Sashe 76
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da sauri daya daga cikin yaran ya budewa khalipha bayan daya daga cikin motocin ya shige,aysha ce ta rufa masa baya tana shiga ta rufe qofar bayan ta dage glashin sashen datake wanda shi kadaine a sauke,sun glass din dake hannunta ta manna a fuskarta wanda ya qarawa shigar tata armashi da kwarjini,ya kuma fitar da kyanta qwarai,ta fuske kaman batasan me ake ba,shi kuwa driver ganin khaliphan da aysha sun shigo sai ya tada mota ya soma reverse don fita daga harabar gidan,mamaki fal zuciyar khalipha yake dubanta,tana ji a jikinta yana kallonta amma saita fuske taqi duban sashen da yake
Yadda ta tsume taci magani saiya fito da dan qaramin bakinta wanda ya qara mata kyau sosai,sai yaji hakan datayi ta burgeshi,murmushi yayi a boye yana kada kai,daga jiya zuwa yau duk acting dinta jinsa yake tamkar da gaske take har cikin jikinsa
Baisan me yasa yake yawan jin baqin lamura a kanta ba wanda baida tabbacin meye su,qarar wayarta ita ta sanyata janyo jakarta dake gefe ta bude ta ciro wayar tata,aliya ke kiranta,murmushi ta saki har kumatunta na lotsawa ta latsa cikin farinciki ta kara a kunneta,cikin yanayi na sabo da shaquwa suka soma gaisawa,duk abinda take idanunshi a kanta yana karantar yanayinta,kaf tsayin rayuwarsa bai damu da wata mace ba bare ya tsaya karantarta ba baya ga anninsa,sai yanzu gashi ya dora hankalinsa kacokam kan ayshan,idanunsa ya janye ya lumshesu ganin wayar tasu bata qare bace yana jin sautin muryarta cikin kunnensa gaba ratsa kowacce gaba ta jikinsa
"Ya salam" ya ambata qasa qasa yana jan earpiece dinsa ya cusa a kunnensa dan ya daina jin muryarta ko ya samu sassauci kan yadda tsigar jikinsa ke tashi.
Har suka isa airphort basu gama wayar ba,saida motar ta tsaya sannan sukai sallama da aliys kan zata kirata.
A tsorace take taka matattakalar jirgin,karo na farko a rayuwarta data tana shigowa airphort ma baki daya balle ta doshi jirgi,yana daga gefanta ya lura da tsoron dake tattare da ita,a hankali ya matsa gefanta ya zura hannunshi daga gefan kafadarta ya jinginata da tashi kafadar,juyowa tayi suka hada idanu,saiya mata nuni da qwayar idanunshi da wasu ma'aurata dake gabansu hannunsu cikin na juna,sai ta sako ajiyar zuciya tana shaqar qamshin turarensa da har yau ta rasa wanne iri ne,haka koda wasa bata taba jin mai irin qamshin ba.
Sosai ya matse hannunsa cikin nata sanda jirgin ke shirin tashi,ruf ta rufe idanunta tana karanto addu'ar hawa abin hawa,wanda hakan ya qara mata nutsuwa,saida komai ya daidaita sannan ta sauke numfashi ta bude idanunta a hankali sai cikin na khalipha,girarshi ya daga mata alamar tambaya,saita girgiza kai tana sake maida idanunta ta lumshe.
Qarfe sha daya na safe suka sauka a legos abinka da tafiyar jirgi,wasu motoci ne guda hudu iri daya sak masu dauke da wani tambari da bata lura dana meye ba suke tsaye suna jiran isowarsu,daya daga cikin motocin aka budewa khalipha ya shiga aysha tabi bayansa,daga bisani motar ta gyara tsaiwa ta fice daga airphort din sauran na biye da su,dukka hankalinta nakan titunan da suke wucewa,karon farko data taba barin jihar kano zuwa wata jaha ta daban wadda bata taba zuwa ba,saidai taji sunanta kawai a baki,sosai garin ya burgeta,yanayin weather dinsu irin wadda takesoce,don a sannan suna samun saukar ruwan sama,duk da bai kankama ba amma hakan ya sake qawata yanayin garin da iska mai dadi da sanyi.
Joygate hotel and suites suka sauka wanda ke lateef salami street don yafi kusa da airphort,a harabar hotel din duka sauran suka dakata shi da ita ne kawai suka shiga ciki,executive suite yayi booking dama tun daga gida,shi ya bude qofar yana kan gaba tana binsa a baya har cikin dakin,cikin yan mintina qalilan aka shigo da abinci da sauran abinda mutum zai buqata
"Ki huta nan da two to three hours zan dawo ki shirya kafin nan zamu fita"
"Ohk" ta fada tana gyada kai
"Akwai damuwa?" Ya tambayeta manyan idanunshi a kanta,kai ta kada alamun a'ah sai ya juya ya fice yana ja mata qofar idanunshi a kanta.
Dakin tabi da kallo yayi mata kyau sosai kaman ba cikin hotel ba,gefan gadon ta samu ta zauna tana tunanin me sukazoyi lagos?,har yau bata san dalilin tafiyar tasu ba
Wayarta ta ciro ta kira anni ta sanar mata sun iso,sannan ta duba taga da saura kafin lokacin sallar azahar ya shiga,sai kawai ta kunna tv din dake dakin ta sauya tasha zuwa arewa.
Qarfe daya da rabi na rana tayi sallah,sannan ta bude abincin da aka kawo mata taci,sai daya dan fada mata sannan ta shiga bandakin dakin ta sake wanka ta fito ta shirya cikin wani material mai azabar kyau da tsada mint green cotton ne amma mai dan qarfi,ta nannade gashinta tayi daurin nan da ake a gaban goshi wanda gashinta data yiwa parking ta kama jelarsa ta kitsa ya zama jela daya ya fito ta qasan daurin,sarqa da dan kunne da kuma abin hannun da tayi amfani dasu duka set ne sirara masu ruwan gold,ba qaramin kyau tayi ba fuskarta tayi fresh sosai,gogewar da fatarta ta sakeyi ita kanta yana mata kyau,dai data tsaya gaban mudubi ta tabbatar komai yayi sannan ta koma saman kujerar.
Tana shirin xama akayi knocking qofar,saita fasa zaman ta isa bakin qofar ta murda muqullin ta bude gami da ja baya,khalipha ne ya shigo hannunshi riqe da top din suit dinshi daya hannun kuwa wayoyinsa ne,kana kallonshi ko ba'a gaya maka ba kasan a gajiye yake,da kallo ya bita cikin nutsuwa yake qarewa adonta kallonta,ba qaramin burgeshi adon nata yayi ba,sai yaga kaman canza ta akayi daga fitarsa zuwa dawowarsa,yana son qaryata hakan amma zuciyarsa taqi karba
"Sannu da zuwa" ta fada cikin sanyinta tana mamakin yadda yau ya ware ido yake kallonta kai tsaye
"Yauwa" ya fada yana zama saman kujea gami da cire takalmi da safar qafarshi,tana daga gefe tana wasa da yatsunta saboda yadda kallonshi ya mata nauyi yayin da shi kuma yake ci gaba da satar kallonta,shuru ya ratsa dakin,sai daya rage kayan jikinsa sannan ya tambayeta me suka kawo mata,tashi tayi ta dauko masa ta bude mishi
"Zubamin" yw fada yana kallon lallenta da kamar kullum turashi ake,nan tayi serving dinsa yaci sannan shima ya shiga wanka.
Tana tsaka da kallon maimacin wani indian hausa a tauraruwa t.v ya bude qofar bandakin ya fito lullube da towel a jikinsa,ya daura wani duk da mai yalwa ne amma duka singalalin qafarsa a waje yake,dauke kanta tayi da sauri tana jin wani feeling cikin ranta,ya jima kafin daga bisani qamshin turarensa ya game dakin,wanda ya haifar mata da kasala,ta lumshe idanuwanta tana jin motsinsa cikin dakin,bata bude ba har sai data tabbatar daya gama shiryawa
"Mu wuce ko?" Ya fada yana sanya takalma a qafarsa sabanin wadanda ya cire daxun,sai a sannan ta bude idanunta,yayi kyau cikin dinkin kufta,batasan me yasa idan ya saka manyan kaya ba saiya koma mata kamar wani saraki,cikin mutuwar jiki da kasala ta miqe ta soma nannadawa jikinta laffaya,ta cikin mirrow yake kallonta,duk wani motsi idan tayi shape dinta ne ke fita,irin shape da daidaikun mata Allah ya yiwa baiwa dashi,ajiyar zuciya ya kuma saki can qasa,baisan me yake damunshi ba sam,baisan me yasa baya iya controlling idanunshi ba a kanta
Tare suka jero har zuwa bakin motocin dake fake a wajen,ga mamakinta da kanshi ya bude mata gidan gaba,saita daga kai ta kalleshi suka hada ido,kafeta da ido yayi yana mata nuni da hannunshi kan ta shiga,a hankali ta zura jikinta kafin ya sanya qafafunta ya maida murfin motar ya rufe sannan ya zagaya,sai taga ya shiga sashen driver ga mamakinta ya sanya muqulli ya tada motar da alama da kanshi zaiyu driving,dubanshi take da mamaki saiya waiwayo caraf suka hada ido,girarshi ya dage mata
"Me naci ban baki ba?,karki cinyeni mana wannan kallo haka tun daxun?" Kunya taji saita kauda kai tans yunqurin danne murmushin daya subuce mata,cikin salon kare kai tace
"Da wanne idon kasan ina kallonka,ni me zan kalla" yanq tada motar ya bata amsa
"Abubuwa da yawa mana"
"Kamar?" Ta tambayeshi tana murmushi fuskarta na kallon window din motar ta yadda bazai iya ganin fsukarta ba
"Idan kin isa juyo ki kalleni saina baki amsa" tilas murmushin dake kan fuskarta ya subuce saidai bata yarda sautinsa ya fita ba
"Kidai rage kallona karki je ki soma sona,bayan ni kuma na riga dana siyar" dan dakewa tayi jin abinda yace,saboda ita batayi qorafin yawan kallonta da yakeyi ba shine shi xaiyi mata qorafi,shuru ne yaci gaba da ratsawa a motar,baka jin komai sai tashin qarar ac,da kuma anguwanni da suketa wucewa.
Yadda ta tsume taci magani saiya fito da dan qaramin bakinta wanda ya qara mata kyau sosai,sai yaji hakan datayi ta burgeshi,murmushi yayi a boye yana kada kai,daga jiya zuwa yau duk acting dinta jinsa yake tamkar da gaske take har cikin jikinsa
Baisan me yasa yake yawan jin baqin lamura a kanta ba wanda baida tabbacin meye su,qarar wayarta ita ta sanyata janyo jakarta dake gefe ta bude ta ciro wayar tata,aliya ke kiranta,murmushi ta saki har kumatunta na lotsawa ta latsa cikin farinciki ta kara a kunneta,cikin yanayi na sabo da shaquwa suka soma gaisawa,duk abinda take idanunshi a kanta yana karantar yanayinta,kaf tsayin rayuwarsa bai damu da wata mace ba bare ya tsaya karantarta ba baya ga anninsa,sai yanzu gashi ya dora hankalinsa kacokam kan ayshan,idanunsa ya janye ya lumshesu ganin wayar tasu bata qare bace yana jin sautin muryarta cikin kunnensa gaba ratsa kowacce gaba ta jikinsa
"Ya salam" ya ambata qasa qasa yana jan earpiece dinsa ya cusa a kunnensa dan ya daina jin muryarta ko ya samu sassauci kan yadda tsigar jikinsa ke tashi.
Har suka isa airphort basu gama wayar ba,saida motar ta tsaya sannan sukai sallama da aliys kan zata kirata.
A tsorace take taka matattakalar jirgin,karo na farko a rayuwarta data tana shigowa airphort ma baki daya balle ta doshi jirgi,yana daga gefanta ya lura da tsoron dake tattare da ita,a hankali ya matsa gefanta ya zura hannunshi daga gefan kafadarta ya jinginata da tashi kafadar,juyowa tayi suka hada idanu,saiya mata nuni da qwayar idanunshi da wasu ma'aurata dake gabansu hannunsu cikin na juna,sai ta sako ajiyar zuciya tana shaqar qamshin turarensa da har yau ta rasa wanne iri ne,haka koda wasa bata taba jin mai irin qamshin ba.
Sosai ya matse hannunsa cikin nata sanda jirgin ke shirin tashi,ruf ta rufe idanunta tana karanto addu'ar hawa abin hawa,wanda hakan ya qara mata nutsuwa,saida komai ya daidaita sannan ta sauke numfashi ta bude idanunta a hankali sai cikin na khalipha,girarshi ya daga mata alamar tambaya,saita girgiza kai tana sake maida idanunta ta lumshe.
Qarfe sha daya na safe suka sauka a legos abinka da tafiyar jirgi,wasu motoci ne guda hudu iri daya sak masu dauke da wani tambari da bata lura dana meye ba suke tsaye suna jiran isowarsu,daya daga cikin motocin aka budewa khalipha ya shiga aysha tabi bayansa,daga bisani motar ta gyara tsaiwa ta fice daga airphort din sauran na biye da su,dukka hankalinta nakan titunan da suke wucewa,karon farko data taba barin jihar kano zuwa wata jaha ta daban wadda bata taba zuwa ba,saidai taji sunanta kawai a baki,sosai garin ya burgeta,yanayin weather dinsu irin wadda takesoce,don a sannan suna samun saukar ruwan sama,duk da bai kankama ba amma hakan ya sake qawata yanayin garin da iska mai dadi da sanyi.
Joygate hotel and suites suka sauka wanda ke lateef salami street don yafi kusa da airphort,a harabar hotel din duka sauran suka dakata shi da ita ne kawai suka shiga ciki,executive suite yayi booking dama tun daga gida,shi ya bude qofar yana kan gaba tana binsa a baya har cikin dakin,cikin yan mintina qalilan aka shigo da abinci da sauran abinda mutum zai buqata
"Ki huta nan da two to three hours zan dawo ki shirya kafin nan zamu fita"
"Ohk" ta fada tana gyada kai
"Akwai damuwa?" Ya tambayeta manyan idanunshi a kanta,kai ta kada alamun a'ah sai ya juya ya fice yana ja mata qofar idanunshi a kanta.
Dakin tabi da kallo yayi mata kyau sosai kaman ba cikin hotel ba,gefan gadon ta samu ta zauna tana tunanin me sukazoyi lagos?,har yau bata san dalilin tafiyar tasu ba
Wayarta ta ciro ta kira anni ta sanar mata sun iso,sannan ta duba taga da saura kafin lokacin sallar azahar ya shiga,sai kawai ta kunna tv din dake dakin ta sauya tasha zuwa arewa.
Qarfe daya da rabi na rana tayi sallah,sannan ta bude abincin da aka kawo mata taci,sai daya dan fada mata sannan ta shiga bandakin dakin ta sake wanka ta fito ta shirya cikin wani material mai azabar kyau da tsada mint green cotton ne amma mai dan qarfi,ta nannade gashinta tayi daurin nan da ake a gaban goshi wanda gashinta data yiwa parking ta kama jelarsa ta kitsa ya zama jela daya ya fito ta qasan daurin,sarqa da dan kunne da kuma abin hannun da tayi amfani dasu duka set ne sirara masu ruwan gold,ba qaramin kyau tayi ba fuskarta tayi fresh sosai,gogewar da fatarta ta sakeyi ita kanta yana mata kyau,dai data tsaya gaban mudubi ta tabbatar komai yayi sannan ta koma saman kujerar.
Tana shirin xama akayi knocking qofar,saita fasa zaman ta isa bakin qofar ta murda muqullin ta bude gami da ja baya,khalipha ne ya shigo hannunshi riqe da top din suit dinshi daya hannun kuwa wayoyinsa ne,kana kallonshi ko ba'a gaya maka ba kasan a gajiye yake,da kallo ya bita cikin nutsuwa yake qarewa adonta kallonta,ba qaramin burgeshi adon nata yayi ba,sai yaga kaman canza ta akayi daga fitarsa zuwa dawowarsa,yana son qaryata hakan amma zuciyarsa taqi karba
"Sannu da zuwa" ta fada cikin sanyinta tana mamakin yadda yau ya ware ido yake kallonta kai tsaye
"Yauwa" ya fada yana zama saman kujea gami da cire takalmi da safar qafarshi,tana daga gefe tana wasa da yatsunta saboda yadda kallonshi ya mata nauyi yayin da shi kuma yake ci gaba da satar kallonta,shuru ya ratsa dakin,sai daya rage kayan jikinsa sannan ya tambayeta me suka kawo mata,tashi tayi ta dauko masa ta bude mishi
"Zubamin" yw fada yana kallon lallenta da kamar kullum turashi ake,nan tayi serving dinsa yaci sannan shima ya shiga wanka.
Tana tsaka da kallon maimacin wani indian hausa a tauraruwa t.v ya bude qofar bandakin ya fito lullube da towel a jikinsa,ya daura wani duk da mai yalwa ne amma duka singalalin qafarsa a waje yake,dauke kanta tayi da sauri tana jin wani feeling cikin ranta,ya jima kafin daga bisani qamshin turarensa ya game dakin,wanda ya haifar mata da kasala,ta lumshe idanuwanta tana jin motsinsa cikin dakin,bata bude ba har sai data tabbatar daya gama shiryawa
"Mu wuce ko?" Ya fada yana sanya takalma a qafarsa sabanin wadanda ya cire daxun,sai a sannan ta bude idanunta,yayi kyau cikin dinkin kufta,batasan me yasa idan ya saka manyan kaya ba saiya koma mata kamar wani saraki,cikin mutuwar jiki da kasala ta miqe ta soma nannadawa jikinta laffaya,ta cikin mirrow yake kallonta,duk wani motsi idan tayi shape dinta ne ke fita,irin shape da daidaikun mata Allah ya yiwa baiwa dashi,ajiyar zuciya ya kuma saki can qasa,baisan me yake damunshi ba sam,baisan me yasa baya iya controlling idanunshi ba a kanta
Tare suka jero har zuwa bakin motocin dake fake a wajen,ga mamakinta da kanshi ya bude mata gidan gaba,saita daga kai ta kalleshi suka hada ido,kafeta da ido yayi yana mata nuni da hannunshi kan ta shiga,a hankali ta zura jikinta kafin ya sanya qafafunta ya maida murfin motar ya rufe sannan ya zagaya,sai taga ya shiga sashen driver ga mamakinta ya sanya muqulli ya tada motar da alama da kanshi zaiyu driving,dubanshi take da mamaki saiya waiwayo caraf suka hada ido,girarshi ya dage mata
"Me naci ban baki ba?,karki cinyeni mana wannan kallo haka tun daxun?" Kunya taji saita kauda kai tans yunqurin danne murmushin daya subuce mata,cikin salon kare kai tace
"Da wanne idon kasan ina kallonka,ni me zan kalla" yanq tada motar ya bata amsa
"Abubuwa da yawa mana"
"Kamar?" Ta tambayeshi tana murmushi fuskarta na kallon window din motar ta yadda bazai iya ganin fsukarta ba
"Idan kin isa juyo ki kalleni saina baki amsa" tilas murmushin dake kan fuskarta ya subuce saidai bata yarda sautinsa ya fita ba
"Kidai rage kallona karki je ki soma sona,bayan ni kuma na riga dana siyar" dan dakewa tayi jin abinda yace,saboda ita batayi qorafin yawan kallonta da yakeyi ba shine shi xaiyi mata qorafi,shuru ne yaci gaba da ratsawa a motar,baka jin komai sai tashin qarar ac,da kuma anguwanni da suketa wucewa.