← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 114

Sashe 28

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana qoqarin sauka anni na hawa,ta wuce ita kuma ta shige ciki,yunqurin tashi yayi ya zauna sanda yaji sallamarta,idanunta a kansa saita kadar ta kalli kayan abincin da bai taba ba,bata ce masa komai ba ta isa gaban abincin da kanta ta soma kiciniyar zuba masa,da hanzarinsa ya taso ya karbeta yana murmushi,itama murmushin tayi sannan ta sakar masa yaci gaba da zubawa,ta koma da baya ta samu waje ta zauna tana cewa
"Ah to...naga alamun 'yan sarautar ne yau a kusa" murmushi kawai yayi bayan ya gama zuba dai dai yadda zai iya ci ya rufe komai ya koma gabanta ya zauna ya soma ci
"Uhmmm....ina jinka ya akayi?" Ta tambayeshi kai tsaye kaman daman ya gaya mata zasuyi wata magana ne,murmushi ya saki yana jin dadi har cikin ransa,mahaifiyarsa ta karanceshi fiye da kowa a duniya,aysha ce ta fado masa a hankali fara'ar fuskarsa ta dan ragu,ya motsa bakinsa yana duban annin yace.

*DB*

18

"Bansan ta ina zan fara ba anni...matar aure aka bani,bansan me zance ba" abinda ya iya fara fada mata kenan saboda shi kansa baisan ta ina zai fara ba,idanunta ta saka tana kallonshi saboda yadda taji maganar tashi banbarakwaii,tana tunanin tayaya haka ta faru,saidai koma meye ta sani cewa zaiyi mata bayani,hakanan bazai taba yin wani abu daba dai dai ba kozai haifar da dana sani,zamanta ta gyara tana qoqarin fahimtar dan nata kamar yadda al'adarta take,bata yankewa koma waye hukunci kai tsaye,murmushi ne bisa fuskarta
"Matar aure a ina?,kaji gorin haidar kenan?" Murmushi shima ya danyi yana ture kwanon abincin gefe duk da ba wani mai yawa yaci ba
"Zaki iya tuna alhajin nan da na taba tsintar wallet dinsa,wanda ya taba biya miki kudin aikin da aka yi miki shekara goma da suka wuce?" Kai take kadawa
"Qwarai kuwa....ya za'ayi na manta muhammadu?irin wadan nan mutanen dan halak bai manta halaccinsu a gareshi"
"A gidanshi take...shine mariqinta"
"Ikon Allah" ta ambata cikin mamaki,a hankali ya zauna ya warware mata komai,babu abinda ya boye mata,tun daga yadda ya dinga neman aure ta sigar DAURIN BOYE,har zuwa neman asma'u yadda mu'amalarsu ta kasance sa kuma yadda ta qulla lamarin shi da aysha,sannan yazo ya bata labarin rayuwar ayshan kamar yadda itama ta bashi.

Ta jima anni tana jinjina kai,falon ya jima shuru shi da ita babu wanda yace wani abu,labarin ratsata yake tun daga kanta zuwa tafin qafarta,lallai duniya,inda ranka kasha kallo,idan kana da rai babu abinda ba zaka gani ba,tsahon wasu mintuna ta dauka kafin ta dubeshi
"Koda baka karbi aurenta ba,ko babu niyyar haka a zuciyarka khalipha ina mai baka umarnin ka aureta khalipha....,Allah ne kadai yasan manufarsa daya kawo silar haduwarmu da ita ta wannan sigar,me yiwuwa Allah ya turomu ne muma cikin rayuwarta,aurenta shine hanaya daya tak da zata zama bamu damar sauya mata rayuwa" Ta fada tana jin lafuzan nata har cikin zuciyarta,wani irin tausayi da qauna ta ayshan na na ratsata duk da bata ganta ba,duk mutumin daya fuskanci rayuwa irin wannan abun a tausaya masa ne,a dubeshi a kuma juyawa a dubeshi,sun taba dandanawa da kalar tasu daban,ba zasu taba mantawa ba.

Kanshi yake jinjinawa,shi kansa yana jin cikin zuciyarsa tamkar haduwarsu daga Allah ce,tamkar Allah ya tsara komai ne don ya sama ma rayuwarta farincikin da bata taba dandanarsa ba tun tasowarta
"Allah ya bani ikon sauke dukkan haqqin mai haqqi dake kaina...." Ya ambata,saidai wani bari na zuciyarsa yana fasalta yadda aure zaiyuwu babu soyayya,bayaso ta amincewa zama da shi saboda ta samu matserar rayuwarta bawai don ta nutsu da hakan har zuciyarta ba.

Kafin kowa yace wani abu a cikinsu zeenart ta shigo falon fuskarta qunshe da fara'a
"Anni...alhaji yazo" tana nufin mahaifinta kenan
"Toooh....maraba" ta ambata tana miqewa daga zaman da take,shima khaliphan miqewa yayi ya sakata a gaba zeenart na bayanshi suka sauko zuwa qasan.

"Ku haka kuke qulewa kubar gida ba kowa.....ba don zeenatun na kusa ba kenan saidai ka gaji ka koma....yo ai wannan gwara da take zaune a gidan ma" ya fada yana saba babbar rigarsa,idonsa na kan khaliph wanda fuskarsa take ba yabo ba fallasa,idanunshi na kam anni bai dauke ba sai da yaga ta zauna sannan ya dauke nashi idanun ya samu hannun kujerar da take kai ya zauna yana sauraren gaisawarsa da anni
"Barka da yamma" khalipha ya fada,waiwayowa alhajin yayi yana dubansa
"Kai wato ba'a isa a ganka gidan kowa ba saidai a naku gidan ko?" Murmushi ne ya subuce masa,sai ya kada kansa kawai yana duban alhajin,idan maye yaci ya manta uwar da ai ba zata manta ba,shi alhajin ya manta furucinsa na qarshe a garesu kenan
"To ni gani nazo da kaina da nacewa zeenatu tace ina nemanka kayi funfurus kaqi zuwa" alhajin ya sake fada yana tsatstsareshi da ido
"Yanayin aiki ne,ba kowanne waje yake barina naje ba....gani...Allah yasa ba laifi nayi ba" ya qarashe maganar ta sigar gatse,gyara zamanshi yayi bayan ya gyara zaman babbar rigarsa
"Wato muhammadu so kake kafi qarfinmu ko?,ka tasamma qin aure qiri qiri kasa qafa kayi fatali da sunnar ma'aiki,kana girma shekarunka na ja qannanka na tasowa,ga 'yar uwarka nan jiddin tana gidan nan tana qaunarka amma ko wannan baisa ka duba ba?....yanzu haka ka zaba kenan?" Murmushi ya sake yi,abubuwa masu yawa na dawo masa cikin kwanyar kansa,yana sake godiya ga Allah kan komai da yayi masa a rayuwa,baiwa masu tarin yawa da shi kansa baisan adadinsu ba,miqewa yayi tsaye hannayensa zube cikin aljihunsa,idonsa ya sauka kan zeenart da kanta ke sunkuye tana wasa da yatsunta ita ala dole kunya sai faman zuba murmushi take
"Kayi haquri alhaji ba haka na zaba ba.....idan Allah ya kaimu ranar asabar kwana biyu masu zuwa za'a kaimin kudin aure harma da sadaki....shikenan?" Baki ya soma budewa,yana jin zallar farinciki,ga tunaninsa komai ya fada ne tsakaninsa da zeenatun,amma maganar da khaliphan ya dora da ita a sanda yake yunqurin barin falon ita ta kadar da duk nutsuwarsa ta kuma sanya gumi ya soma karyo masa
"Duk da ban sanar da mahaifin yarinyar ba,amma zanyi qoqarin shaida masa yau zuwa gobe in sha Allahu" daga haka ya fice ya bar alhajin cikin rudani
[1/6, 11:50 AM] Om Muhammadiyya: Shiru ne ya ratsa falon kafin daga bisani kukan zeenart ya karade falon,kuka take sosai mai sauti tana raba ido tsakanin mahaifinta da anni,hakan ya sake tunzura alhajin wanda yaketa qoqarin share gumin goshinsa,miqewa tsaye yayi cikin banbami yake cewa zeenart
"Ke,tashi mu tafi....tashi nace maza....mu za'a yiwa wulqanci aci mana mutunci?,mu za'a nunawa qaryar arziqi,dadin abin ai tun kafin ayi daran akai kwandi" a tausashe anni ke dubansa
"Haba bashir....abun baikai haka ba don Allah...ka zauna"
"In zauna inyi me hajiya A'i?....me zan zauna inji?,ina cewa a gabanki ya fadi komai baki dakatar da shi ba...ina tsammatarma hadin baki ne kukayi saboda kada a auri yaranmu...to babu komai....shi yasa zumunci ya shiga halin ni 'yasu,dole zumunci ya lalace,tashi ki wuce mu tafi" kada kai anni take can qasan zuciyarta mamaki na kaikawo na maganganun da alhajin keyi,duk da haka ta danne
"Kayi haquri dai duk da haka,ka barmin zeenatun"
"Mai zata zauna tayi muku...ai magana ta riga ta qare"ba yadda annin bata yi ba amma ya qeqashe qasa yaqi,tana zaune tana kallonsu ya tasata ta hada kayanta suka zo suka fice,ajiyar zuciya kawai ta saki,me hali baya fasa halinsa,lallai khalipha shi yasa meya gani...shi yasan wanne tunani yayi daya sanyashi qin duk wata yarinya dake cikin ahalin nasu.

Khalipha ne ya sake dawowa falon,harararshi annin tayi sai ya saki murmushi yana takowa inda annin ke zaune,duk sanda yaga ta harareshin yasan ya aikata mata laifi kenan
"Kaji dadi.....ka hadani da dan uwan mahaifinka" gabanta ya qaraso dariya tana kubce masa,kan gwiwoyinsa ya durqusa ya kama hannayenta
"Ki cire dukkan wata damuwa anni dangane da mutanen nan,kin dade da sanin cewa babu wani abu da zakiyi ki fita a wajensu,Allah shine shaidarki,mutane masu adalci suma sun shaida hakan....banda ke anni da wata ce ko kallo basu isheta ba bare su jibanceta ko su jibanci nata yaran,anni.....bazan iya auren kowacce yarinya data fito daga zuri'armu ba ko daga sama ta sauko kuwa....kiyi haquri karki tambayeni dalili saboda suk duniya kinfi kowa sanin dalilin....ki manta da su da lamuransu....kici gaba da duk abinda kikega zaki iya kuma shine dai dai hat a gaban mahaliccinmu" shiru tayi tana tunani,ba shakka duk maganar khaliphan haka take tana bisa hanya,ita kanta tafi kowa sanin wuyar data sha da shi kafin yaci gaba da mu'amala da dangin nashi,amma a yanzun saika rantse babu komai tsakaninsu basu taba aikata musu komai ba,don indai anni ta bada umarnin yayi abu zai cikashi duk wuyarshi
"Yanzu ina kayan abincin da za'a kaima baffan ka"
"Wannan maganar an gamata....haidar kawai nake jira yazo ya kai" ya qarasa fadi yana duban idanunta
"Yanzu jibin za'a je gidansu yarinyar?"
"Eh anni...in sha Allah...inason mutanen nan ne su qyaleni suda yaransu...koda kika ga zeenat ta tafi ina mai tabbatar miki zata dawo...ko bata dawo ba wata na nan zuwa"kai take kadawa sannan ta bude baki
"shikenan,Allah ya sanya alkhairi yasa a yi a sa'a ya kade dukkan fitina.....saika gayawa dukan wanda ya dace kada wani yaji daga baya yayi qorafin bai sani ba"
"Ko sunzo ma mota daya zan bada,sauran suje a motar haya.....har yau bani da komai sai rufin asirin Allah da shi zanci gaba da neman aurenta idan har zata iya zama da ni a haka" dariya ya bawa anni...khaliphan ya fita daban da matasan zamani...matasan dake neman kayan aro da zasu sanya ariqa musu kallon masu arziqi su yaudaro yarinya su aureta,yau shi gashi da dukkan wani abu da ake da buqata amma boyesu yake yana maida kansa ruwa da zubin maqasqanciyar rayuwa,bai bar falon ba saida haidar din yazo ya miqa masa saqonnin duk wadanda za'a kaiwa abincin sannan ya fice zuwa gidan babban wan mahaifinsa suyi maganar zuwa gidansu ayshatun.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Chapter 28 · 0% Book details