Sashe 62
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tana tsaka da wannan bacin ran taji knocking,kafin ta bada izini an turo an shigo,yayyen hamid ne guda biyu da qannenshi su uku duka mata,da yake su biyu ne maza a gidansu shi da qaninsa,hakanan ta aro fara'a ta dorawa fuskarta,kana gani tasan bata saba hakan ba,haka yake don bata da experience na yadda ake taryar baqo,kujerun suka samu suka zazzauna suna bubbuda hanci da qarewa gidan kallo fes,aka rasa wanda zai fara gaida wani,su suna ji da girman kai,yayin da ita kuma batasan ya akewa baqin ba idan sunzo,don a gida abinda ta sani shine ta qwalawa mai aiki ko aysha kira ta kawo lemo da ruwa wani lokaci da abinci,to yau mai aikin nata tunda ta tafi gidan qanwar babanta bata dawo ba tun safe,kusan tare suka fita da hamid,ita kuma ta qyuyar tashi,koda ta tashin ma basu da wani abun azo a gani,ruwanta ne data siya cartoon uku takesha ba kuma zata iya basu ba,sai lemon da hamid ya shigo dasu jiya qwaya uku yace mata kuma nashi ne kar a taba masa,tanajin girman kan ta taba masan don karya rainata shi yasa ko kallonsa batayi ba
"wacce iriyar mace hamid ya aura ne wadda bata iya gaida mutane ba?" Babbar yayarsu ta fada tana yatsina baki,kallonta asma'u tayi,sai a sannan ta ganeta cewa itace babba a gidan,dole yasa tace mata ina yini.ita kadai ta amsa da qyar aka ci gaba da kallon kallo da zaman kurame,kowa da abinda yakeji dashi cikin ransa,qaramar qanwarsu ce kuma autarsu wadda a qalla ta kusa shekara sha biyar ta saka kuka tana cewa
"Tun a hanya nakejin qishirwa maman salima kika ce na bari mu iso,gashi mun iso din kuma banga alamun ruwa ba"
"Ki bamu ruwa tunda saimun roqa" wadda daga ita sai autar tasu ta fada,miqewa autar tasu tayi tana cewa
"Ta barshi idan ma bazata bani ba ai nasan kitchen din,tunda gidan yayana ne" ta fada tana nufar kitchen din asma'u,take zuciya ta ciyo asma'un,ta miqe da hanzari ta janyo ta tana cewa
"Bana daukar raini ko rashin kunya,karki kuskura ki shigarmin kitchen nada izinina ba,idan kina taqamar gidan wanki ne me ya ajiye a gidan?,wani abun arziqi yake bani?" Salati babbar yayar tasu ta saka,sanda auta ramla ta saki kuka
"Lallai hajiya tazo ta ganema idonta 'yar gudan butulu,tun daga aurenki har kawoki gidan nan kike laqwame dukiyar dako mahaifiyar data haifeshi bata ci ba,shine yanzu zaki bishi da sharrin bai aje miki komai?,ku tashi mu tafi maza kafin muma ta jefe mu da wani sharrin" tana nan tsaye har suka gana ficewa daga falon,ta bisu ta bame qofarta ta tsaya tana maida numfashi gami da tambayar kanta meye haka ne?,sai ta dafe kanta tana son ta gane me hakan yake nufi?,wai dama haka rayuwar auren take ne wai?,wannan shine jin dadin da hamid ya dade yana mata dadin bakin yayi mata tanadinshi?,kuka ta saki ta sake daukar wayarta tana neman layin mummy,saidai cikin rashin sa'a a kashe wayar take,haka ta zauna taci kukanta daga bisani ta haura sama tayi wanka saboda gumi data yi,sakamakon yanayin zafi da aka shiga,don gidan babu wuta,hakanan engine dinsa baya kunnawa sai ya dawo gida,shima na iya mintinan da zai zauna a falo ne,daya tashi yin bacci zai kashe yayi kwanciyarsa,a sanda suke zuwa ganin gini ya nuna mata kayan hada solar inverter,amma daga baya bayan sun tare suna tsaka da amarci ya kwashe ya saida yace babbar wannan zai saka,gashi yanzu a qalla watanni uku ba ita ba dalilinta,babu ma wannan maganar,mutumin da duk wani alatun rayuwa ya janye shi daga gidan sai abinda ba'a rasa ba wanda bazai iya rayuwa babu shi ba.
Falon qasan ta sake dawowa bayan ta gama wankan ta zauna tana sauke ajiyar zuciya,yunwa take ji ta kasa cin komai,Allah ya taimaketa aka kawo nepa,a nan ta kwanta sosai iskar A.c na kadata tana jin dadin iskar duk da zuciyarta a cunkushe take,tana ta son ta lalubo dalilin sauyawar hamid amma ta rasa,tana son tasan shin dama tun ainihinsa haka yake ko kuwa sauyawa yayi.
Kana kallonshi kasan a fusace ya shigo falon yana wani daddaurewa yana cin magani,a baya farkon fara hakan sanda bata saba ba duk sanda ya shigo din takan aje girman kanta ta bishi ta rissina masa tana neman jin ba'asi da lallashi yana fuffurjewa,daga bisani itama ta watsar ta nuna masa sam itafa ba haka aka raineta ba,batasa daukar wulaqanci ba,ba'a sakata saidai ita ta saka,idan ta nema dole ta samu,yadda ta tsara ahaka ake aiwatarwa,abinda shi kuma yake kallonshi a amatsayin shi da babu duk daya.
Har ya wuce ya soma taka matattakala ya dawo da baya yana dubanta
"Na lura iskancinki da rashin mutuncinki qara gaba yake,takai ma ban isa kimin sannu da zuwa ba ko?" Banza tayi da shi kamar bata ji me yace ba,saima gyara kwanciyarta da tayi,kai ya kada ya haye saman,ta bishi da kallon banza taja tsaki,gaba daya auren dashi hamid din kansa ya fice mata a rai,minti arba'in ya sake saukowa ya sauya kaya da alama wanka yayi,duk sanda ya dawo haka yakeyi,daga yaci ya qoshi zai sake fita ba zata kuna ganinsa ba sai sha daya da rabi ko sha biyu na dare
"Ina wainar fulawar da malam zailani ya kawo miki?"
"Tana shara" ta bashi amsa cikin gadara,sosai yaji wani bacin rai ya kamashi,shi zata yiwa almubazzaranci bayan kudi ya saka ya siya mata
"Ina abinci na?" Sai a sannan ta dubeshi
"Mai dafawar ai kafi kowa sanin bata nan,tunda kai ta tambaya sanda zata fice yawonta"
"Saitana nan zanci abinci a gidan nan?"miqewa tayi ta zauna sosai don dama qule take da shi,ta dubeshi sosai
"Eh mana,meye amfaninta?"
"Ke nake aura ko ita?,baiwar uwarki ce ita da kullum ita zata dinga dafa muku abinci" sosai lafazin nashi ya bata mamaki,yau ita hamid ya zaga kanshi tsaye ba wani damuwa kamar ya zagi banza
"Baiwar uwata?,idan ita din ba baiwar uwata bace ni baiwar uwarka ce?,ko yarjejeniyar da mukayi kenan da kai kafin aurenmu?,ka wargaza komai ka saba duk wani al....." Bata samu damar qarasawa ba ya kasheta da mari sannan ya nunata da yatsa
"Kin tabbata cikakkiyar mara tarbiyya wadda ba'a koya mata tarbiyya ba daga gidansu,uwata zaki zaga?,tun kafin ma dawo gidan nan labarin wulaqanta min 'yan uwa da kikayi ya iskeni,da mike zancan na karya duk alqawarin da nayi an gaya miki bansan don me mike sona ba?,bansan samari nawa kikayi ba kafin ni duk kika qisu saboda kina tunanin na fisu arziqi?,dama an gaya min din me kike sona yanzu gashi kuwa ya tabbata,wannan aishan da kike qi kike gayamin maganganu kullum a kanta din na tsaneta tota fiki,na tabbatar da ita na aura bani da matsalar komai kome zan ciyar da ita kowanne umarni zan bata,saboda haka ta fiki wawiyar mace wadda bata iya komai ba,kuma duk kudin dana kashe miki da asarar da siyayya masu tsada da kika dinga roqa ina miki duk sai na fanshe abuna,an gaya miki ni sakarai ne bansan ciwon nema ba?,to idan baki sani ba bari in gaya miki yau free,ba'a cin kudina haka siddan koda kai ka kawoni duniyar,bare ke da mika tsinceni da haqorana talatin da hudu cif" hannu ya zura cikin aljihunsa ya fito da envalope ya farkesu,kudi ne suka zubo daga ciki,ya qirgasu ya zari wani abu daga ciki ya watsa mata sauran
"Gashinan inji tsohonki,mun hadu a banki naje kai kudi shima tasa ta kaishi,na cire kudin wainata da kikamin asara,canjin zanje naci abincin da baki girka ba" ya fada yana maida uban kudin daya zara da sunan kudin wainar fulawa,sannan ya isa gaban dustbin din data ce ta jefa wainar ya zura hannu ya laluba ya cirota a keda ya fice ya jefawa karnukansa,ba bata lokaci suka hau ci don ya koya musu cin komai,babu abinda basa ci.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Cikin qanqanin lokaci komai da komai ya kammala na karatunta,sunanta na gaba gaba cikin jerin sunayen daliban da suka samu admission,kusan tana zaune akayi mata komai,zirga zirgar da tayi bata kai ta kawo ba abinka da wadanda keda masu gidan rana,ta riga data zabi zaman hostel,ba don komai ba donta samu yin karatu sosai yadda ya kamata,sannan tanason hankalinta ya ttara waje guda,saidai kuma zata dinga zuwa gida duk weekend.
Sam anni bataso haka ba,don zuwa yanzun ayshan kusan itace mai kula da komai na annin,hatta da kayan sawarta,kitsonta abincinta da sauransu,uwa uba sabo daya shiga tsakaninsu,tana matuqar jin dadin zama da ita,duk yadda take hasashen ayshan saita karanci ta wuce nan,wata baiwa Allah yayi mata ta daban wadda ko ita ba lallai tasan da ita,saidai annin bata nuna rashin jin dadin nata ba don kada ta rage mata qwarin gwiwa ko taji babu dadi,don ta fuskanci sosai takeson karatunta,gefe guda kuma amal na dan tabukawa kada ta fuskanci ta raina qoqarinta ne itama.
Ranar da komai ya kammala ya sameta a falon anni,ta riga data saba bacci ne kawai ke maidata nasu sashen,tana zaune saman kujera annin na qasa tana lallabe mata kanta,zanen hausa take mata guda shida duk bayan kwana goma,da yake annin akwai gashi tubarkalla kasancewarta buzuwar bafulatana har bayanta jelar ke fitowa.
"wacce iriyar mace hamid ya aura ne wadda bata iya gaida mutane ba?" Babbar yayarsu ta fada tana yatsina baki,kallonta asma'u tayi,sai a sannan ta ganeta cewa itace babba a gidan,dole yasa tace mata ina yini.ita kadai ta amsa da qyar aka ci gaba da kallon kallo da zaman kurame,kowa da abinda yakeji dashi cikin ransa,qaramar qanwarsu ce kuma autarsu wadda a qalla ta kusa shekara sha biyar ta saka kuka tana cewa
"Tun a hanya nakejin qishirwa maman salima kika ce na bari mu iso,gashi mun iso din kuma banga alamun ruwa ba"
"Ki bamu ruwa tunda saimun roqa" wadda daga ita sai autar tasu ta fada,miqewa autar tasu tayi tana cewa
"Ta barshi idan ma bazata bani ba ai nasan kitchen din,tunda gidan yayana ne" ta fada tana nufar kitchen din asma'u,take zuciya ta ciyo asma'un,ta miqe da hanzari ta janyo ta tana cewa
"Bana daukar raini ko rashin kunya,karki kuskura ki shigarmin kitchen nada izinina ba,idan kina taqamar gidan wanki ne me ya ajiye a gidan?,wani abun arziqi yake bani?" Salati babbar yayar tasu ta saka,sanda auta ramla ta saki kuka
"Lallai hajiya tazo ta ganema idonta 'yar gudan butulu,tun daga aurenki har kawoki gidan nan kike laqwame dukiyar dako mahaifiyar data haifeshi bata ci ba,shine yanzu zaki bishi da sharrin bai aje miki komai?,ku tashi mu tafi maza kafin muma ta jefe mu da wani sharrin" tana nan tsaye har suka gana ficewa daga falon,ta bisu ta bame qofarta ta tsaya tana maida numfashi gami da tambayar kanta meye haka ne?,sai ta dafe kanta tana son ta gane me hakan yake nufi?,wai dama haka rayuwar auren take ne wai?,wannan shine jin dadin da hamid ya dade yana mata dadin bakin yayi mata tanadinshi?,kuka ta saki ta sake daukar wayarta tana neman layin mummy,saidai cikin rashin sa'a a kashe wayar take,haka ta zauna taci kukanta daga bisani ta haura sama tayi wanka saboda gumi data yi,sakamakon yanayin zafi da aka shiga,don gidan babu wuta,hakanan engine dinsa baya kunnawa sai ya dawo gida,shima na iya mintinan da zai zauna a falo ne,daya tashi yin bacci zai kashe yayi kwanciyarsa,a sanda suke zuwa ganin gini ya nuna mata kayan hada solar inverter,amma daga baya bayan sun tare suna tsaka da amarci ya kwashe ya saida yace babbar wannan zai saka,gashi yanzu a qalla watanni uku ba ita ba dalilinta,babu ma wannan maganar,mutumin da duk wani alatun rayuwa ya janye shi daga gidan sai abinda ba'a rasa ba wanda bazai iya rayuwa babu shi ba.
Falon qasan ta sake dawowa bayan ta gama wankan ta zauna tana sauke ajiyar zuciya,yunwa take ji ta kasa cin komai,Allah ya taimaketa aka kawo nepa,a nan ta kwanta sosai iskar A.c na kadata tana jin dadin iskar duk da zuciyarta a cunkushe take,tana ta son ta lalubo dalilin sauyawar hamid amma ta rasa,tana son tasan shin dama tun ainihinsa haka yake ko kuwa sauyawa yayi.
Kana kallonshi kasan a fusace ya shigo falon yana wani daddaurewa yana cin magani,a baya farkon fara hakan sanda bata saba ba duk sanda ya shigo din takan aje girman kanta ta bishi ta rissina masa tana neman jin ba'asi da lallashi yana fuffurjewa,daga bisani itama ta watsar ta nuna masa sam itafa ba haka aka raineta ba,batasa daukar wulaqanci ba,ba'a sakata saidai ita ta saka,idan ta nema dole ta samu,yadda ta tsara ahaka ake aiwatarwa,abinda shi kuma yake kallonshi a amatsayin shi da babu duk daya.
Har ya wuce ya soma taka matattakala ya dawo da baya yana dubanta
"Na lura iskancinki da rashin mutuncinki qara gaba yake,takai ma ban isa kimin sannu da zuwa ba ko?" Banza tayi da shi kamar bata ji me yace ba,saima gyara kwanciyarta da tayi,kai ya kada ya haye saman,ta bishi da kallon banza taja tsaki,gaba daya auren dashi hamid din kansa ya fice mata a rai,minti arba'in ya sake saukowa ya sauya kaya da alama wanka yayi,duk sanda ya dawo haka yakeyi,daga yaci ya qoshi zai sake fita ba zata kuna ganinsa ba sai sha daya da rabi ko sha biyu na dare
"Ina wainar fulawar da malam zailani ya kawo miki?"
"Tana shara" ta bashi amsa cikin gadara,sosai yaji wani bacin rai ya kamashi,shi zata yiwa almubazzaranci bayan kudi ya saka ya siya mata
"Ina abinci na?" Sai a sannan ta dubeshi
"Mai dafawar ai kafi kowa sanin bata nan,tunda kai ta tambaya sanda zata fice yawonta"
"Saitana nan zanci abinci a gidan nan?"miqewa tayi ta zauna sosai don dama qule take da shi,ta dubeshi sosai
"Eh mana,meye amfaninta?"
"Ke nake aura ko ita?,baiwar uwarki ce ita da kullum ita zata dinga dafa muku abinci" sosai lafazin nashi ya bata mamaki,yau ita hamid ya zaga kanshi tsaye ba wani damuwa kamar ya zagi banza
"Baiwar uwata?,idan ita din ba baiwar uwata bace ni baiwar uwarka ce?,ko yarjejeniyar da mukayi kenan da kai kafin aurenmu?,ka wargaza komai ka saba duk wani al....." Bata samu damar qarasawa ba ya kasheta da mari sannan ya nunata da yatsa
"Kin tabbata cikakkiyar mara tarbiyya wadda ba'a koya mata tarbiyya ba daga gidansu,uwata zaki zaga?,tun kafin ma dawo gidan nan labarin wulaqanta min 'yan uwa da kikayi ya iskeni,da mike zancan na karya duk alqawarin da nayi an gaya miki bansan don me mike sona ba?,bansan samari nawa kikayi ba kafin ni duk kika qisu saboda kina tunanin na fisu arziqi?,dama an gaya min din me kike sona yanzu gashi kuwa ya tabbata,wannan aishan da kike qi kike gayamin maganganu kullum a kanta din na tsaneta tota fiki,na tabbatar da ita na aura bani da matsalar komai kome zan ciyar da ita kowanne umarni zan bata,saboda haka ta fiki wawiyar mace wadda bata iya komai ba,kuma duk kudin dana kashe miki da asarar da siyayya masu tsada da kika dinga roqa ina miki duk sai na fanshe abuna,an gaya miki ni sakarai ne bansan ciwon nema ba?,to idan baki sani ba bari in gaya miki yau free,ba'a cin kudina haka siddan koda kai ka kawoni duniyar,bare ke da mika tsinceni da haqorana talatin da hudu cif" hannu ya zura cikin aljihunsa ya fito da envalope ya farkesu,kudi ne suka zubo daga ciki,ya qirgasu ya zari wani abu daga ciki ya watsa mata sauran
"Gashinan inji tsohonki,mun hadu a banki naje kai kudi shima tasa ta kaishi,na cire kudin wainata da kikamin asara,canjin zanje naci abincin da baki girka ba" ya fada yana maida uban kudin daya zara da sunan kudin wainar fulawa,sannan ya isa gaban dustbin din data ce ta jefa wainar ya zura hannu ya laluba ya cirota a keda ya fice ya jefawa karnukansa,ba bata lokaci suka hau ci don ya koya musu cin komai,babu abinda basa ci.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Cikin qanqanin lokaci komai da komai ya kammala na karatunta,sunanta na gaba gaba cikin jerin sunayen daliban da suka samu admission,kusan tana zaune akayi mata komai,zirga zirgar da tayi bata kai ta kawo ba abinka da wadanda keda masu gidan rana,ta riga data zabi zaman hostel,ba don komai ba donta samu yin karatu sosai yadda ya kamata,sannan tanason hankalinta ya ttara waje guda,saidai kuma zata dinga zuwa gida duk weekend.
Sam anni bataso haka ba,don zuwa yanzun ayshan kusan itace mai kula da komai na annin,hatta da kayan sawarta,kitsonta abincinta da sauransu,uwa uba sabo daya shiga tsakaninsu,tana matuqar jin dadin zama da ita,duk yadda take hasashen ayshan saita karanci ta wuce nan,wata baiwa Allah yayi mata ta daban wadda ko ita ba lallai tasan da ita,saidai annin bata nuna rashin jin dadin nata ba don kada ta rage mata qwarin gwiwa ko taji babu dadi,don ta fuskanci sosai takeson karatunta,gefe guda kuma amal na dan tabukawa kada ta fuskanci ta raina qoqarinta ne itama.
Ranar da komai ya kammala ya sameta a falon anni,ta riga data saba bacci ne kawai ke maidata nasu sashen,tana zaune saman kujera annin na qasa tana lallabe mata kanta,zanen hausa take mata guda shida duk bayan kwana goma,da yake annin akwai gashi tubarkalla kasancewarta buzuwar bafulatana har bayanta jelar ke fitowa.