Sashe 68
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gab da zata shiga wayarta tayi ringing,saita dakata tana dubawa,hanan ce,dariya ta dan saki tasan cewa akwai wata a qasa tunda ta kirata,dagawa tayi da sallama ilai kuwa karadin hanan din ya cika kunnenta,ko gaisawa bata tsaya sunyi ba tace
"Nida saddiq...yace na cikashi da zancan aysha naqi na hadaku ku gaisa,na gaya mishi ba laifi na bane,ke din ce kifin rijiya ce baki zuwa ko ina" dariya aysha tayi
"Bani shi mu gaisa" miqa masan tayi ya amsa suka soma gaisawa,sosai yake da so jama'a kamar hanan din,sun dan taba hira kadan kana daga bisani ya zolayeta kan ta kula mishi da gimbiyarsa,sannan zayazo a raba gardama kan wanda yafi wani son dan uwanshi,shi yace ya fi sonta ita tace shi,da dariya aysha ta katse kiran jin musu na niyyar barkewa tsakanin hanan din da saddiq,tana dariyar abin ta bude sashen ta shiga,abu na farko data soma cin karo da shi daya daga cikin window size na hoton khalipha wanda ya fito tarrr kamar kayi masa magana ya amsa ka,fuskarshi qunshe da murmushi wanda hakan ya sake bayyana kyanshi,gabanta ne yadan fadi,sai taji kaman shine a gabanta yake kallonta,dauke kai tayi taci gaba da shiga sai kuma ta kasa,sake maida kanta tayi zuwa ga hoton,ta soma takawa a hankali zuwa sashen da hoton yake.
Ta jima tsaye gaban hoton tana kallonshi,sai ta sanya hannunta a hankali ta shafi qafafunsa,hakanan tausayinsa taji ya kamata,yabar gida yabar ahalinsa duk saboda ci gaban familynsa,tsahon watanni baiga mahaifiya mafi soyuwa a gareshi ba ko wani dan uwansa,cikin ranta ta soma jera masa addu'ar samun dacewa da nasara a rayuwarsa,ba shakka khalipha wani babban jigo ne a rayuwarta,yana daya daga cikin shika shikan da komai nisan rabuwa komai tsahon lokaci ko zamani bazaiyiwu ta manta da wanzuwarsa ba,iyakacin zamanta a gidan ta shaida jatumtarsa a rayuwa,jarumi ne kuma tsayayye na gaske,zata so taji wani abu daga tarihin rayuwarshi daga bakinsa,ta tabbata akwai gwagwarmaya ba qarama ba,a hankali ta sauke hannunta ta juya,sai hanan da saddiq suka fado mata a rai,murmushi ta saki tana ayyana dadin da soyayya ke da shi,sai ta dinga gwada kanta a matsayinsu,wani tunani ne ya fado mata a rai wanda ya tilastata daga kai ta dubi daya hoton khalipha dake gabanta,wanda yana zaune ne saman wata irin kujera ya dora qafarshi daya kan daya,kai ta girgiza tana gayawa kanta bamai yiwuwa bane,khaliphan?,da hanzarin ta watsar da tunanin ta shiga nazarin sashen,akwai 'yar qura bamai yawa ba,wanda hakan ke alamta ana shigowa a share lokaci lokaci,sosai ta gayara wajen tsaf,take komai ya koma fes,ta rurruf abubuwan da tasan zasu qara qura ta sake dauraye jikinta ta debi kayan da take buqata tabar sashen.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
"Wayyo bayana" aysha ta furta bayan ta dago daga durqushen da tayi tana hada kayanta,ajiye littafin hannunta hanan tayi tana dubanta
"Wai karkicemin wannan satin duk sai kin rigamu tafiya gida?da alama ma dai ni kadai zaku bari,don maman hunaifa ma jiya najita tana waya da abban hunaifa abuja zatayi weekend" Sai data samu gefan gadonta ta zauna tana miqe qafarta sannan ta amsa mata
"Wallahi haka kawai wannan karon duk hankalina yayi gida....ki shirya don Allah mu wuce wajen wankin kan nan sai nayi zan wuce"mirginawa hanan tayi daga kwancen da take zuwa daya bangaren
"Wallahi yau kasala nakeji da gajiya...anya zan iya zuwa kuwa?" Harararta ayshan tayi
"Baki isa ba kuwa,ki tashi kawai ki shirya" hakanan hanan ta miqe a kasalance ta shiga wanka ta fito ta shirya suka fice.
Tare suka jero suna 'yan hirarrakinsu jifa jifa,idan sunga wanda suka sani su tsaya su gaisa wani lokaci har sukan dan taba hira kafin su wuce.
Dab da zasu wuce wata mota hanan ta taba aysha
"Gafa mutumin can,kinga mota zai bude amma ya tsaya satar kallonki"
"Wafa?" Ayshan ta tambaya tana duban hanan
"Waye banda daddy huguma,kinsan Allah gayen ya hadu,a nan makarantar yake geology ya karanta suka riqeshi suka bashi lacturing,da qyar ma idan ba zuwa sabuwar semester ku hadu da shi ba,ki bashi dama kawai aysha wallahi,ya hada komai fa" kallonta ayshan tayi taja tsaki tana kauda kai,gabanta taji yana faduwa
"Kekam hanan kinga dacewar haka?,kinsan wayeshi ne?,pls karki sake wannan maganar" dariya da mamakinta take boyewa,batasan me yasa ayshan ta tsani ayi mata zancan wani ba,ta tsani ace wani na sonta
"Allah ya baki haquri,amma maganar gaskiya karki bari wannan damar ta subuce miki,ina miki sha'awarsa"
"Toh naji" ta fada da alama ta qosa da zancan
"Aysha sai yaushe zaki bawa mutane dama?,waikekam soyayya bata burgeki?,kinsan bakasan dadin rayuwa ba harsai kaso kaima ansoka?,rayuwar da babu soyayya nikam ina tunanin wace iriyar rayuwa kenan?" Hanan ta fada da alamun da gaske take magana,shuru aysha tayi tana saurarenta,saita dinga jujjuya maganar hanan din cikin ranta.
Gab da zasu fice daga makarantar motar saddiq ta sako kai,ja hanan tayi ta tsaya tana dubanshi cikin murmushi sanda yayi parking ya fito
"Wato ba zata kayi niyyar yimin kenan?"murmushi yake yana dubanta
"Tuba nake ranki ya dade,na kasa zama ne kawai naji inason ganinki"
"Yayi kyau,kaman kasan tunaninka nima nake"
"Zuciya daya"
"Ruhi daya" sai suka sanya dariya shi da ita,aysha na gefe tana kallonsu,burgeta suke sosai yadda suke son junansu
"Ranki ya dade" saddiq ya ce da aysha
"Tare da naka..Allah yasa ba zuwa kayi ka hanata rakani ba"
"Ni na isa,ina zuwa?"
"Zamu wankin kaine"
"To bismillah ku shigo nayi rakiya" ba musu suka qarasa jikin motar,hanan ta shiga gaba aysha na baya yaja suka tafi,cikin motarma hirarsu suke,ba komai aysha keji ba,wani lokaci saidai taji dariyarsu har suka isa wajen,cewa yayi zai jirasu,saboda haka tabar hanan cikin motar ita ta shiga aka soma yi mata.
Awa uku aka gama musu komai har lallen,yayi kyau kuwa fiye da ko yaushe ita kanta taga haka,kaman wata amarya haka tayi fes tayi kyau,wannan karon haka tabar gashinta,maimakon daa da ake mata manya kalba guda biyu ko uku,ta saki jelarta kota hadeta da ribbom.
Da suka dawo ma tare ta barsu ta shige hostel din,ta taras maman hunaifa ta dawo harta musu abinci,sallah kawai tayi ta zauna suka ci abincin suna hirarsu har zuwa sanda hanan ta shigo.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe goma drivern gidan anni ya iso
"Toh sai Allah ya kaimu monday kuma"
"Anya ko zako ma dawo monday din kuwa?" Hanan ta fada tana tsokanarta,waiwayowa tayi tana kallontq cikin harara
"Me kika gani?" Dariya tayi
"A'ah babu komai,wannan zumudi haka,kodai kinyi kamu ne?"tsaki ta saki tana dariya
"baki da amsa"
"Idan tayi wari maji" hanan ta fada tana qyalqyalewa da dariya,har bakin mota hanan din ta rakota sukai sallama,don maman hunaifa tun safe ta fita.
Cikin girmamawa dirvern ya fito xai amshi kayan hannunta ta dakatar da shi
"Yi zamanka malam shehu" ba qarami girmansa take gani ba,saboda a qalla ya kusa haifarta,haka shima ba qaramin girmamata yake ba saboda yadda take ganin mutuncinsa,cikin mota suna tafe suna hira jifa jifa,duk da rabin hankalinta na kan dan qaramin littafin dake hannunta,wanda duka lacture din jiya ce.
Da yammaci suka iso gidan,kaman kullum anni na zaune a falo tana kallon africa t.v 3,dukkansu fuskokinsu qunshe da murmushi,anni ta amsa sallamar ayshan
"Lale da 'yan makaranta"
"Anni sannu da gida" ta fada tana zama qasa kaman yadda al'adarta take yawanci idan annin na zaune kan kujera
"Yauwa ayshatu" gaisawa sukai cikin kewar juna annin na tambayarta hanya da sauran al'amura,daga bisani annin da kanta tace taje ta huta,ba musu kuwa ta wuce dakin ta,wanka tayi tana saman gado zata shafa mai a nan bacci yayi awon gaba da ita,bata farka ba sai la'asar,shi dinma kiran wayar aliya ya tada ta
"Kin dawo kenan"
"Tun azahar ma,wannan satin duka makarantar naji ta isheni gida nakeso"
"Da kyau,ina hanya to ki jireyeni" cikin zumudi ta amsa mata dan sun dan kwan biyu basu hadu da aliyar ba,alwala ta daura ta shafa mai da hoda ta sauya kaya ta tada sallah sannan ta fito falon.
Amal ce kawai zaune a falon da alama bata jima da zuwa ba don har mayafinta na kafadarta,hada ido sukai da aysha,ayshan ta sakar mata murmushi,yayin da gaban amal din ke faduwa,kullum rana ta Allah ayshan sauyawa take kamar wadda ake canzawa,komanta qara kyau da fitowa yake kaman ba ayshan data sani watannin baya da suka shude ba,duk sa cewa ko dacan dinma ayshan a hade take,saidai kanta ya bude sosai fiye da yadda ta santa
"Amal ce?"aysha ta fada tana murmushi
"wallahi" ta amsata a taqaice tana jin kishinta na ratsata,tana satar kallon yadda fatar ayshan tayi kyau,jan lallen yatsunta yayi matuqar zama ado a gareta.
"Kwana da yawa....sau wajen hudu ina zuwa weekend bana samunki"
"Nima makaranta na koma banda cikakken lokacin kaina"
"Ma sha Allah,abu yayi kyau Allah ya taimaka" ta fada cikin fara'a ba tare da ta kawo komai ranta ba ta wuce kitchen.
"Nida saddiq...yace na cikashi da zancan aysha naqi na hadaku ku gaisa,na gaya mishi ba laifi na bane,ke din ce kifin rijiya ce baki zuwa ko ina" dariya aysha tayi
"Bani shi mu gaisa" miqa masan tayi ya amsa suka soma gaisawa,sosai yake da so jama'a kamar hanan din,sun dan taba hira kadan kana daga bisani ya zolayeta kan ta kula mishi da gimbiyarsa,sannan zayazo a raba gardama kan wanda yafi wani son dan uwanshi,shi yace ya fi sonta ita tace shi,da dariya aysha ta katse kiran jin musu na niyyar barkewa tsakanin hanan din da saddiq,tana dariyar abin ta bude sashen ta shiga,abu na farko data soma cin karo da shi daya daga cikin window size na hoton khalipha wanda ya fito tarrr kamar kayi masa magana ya amsa ka,fuskarshi qunshe da murmushi wanda hakan ya sake bayyana kyanshi,gabanta ne yadan fadi,sai taji kaman shine a gabanta yake kallonta,dauke kai tayi taci gaba da shiga sai kuma ta kasa,sake maida kanta tayi zuwa ga hoton,ta soma takawa a hankali zuwa sashen da hoton yake.
Ta jima tsaye gaban hoton tana kallonshi,sai ta sanya hannunta a hankali ta shafi qafafunsa,hakanan tausayinsa taji ya kamata,yabar gida yabar ahalinsa duk saboda ci gaban familynsa,tsahon watanni baiga mahaifiya mafi soyuwa a gareshi ba ko wani dan uwansa,cikin ranta ta soma jera masa addu'ar samun dacewa da nasara a rayuwarsa,ba shakka khalipha wani babban jigo ne a rayuwarta,yana daya daga cikin shika shikan da komai nisan rabuwa komai tsahon lokaci ko zamani bazaiyiwu ta manta da wanzuwarsa ba,iyakacin zamanta a gidan ta shaida jatumtarsa a rayuwa,jarumi ne kuma tsayayye na gaske,zata so taji wani abu daga tarihin rayuwarshi daga bakinsa,ta tabbata akwai gwagwarmaya ba qarama ba,a hankali ta sauke hannunta ta juya,sai hanan da saddiq suka fado mata a rai,murmushi ta saki tana ayyana dadin da soyayya ke da shi,sai ta dinga gwada kanta a matsayinsu,wani tunani ne ya fado mata a rai wanda ya tilastata daga kai ta dubi daya hoton khalipha dake gabanta,wanda yana zaune ne saman wata irin kujera ya dora qafarshi daya kan daya,kai ta girgiza tana gayawa kanta bamai yiwuwa bane,khaliphan?,da hanzarin ta watsar da tunanin ta shiga nazarin sashen,akwai 'yar qura bamai yawa ba,wanda hakan ke alamta ana shigowa a share lokaci lokaci,sosai ta gayara wajen tsaf,take komai ya koma fes,ta rurruf abubuwan da tasan zasu qara qura ta sake dauraye jikinta ta debi kayan da take buqata tabar sashen.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
"Wayyo bayana" aysha ta furta bayan ta dago daga durqushen da tayi tana hada kayanta,ajiye littafin hannunta hanan tayi tana dubanta
"Wai karkicemin wannan satin duk sai kin rigamu tafiya gida?da alama ma dai ni kadai zaku bari,don maman hunaifa ma jiya najita tana waya da abban hunaifa abuja zatayi weekend" Sai data samu gefan gadonta ta zauna tana miqe qafarta sannan ta amsa mata
"Wallahi haka kawai wannan karon duk hankalina yayi gida....ki shirya don Allah mu wuce wajen wankin kan nan sai nayi zan wuce"mirginawa hanan tayi daga kwancen da take zuwa daya bangaren
"Wallahi yau kasala nakeji da gajiya...anya zan iya zuwa kuwa?" Harararta ayshan tayi
"Baki isa ba kuwa,ki tashi kawai ki shirya" hakanan hanan ta miqe a kasalance ta shiga wanka ta fito ta shirya suka fice.
Tare suka jero suna 'yan hirarrakinsu jifa jifa,idan sunga wanda suka sani su tsaya su gaisa wani lokaci har sukan dan taba hira kafin su wuce.
Dab da zasu wuce wata mota hanan ta taba aysha
"Gafa mutumin can,kinga mota zai bude amma ya tsaya satar kallonki"
"Wafa?" Ayshan ta tambaya tana duban hanan
"Waye banda daddy huguma,kinsan Allah gayen ya hadu,a nan makarantar yake geology ya karanta suka riqeshi suka bashi lacturing,da qyar ma idan ba zuwa sabuwar semester ku hadu da shi ba,ki bashi dama kawai aysha wallahi,ya hada komai fa" kallonta ayshan tayi taja tsaki tana kauda kai,gabanta taji yana faduwa
"Kekam hanan kinga dacewar haka?,kinsan wayeshi ne?,pls karki sake wannan maganar" dariya da mamakinta take boyewa,batasan me yasa ayshan ta tsani ayi mata zancan wani ba,ta tsani ace wani na sonta
"Allah ya baki haquri,amma maganar gaskiya karki bari wannan damar ta subuce miki,ina miki sha'awarsa"
"Toh naji" ta fada da alama ta qosa da zancan
"Aysha sai yaushe zaki bawa mutane dama?,waikekam soyayya bata burgeki?,kinsan bakasan dadin rayuwa ba harsai kaso kaima ansoka?,rayuwar da babu soyayya nikam ina tunanin wace iriyar rayuwa kenan?" Hanan ta fada da alamun da gaske take magana,shuru aysha tayi tana saurarenta,saita dinga jujjuya maganar hanan din cikin ranta.
Gab da zasu fice daga makarantar motar saddiq ta sako kai,ja hanan tayi ta tsaya tana dubanshi cikin murmushi sanda yayi parking ya fito
"Wato ba zata kayi niyyar yimin kenan?"murmushi yake yana dubanta
"Tuba nake ranki ya dade,na kasa zama ne kawai naji inason ganinki"
"Yayi kyau,kaman kasan tunaninka nima nake"
"Zuciya daya"
"Ruhi daya" sai suka sanya dariya shi da ita,aysha na gefe tana kallonsu,burgeta suke sosai yadda suke son junansu
"Ranki ya dade" saddiq ya ce da aysha
"Tare da naka..Allah yasa ba zuwa kayi ka hanata rakani ba"
"Ni na isa,ina zuwa?"
"Zamu wankin kaine"
"To bismillah ku shigo nayi rakiya" ba musu suka qarasa jikin motar,hanan ta shiga gaba aysha na baya yaja suka tafi,cikin motarma hirarsu suke,ba komai aysha keji ba,wani lokaci saidai taji dariyarsu har suka isa wajen,cewa yayi zai jirasu,saboda haka tabar hanan cikin motar ita ta shiga aka soma yi mata.
Awa uku aka gama musu komai har lallen,yayi kyau kuwa fiye da ko yaushe ita kanta taga haka,kaman wata amarya haka tayi fes tayi kyau,wannan karon haka tabar gashinta,maimakon daa da ake mata manya kalba guda biyu ko uku,ta saki jelarta kota hadeta da ribbom.
Da suka dawo ma tare ta barsu ta shige hostel din,ta taras maman hunaifa ta dawo harta musu abinci,sallah kawai tayi ta zauna suka ci abincin suna hirarsu har zuwa sanda hanan ta shigo.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe goma drivern gidan anni ya iso
"Toh sai Allah ya kaimu monday kuma"
"Anya ko zako ma dawo monday din kuwa?" Hanan ta fada tana tsokanarta,waiwayowa tayi tana kallontq cikin harara
"Me kika gani?" Dariya tayi
"A'ah babu komai,wannan zumudi haka,kodai kinyi kamu ne?"tsaki ta saki tana dariya
"baki da amsa"
"Idan tayi wari maji" hanan ta fada tana qyalqyalewa da dariya,har bakin mota hanan din ta rakota sukai sallama,don maman hunaifa tun safe ta fita.
Cikin girmamawa dirvern ya fito xai amshi kayan hannunta ta dakatar da shi
"Yi zamanka malam shehu" ba qarami girmansa take gani ba,saboda a qalla ya kusa haifarta,haka shima ba qaramin girmamata yake ba saboda yadda take ganin mutuncinsa,cikin mota suna tafe suna hira jifa jifa,duk da rabin hankalinta na kan dan qaramin littafin dake hannunta,wanda duka lacture din jiya ce.
Da yammaci suka iso gidan,kaman kullum anni na zaune a falo tana kallon africa t.v 3,dukkansu fuskokinsu qunshe da murmushi,anni ta amsa sallamar ayshan
"Lale da 'yan makaranta"
"Anni sannu da gida" ta fada tana zama qasa kaman yadda al'adarta take yawanci idan annin na zaune kan kujera
"Yauwa ayshatu" gaisawa sukai cikin kewar juna annin na tambayarta hanya da sauran al'amura,daga bisani annin da kanta tace taje ta huta,ba musu kuwa ta wuce dakin ta,wanka tayi tana saman gado zata shafa mai a nan bacci yayi awon gaba da ita,bata farka ba sai la'asar,shi dinma kiran wayar aliya ya tada ta
"Kin dawo kenan"
"Tun azahar ma,wannan satin duka makarantar naji ta isheni gida nakeso"
"Da kyau,ina hanya to ki jireyeni" cikin zumudi ta amsa mata dan sun dan kwan biyu basu hadu da aliyar ba,alwala ta daura ta shafa mai da hoda ta sauya kaya ta tada sallah sannan ta fito falon.
Amal ce kawai zaune a falon da alama bata jima da zuwa ba don har mayafinta na kafadarta,hada ido sukai da aysha,ayshan ta sakar mata murmushi,yayin da gaban amal din ke faduwa,kullum rana ta Allah ayshan sauyawa take kamar wadda ake canzawa,komanta qara kyau da fitowa yake kaman ba ayshan data sani watannin baya da suka shude ba,duk sa cewa ko dacan dinma ayshan a hade take,saidai kanta ya bude sosai fiye da yadda ta santa
"Amal ce?"aysha ta fada tana murmushi
"wallahi" ta amsata a taqaice tana jin kishinta na ratsata,tana satar kallon yadda fatar ayshan tayi kyau,jan lallen yatsunta yayi matuqar zama ado a gareta.
"Kwana da yawa....sau wajen hudu ina zuwa weekend bana samunki"
"Nima makaranta na koma banda cikakken lokacin kaina"
"Ma sha Allah,abu yayi kyau Allah ya taimaka" ta fada cikin fara'a ba tare da ta kawo komai ranta ba ta wuce kitchen.