← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 114

Sashe 3

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru ya ratsa tsakaninsu bayan ya gama iya maganganun da yaga sun kamata,saidai rashin samun gamsashshiyar amsa yasa maganganun nashi basuyu tsaho ba
"Ammm...dama akwai abinda nakeson gaya maka" ta fada tana gyara yafen mayafinta
"Uhmmm...babu damuwa,yi maganarki"
"Cewa nayi don Allah daga yau ina son ka janye daga zuwa wajena da kake....saboda ina da buqatar space"qaramin murmushi ne ya subucewa fuskarsa,abinda yake zato yau zai tabbata kenan
"Amma wani laifi na aikata ne haka" kai ta kada tana dan tabe baki
"Ko daya,kawai na gaji da alaqarmu ne haka.....har yau jiya iyau,kai ba qaruwa ake da kai ba" ta qarashe furucin qarshe can qasan maqoshinta,saidai abinda bata sani ba shine,yana daga cikin jinsin mutanen da Allah ya musu kaifin ji matuqa,murmushi ya kuma saki mai dan sauti,ga mamakinta taji yace
"Shikenan....in sha Allahu daga yau din zan janye....amma" ya fadi yana sanya hannunsa cikin aljihun trouser dinsa,american dollers ya ciro daga aljihun nasa wanda baisan ko na nawa bane,takawa yayi a hankali har ya isa inda take jingune rungume da hannayenta ya soka mata su tsakanin hannayenta yana ci gaba da jifanta da murmushi
"Na gode da lokutanki na baya da kika aramin.....sai wara rana" ya fadi yana juyawa,binsa tayi da kallo galala,duk wata tasha ta tunaninta ta dauke tsaf,har ya isa bakin wata baqar mota wadda bataji sanda ta iso inda suke ba,gidan baya ya bude ya shige kana ya rufe,sai data ga motar ta bar layin nasu sannan hankalinta ya dawo jikinta,tabi dollers din dake liqe a jikinta da kallo,sabbi kar suna fidda wani irin qamshi dake cakude da sassanyan qamshin turarensa da har rana irin ta yau ta rasa gane wanne irin turare yake amfani da shi,cikin sauri kaman wadda aka yiwa allura ta juya cikin hanzarinta shige gidan su,bata tsaya ko ina ba sai parlourn gidansu,inda tabar qawarta barratu na jiranta
"Ya akayi,kin sallami dan anacen naki" maimakon ta amsa mata saita miqa mata dalolin dake hannunta
"Wadannan fa daga ina?" Barratu ta fada tana zakudawa gami da gyara zamanta tare da tattara dukkan hankalinta kan zulaiha,mayafinta ta yage sannan ta zauna hannun kujera tana baiwa barratu labarin abinda ya faru,ta rufe da cewa
"Tsoro na daya barratu,kada ya kasance irin mijin da nake muradi ne na koreshi da kaina,kinga irin motar daya shiga kuwa" ta fada fargabarta na fitowa fili qarara,murmushi barratu ta saki tana karkada kudaden
"Kinga malama....kwantar da hankalinki....tundan yau kin gano haka ai baki makara ba,waskewa zakiyi,ai kiransa zakiyi kawai ki nuna ke bakison kudinsa yazo ya amshi abinsa,ke gwadashi dama kike yi" bata tsaya ta gama jinma qarshen zancan ba ta zaro wayarta cikin hanzari ta soma laluba inda ta jefa lambar tasa,can cikin black list ta ganota,cikin hanzari ta cireta daga black list din sannan ta soma kiransa.

Dai dai lokacin yana lafe a bayan motar suna tafe, mahmoud nata tambayar sa ya akayi a gefe guda kuma yana sheqa masa dariya,qarar wayar ita ta sanyashi bude manyan idanunshi da suke a rufe,waya ce da ita daya keda number,wadda dama dominta ya siya wayar da layin,hannunshi ya kai ya daga wayar ya kara a kunnensa ba tare da yace komai ba
"Ka dawo ka amshi kudinka,ni basu nake so ba,gwadaka dama nake,kuma alamu sun nuna kaci wannan jarrabawar" irin maganganun data ringa jerowa kenan duk a niyyarta nason amintar da shi da gamsar da shi,murmushi kawai ya sake mata wanda ya ratsa kunne da qwaqwalwarta
"Am sorry to say,ida na wuce aji bana maimaita shi.....sai wata rana" ya qarashe fada yana cire wayar daga kunneshi,bai tsaya a nan ba sai daya cire layin ya karyashi gida biyu,ya sauke glass din motar qasa kadan ya watsar ta window sannan ya maidashi yadda yake ya koma jikin kujerar motar ya sake lafewa ba tare daya bi ta kan dariyar mahmoud ba,hannayensa ya saka ya rufe kunnuwansa saboda yadda mahmoud din ya hanashi sakat,daga bisani da yaga baida niyyar barinshi ya huta ya shammaceshi ya kai masa naushi,Allah ya taimakeshi ya kauce yana cewa
"A'ah,karka lahantani,haka kawai bani na kar zomon ba ai,danma ka samu wai ina rakoka,tunda an kasaka ba shikenan ba sai ka sake sabon lale....amma fa ka riqr a ranka,'yammatan zamani indai zaka ci gaba da zuwa musu a haka za'a dade ana kasaka" dariya ce ta subucewa khalipha ba tare saya shirya ba,suka dan dara tare da mahmoud din,shi kansa lamarin na bashi mamaki gamibda daure masa kai,karo na uku?,karo na uku duk tafiyar ta kasance iri guda?,sai yaushe?,sai yaushe zaiga sauyi,zaya so yaga wannan rana qwarai.
*_HUGUMA_*

0⃣3⃣

Tsaye yake cikin tafkekan dakin taron a gaban wani hamshaqin teburi wanda yake dauke da aqalla ma'aikata kimanin mutuk arba'in,hannunsa guda dafe yake da gaban teburin yayin da daya hannun yaketa wulwulgashi cike da gwanancewa duk da baisan yana yi ba,da alama bayanin da yakewa ma'aikatan da suka bashi dukkan nutsuwarsu ya dauki zafi,lokaci lokaci yana daga daya hannun nasa dake dafe da teburin yana duba agogon hannunsa,wannan kadai ya isa ya nuna maka mutum ne mai kiyaye lokaci da kuma alfanunsa.

"Is there any problem?...." Ya qarashe jimlar tasa ta qarshe yana duban fuskokin ma'aikatan,saidai kowanne ya gamsu girgiza kai suka dinga yi daya bayan daya,ganin haka ya sanya shi ya soma tattare kayanshi dake saman teburin tare da bada umarnin a rufe taron da addu'a kaman yadda yake a qa'idarsa.

Shine mutum na farko da ya soma fita,shahid ya rufa masa baya suna magana qasa qasa,a bakin hall din daya daga cikin mutanen dake tsaye a wajen ya karbi kayan hannunsa sannan yabi bayansa har cikin elevetor wadda bata saukesu ko ina ba sai hawan qarshe na kamfanin inda office dinsa yake.

Mahmoud ne kawai zaune cikin office din ya tasa computer a gaba da alamu wani aiki yake ragewa mai muhimmanci Hannu mahmoud ya baiwa shahid suka gaisa cike da alamun cikakkiyar sanayya a tsakaninsu bayan security din dake riqe da kayan khaliphan ya aje ya fice,yayin da khalipha ya wuce kai tsaye bakin freezer ya dauki ruwa ya sha bayan ya rage suit din jikinsa kana ya shige toilet,alwala ya daura sannan ya dawo cikin office din ya tadda shahid da mahmoud suna hira,wadda fiye da rabinta abinda ya shafi kasuwancinsu ne,daya daga cikin wayayoyinshi wadda ke dauke da lambobin dukkan mutanen daya baiwa muhimmanci a rayuwarsa lambarsu ke ciki,kai tsaye ya nufi bakin daya daga cikin windows din dake cikin dakin office din wanda kai tsaye zaka iya kiransu da qofa saboda kadan ne ya rage basu kai girman qofar ba,saidai glass ne zalla a jiki wanda hakan zai baka damar gano ainihin farfajiyar companyn daga sama har qasa.

Bugu biyu aka daga wayar,ya sauke ajiyar zuciya sallamar matar na ratsa kunnensa,cikin sanyin murya kaman yadda halittar muryarshi take ya amsa sallamar sannan yace"Anni...barka da warhaka"
"Barka kadai khalipha,kun fito daga taron ne?"
"Mun fito ammi,saidai aci gaba da yi mana addu'a Allah yasa mu dace"
"Ubangiji ya dafa,ya shiga lamarinku,ya zama jagora a gareku,ya albarkaci rayuwarku". Cike da jin dadi yaketa amsawa da ameen,idanunsa lumshe yana shafa qirjinsa yana jin zuciyaraa wasai
"Ya jikin anni?,kinsha maganinki na rana,naga lokaci yayi"murmushi ta saki cike da qaunar yaron nata
"Khalipha kenan baka gajiya?,kaman ba awannin da suka shude muka gama waya da kai ba,jiki alhamdulillah,magani kuma ina gama sha kiranka ya shigo"cikin murmushi ya amsa
"Ya za'ayi na gaji da jinki anni....Allah ya qara miki lafiya mai dorewa"
"Allahumma amin khalipha,Allah yayi albarka"
"Ameen anni...sai na dawo"
"Allah ya tsare" ta sake ambata cikin nuna kulawa da qauna,ya amsa sannan ya kashe wayar yana murmushi,abubuwa da yawa na dawowa cikin kwanyarsa game da annin tasa,zai iya cewa baiga uwa irin tashi ba,kuma baya zaton za'a samu,anninsa da taban ce ko cikin halittun ubangiji,da wannan zancan zucin ya qaraso inda su mahmoud suke.

🧶🧶🧶

Zaune yake gaban annin tashi cikin shigar qananun kaya na t shirt da trouser,qafafunshi tanqwashe gabanshi kuma plate ne wanda ke dauke da tuwon shinkafa miyar water leaf da ogu wadda ta wadata da ganda busashshen kifi da kuma tsokar nama,a nutse yake cin abinci gefe guda suna hira da anni,hirar dake nuna tsantsar shaquwa dake tsakaninsu,kallo daya zaka yi musu ka tabbatarwa kanka lallai akwai saboda da shaquwa mai qafi tsakaninsu
"Khalipha..." Ta ambata a hankali wanda hakan yasa ya dago kanshi yana dubanta sannan ya amsa
"Wai sau yaushe zan daina jiran ganin zuwam surukata?" Murmushi ne ya subuce masa,sai ya aje cokalin hannunsa ya fasa kai lomar da yayi niya,cikin kulawa da qauna yake dubanta sannan yace
"Kwanan nan anni,karki damu....addu'arki nake buqata kawai...ina son na kawo miki surukar da zata kulamin dake,surukar da zata daukeki a matsayin uwa....surukar da zakiji dadin zama da ita fiye dani yadda zanji" murmushi ya subuce mata,sai ta kada kai tana dubanshi
"Allah ya baka mace ya gari wadda zata zame maka majingina.....amma banda abin khalipha kana tunanin akwai irin wannan surukan yanzu?" Ta qarashe managanar tana dariya qasa qasa,don har ga Allah bata dauki burinta ta cillashi har haka ba,kullum dai addu'arta Allah ya bashi wadda zata soshi tsakani da Allah,nagartacciyar matar aure,dan marairaicewa yayi kadan sannan yace
"Anni,kin sha gayamin ba'a fidda rai da rahamar Allah"
Kai ta jinjina cike da gamsuwa tace"wannan haka yake,ubangiji ya maka zabi ja gari"
"Ameen" ya amsa yana daukar cokalinsa dinci gaba da cin abincinsa sannan yace
"Cikin sati na gaba haidar zai dawo gida hutu" murmushi tayi kaman ko yaushe
"Sun kammala jarabawar kenan"
"Eh sun samu hutu na wata biyu"
"Allah ya kai mana rai"
"Ameen" ya amsa yana daukar cup din daya cika da ruwa ya soma sha.

🧶🧶🧶

Da sauri sauri take tafiya hadi da duba agogon hannunta,qarfe tara da rabi na safe dai dai,mintuna talatin zata qara ta makara wanda hakan dai dai yake da rasa lacture dinta har na tsahon awa biyu.
Chapter 3 · 0% Book details