ya fada yana hade hannyensa waje guda
"Anty Allah ya kiyaye hanya,asha L....." Sai ya juya da sauri yana dariya zuwa cikin gida,cikin zuciyarshi yana tuna hirat da sukayi jiya shida anni bayan barinsu khalipha wajen
"Haidar....kayi a hankali"
"Me ya faru anni?" Ya tambayeta yana tsayawa da bare bayan wayarshi da yake
"Yayanka ya fara kishinka ne" idanu ya zaro
"Kishi anni akanme?" Murmushi ta saki
"Akan matarsa" idanunsa a waje yaci gaba da duban annin yanason yaji qarin bayani
"Ya kamata ka janye jikinka zuwa yanzu,saboda ya fara soyayya,kasan kuwa illar da soyayya kewa wanda ya fada cikinta ba tare daya sani ba ba kdan bane,zaiyita abubuwa gq zaton na wanda yake kallonsa ko yana cikin hayyacinsa,saidai ina lamarin ba haka bane,shi sha'anin soyayya ya wuce duk tunani" ta qarashe maganar tana tubawa kanta da nata masoyin alhj sa'id,da irin gwagwarmayar da suka fuskanta kafin su cimma gaci
"Lalle ya khalipha ya hau network,ni anni kawai ina respecting din anty saboda na jima banga mai shekaru irin nata dake da hankali da nutsuwa kamar haka ba,sannan tausayinta nake ji tun daga randa na fuskanci tayi shigen tamu rayuwar,uwa uba ina taya yaya kishi ne saboda nasan halin sa'o'inmun nan,suna qyalla ido suka ganta ita kadai ba wani gefanta tsaf zasu iya yiwa ya khalioha shigar burtu....hajjaju anni da alama an tuna da,ya kamata na sanarwa mus'ab harma da ya khalipha muzo mu kwashi darasin soyayya...." Ya qarashe yana dariyar zolaya,daquwa ta watsa masa
"kaci gidanku,tashi ka bani waje ja'iri" yana dariya ya bar wajen yayin data bishi da kallo,na shakka soyayya bata tsufa,don har kwanan gobe bata fasa son sa'id dinta ba,da wannan tunanin haidar ya qarasa cikin gida,lallai zancan annin ya tabbata,tunda suka taso da yayan nasu basu taba ganinshi yana soyayya ba,ah lallai abun zaiyi matuqar armashi,zaiso yaga ya za'a buga wannan game din mai qayatarwa.
48
Ajiyar zuciya ya sauke mai sanyi sannan ya dauke idonsa daga binta da yayi da kallo sanda ta gama shigewa cikin hostel din nasu,a hankalibya sauke hannauensa ya shige motar da tuni aka bude masa murfinta,sauran suma suka shiga tasu suka tashi motocin suka bar wajen.
"Me zaki wuce ciki kiyi?,kefa kika ce tausa zaki yimin ko?" Cikin mutsu mutsu ta girgixa kanta tana son qwatar kanta saboda riqon tsauri da yayi mata
"Ohk,yanxu kuma don kinga babu idanunsu zaki canza magana kenan?"
"Kai ka sani na dinga musu haka"boyayyen murmushi ya saki
"Over act kikayi,tunda kuma kika sakamin rai saikin yi,dama am too tired" dage mata yayi kan sai tayi masa idan ba haka ba shi zaiyi mata,da qyar ta kubuta bayan data fake masa da bata karanta komai ba,bedroom ta gudu,ta jima zaune a can sai data dai daita mode dinta sannan ta fito,kanta na a qasa tace
"System dina pls ta rannan..."
"Wadda na kamaki kina kallon fina finan soyayya?" Ya tambayeta ba tare daya dubeta ba,saita kasa amsa mishi
"Nayi seezing,bana so ki sake amfani da ita" mamaki ne ya kamata,me tayi da zai mata seeizing na system?,itakam bata sani ba,saidai koma meye yafi gaban haka saboda haka batace komai ba kawai ta juya ta samu wani guri can daban ta xauna tana duba abinda ya kamata ta karanta.
Sha biyu saura na dare ta tura qofar bedroom din,ga mamakinta saita sameshi zaune dirshan saman gadon da system a gabanshi,tayi tsammani yayi bacci ne,taqi shigowa da wuri don kada abinda ya faru jiya wanda batasan ya akayi ya faru ba ya sake maimaituwa,ta farka ne kawai ta ganta cikin jikinshi,wanda kuma da alama itace ta baro side dinta ta dawo nashi.
A hankali take takowa har zuwa bakin gadon,ba abinda zata yi sai kwanciya kawai,don haka ta aje litafanta kan bedside din dake daura da ita,ta zauna a side dinta ta hada tafukan hannunta ta soma addu'ar kwanciya bacci,bayan ta gama ta hura ta shafe jikinta sannan ta maida duka qafafunta saman gadon,gyaran murya taji yayi wanda ya danja hankalinta,saidai bata juyo ta dubeshi ba
"Bacci zakiyi?" Ya tambayeta yana ci gaba da aikinshi,kanta ta gyada sannan tace
"Eh"
"Gobe zaki koma,hira ya kamata muyi" ya furta a dake kaman bashi yayi maganar ba,dan boyayyen murmushi ta saki
"Cikin wannan satin nima zan koma so ba lallai mu sake haduwa kafin sannan din" ya kuma yin maganar yana kashe system din,rasa amsar sa zata bashi ya sanyata yin shuru,bai sake cewa komai ba shima sai daya kammala komai ya dauke daga wajen sannan ya jingina bayanshi sosai da fuskar gadon bayan ya kara pillow
"Dame dame kike da buqatar tafiya dashi?"
"Babu komai,ina da komai" ta fada cikin sanyin muryarta data bada wani amo da salo ma daban saboda shurun dare da yanayin duhu duhun dakin,wanda hasken wayarshi daya haske fuskarshi mai saye da gilashin qarawa ido gani ya haska fuskarshi sosai,dan yatsanshi ya saka ya gyara glass din sosai sannan yace
"Come closer" daga kanta tayi ta dubeshi,yanzun ma kamar bashi ne yayi maganar ba hankalinsa nakan wayarshi,tsahon sakan goma kafin ta matsa kadan ta rage tazarar dake tsakaninsu ba mai yawa ba can,pillow din dake gefanshi ya dauko ya maida side din da take sannan ya nuna mata inda yake nufi da yatsa ba tare da yace komai ba,a hankali ta zauna inda yace din,tana gab dashi don tana iya jiyo fitar numfashinsa,wanzuwar pillow din a wajen kawai shiya hana cinyoyinsu gogar juba,wayar hannunshi yayi mata nuni da ita saita maida kallonta kai,tana kallonshi ya tafa (www.rahamalls.com) ya shiga,ba dadewa link din ya bude,jerin kayan da store din na rahamalls suke saidawa ya bude,kaya ne babu wanda babu a kai,yaci gaba da dubawa har yazo bangaren computers
"Dubamin...wacce ce tafi kyau?" Ya fada yana scrolling down,da ido ta dinga bin hotunan system din tana kallo,dukka bata banxa ba wadda batayi kyau ba,dai dai kan wata ash tace
"Irinta maman hunaifa...."sai kuma tadan kame bakinta batasan cewa a fili ta fada ba
"ohkey"ya fada yana shiga page din gaba wanda dinkakkun kayan maza suka bayyana,yayi order din wanda zaiyi ya kashe data dinsa,har a lokacin tana zaune a wajen
"bayan na tafi?,me zaki dinga tunawa dani?" So take ta daga kanta ta kalleshi tada da wanne yanayi yayi maganar,amma nauyi da kwarjinin idanunsa dake bisa kanta sun hanata dagowa,a sanyaye tace
"Babu"
"Ni kuma akwai" ya fada kana yayi shuru yana ci gaba da dubanta,batasan sanda ta furta lafazin
"Mene shi?"
"Yanzu nake so ki barmin abu daya da idan na tuna zaici gaba da debemin kewa duk tsahon lokaci" hannunshi ya miqa mata sannan ya kafeta da idanunshi sai ta dan tsaya tana kallon hannun nashi,ya qagu yaji dumin jikinta mai dadi,tunda ya taba dandanashi sau daya har yau feelings din yaqi barin jiki da qwaqwalwarsa.
A hankali ta dora tafin hannun nata itama saman nashi kamar yadda ya buqata,sosai ya rintse hannun kafin ya jawota ta fada jikinsa yasa hannayensa ya rufeta ruf yans jin dumi gami da shaqar daddad'an qamshin turarenta dake tashi a jikinta,dukkaninsu kowanne yana iya jiyo bugun zuciyar kowa,ba wanda yake wani qwaqwwaran motsi a cikinsu kowa yayi luf jikin dan uwanshi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A kunyace take hada dan abinda tasan tana buqata wanda dashi zata tafi wudil,ta rasa me ya fisgeta jiya har ta amsa tayin khalipha,duk inda yabi saita kaicewa ganinsa,har ya kammala uzurinsa cikin dakin ya rigata fita,batasan meye manufarshi ba akanta shima me yake nufi?,abu guda ta sani har sukayi aure suna kallon juna ne a matsayin wa qanwa.
Riga da skert ne a tamfa a jikinta,qafarta plat takalmi ne mai igiya wanda mahadi ne da jakar hannunta mai azabar kyau da tsari,hijani ta sanya mai hannu iya gwiwa,wanda yake hade da niqab,saita saka glass din da kanyi amfani dashi lokaci zuwa lokaci domin ado,harabar gidan take takowa bayan sunyi sallama da anni,yau duka cikin mutanen nata babu wacca ta gani,kodon da wuri ta fito oho.
Motocin khalipha ta gani jere a harabar gidan,tayi zaton wani guri zashi shima,saita dan tsaya tana duba ta inda zata hangi malam shehu,don wani lokaci shi ko haidar dama wani ke kaita.
Dai dai lokacin khaliphan ya fito da dan sassarfa daga sashen ma'aikatan gidan,da alama wata 'yar ganawa yayi dasu,yana tafe yana duba agogonshi,caraf ya kamata tana satar kallonshi,ta kalleshi ita kanta batasan yakai sau nawa ba,shigarsa ta yau ba qaramin kyau tayi masa ba,haka uwa uba take jin wani ba dadi gami da wassafa adadin kwanakin da zata dauka kafin ta sake ganinshi.
Dauke kanta tayi ita ala dole saita tayi pretending kan cewa bashi take kallo ba,wani sashen na gidan daban ta maida kanta tana kalla,saidai haka kawai zuciyarta taqi biyota,ji tayi an riqe jakar hannunta,abinda ya sanyata waiwayo kenan ba tare data shirya ba,yana tsaye gabanta ita yake kalla,saidai fuskarsa a dinke take,ya mata kwarjini sosai,hakan ya sanya gabanta faduwa,da hannu ya mata nuni data wuce,jakar daya riqe ta kalla alamun ya sakar mata,sai ya dage kafadu yana gaya mata ina ruwanta,sakin jakar kawai tayi tayi gaba,da sauri nasir yaronshi dake riqe masa muhimman abubuwanshi duk sanda zasu fita ya matso da sauri zai karba saiya dakatar dashi.
Gab da zasu isa wajen motocin haidar ya faka tashi motar ya fito,tuni ya riskesu,cikin girmamawa ya gaida khalipha
"Barka da safiya yaya"
"Barkanka....ina fata ka kammala yadda ya dace?"
"In sha Allahu" ya amsa yana murmushi yana duban aysha sai ya kallo khalipha
"Na fito da motane na kaita?"
"Na hutashsheka yau" ya fada yana bude mata murfin motar da kanshi
"Yaya ni nake kaita dama ai,yauma bansan da wuri zata koma bane shi yasa na fita" tsayawa yayi da abinda yake ya zubawa haidar ido,shakka ta dan shigeshi,don khalipha ba daga nan ba wajen kwarjini,ko dan uwanshi namiji ya zubawa ido sai yaji ya a jikinsa
"Sorry yaya...." Ya fada yana hade hannyensa waje guda
"Anty Allah ya kiyaye hanya,asha L....." Sai ya juya da sauri yana dariya zuwa cikin gida,cikin zuciyarshi yana tuna hirat da sukayi jiya shida anni bayan barinsu khalipha wajen
"Haidar....kayi a hankali"
"Me ya faru anni?" Ya tambayeta yana tsayawa da bare bayan wayarshi da yake
"Yayanka ya fara kishinka ne" idanu ya zaro
"Kishi anni akanme?" Murmushi ta saki
"Akan matarsa" idanunsa a waje yaci gaba da duban annin yanason yaji qarin bayani
"Ya kamata ka janye jikinka zuwa yanzu,saboda ya fara soyayya,kasan kuwa illar da soyayya kewa wanda ya fada cikinta ba tare daya sani ba ba kdan bane,zaiyita abubuwa gq zaton na wanda yake kallonsa ko yana cikin hayyacinsa,saidai ina lamarin ba haka bane,shi sha'anin soyayya ya wuce duk tunani" ta qarashe maganar tana tubawa kanta da nata masoyin alhj sa'id,da irin gwagwarmayar da suka fuskanta kafin su cimma gaci
"Lalle ya khalipha ya hau network,ni anni kawai ina respecting din anty saboda na jima banga mai shekaru irin nata dake da hankali da nutsuwa kamar haka ba,sannan tausayinta nake ji tun daga randa na fuskanci tayi shigen tamu rayuwar,uwa uba ina taya yaya kishi ne saboda nasan halin sa'o'inmun nan,suna qyalla ido suka ganta ita kadai ba wani gefanta tsaf zasu iya yiwa ya khalioha shigar burtu....hajjaju anni da alama an tuna da,ya kamata na sanarwa mus'ab harma da ya khalipha muzo mu kwashi darasin soyayya...." Ya qarashe yana dariyar zolaya,daquwa ta watsa masa
"kaci gidanku,tashi ka bani waje ja'iri" yana dariya ya bar wajen yayin data bishi da kallo,na shakka soyayya bata tsufa,don har kwanan gobe bata fasa son sa'id dinta ba,da wannan tunanin haidar ya qarasa cikin gida,lallai zancan annin ya tabbata,tunda suka taso da yayan nasu basu taba ganinshi yana soyayya ba,ah lallai abun zaiyi matuqar armashi,zaiso yaga ya za'a buga wannan game din mai qayatarwa.
48
Ajiyar zuciya ya sauke mai sanyi sannan ya dauke idonsa daga binta da yayi da kallo sanda ta gama shigewa cikin hostel din nasu,a hankalibya sauke hannauensa ya shige motar da tuni aka bude masa murfinta,sauran suma suka shiga tasu suka tashi motocin suka bar wajen.