← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 114

Sashe 78

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Aminity aka basu bayan 'yan gwaje gwaje da likitan ya sanya aka yi mata aka sanya mata qarin ruwa sannan ya buqaci ganin khalipha,cikin murmushi likitan ya yiwa khalipha barka da zuwa sannan sukayi musabaha da juna
"Madam na cikin damuwa qwarai,gaskiya tana buqatar kulawa,tana buqatar abinda zai kwantar mata da hankali ya debe mata kewa....yanzu zamu dan riqeta haka zuwa ko nan da gobe ne idan muka ga yanayin jikin nata zaku iya tafiyama a yau"jinjina kai khalipha yayi sannan ya yiwa likitan godiya ya fita daga office din.

A hankali ya tura qofar dakin idanunsa akanta da take kwance saman gadon barin hannun damanta wanda hakan shi yasa fuskarta ke fuskantar bakin qofa,bacci take sosai wanda hakan baya rasa nasaba da ruwa da alluran dake cikin ruwan dake shiga jikinta,kanta babu mayafi sai dankwalin dake daure a kanta wanda shima ya zame ya bayyanar da rabin gashin kanta,har ya qaraso wajen batasan me ake ba,kujera yaja gaban gadon saitin kanta ya zauna.

Tayi wani fayau tayi kyau,haskenta ya sake fitowa sakamakon kukan data sha daya sanya fuskarta ta sake yin jaa,dan qaramin bakinta na tsuke hakanan girarta a tattare take alamun ba dadin baccin take ji ba,tausayinta ne ya dinga ratsashi,ya shiga tunani kan maganganun da likita ya gaya mishi,ta jima a rayuwarta cikin damuwa dole hakan yayi affecting lafiyarta,ya dade zaune gabanta yana tunanin abubuwan daya dace yayi,har sai da lokacin sallar la'asar yayi sannan ya daura alwala ya fita can masallacin daya gani gefan asibitin don bada farali.

Har ya dawo baccin take,sai ya sake komawa gurbin daya tashi ya zauna,yanayin kwanciyarta yaga ya sauya cikin dabara ya gyara mata gami da lullubeta zuwa qugunta,kallonta yaci gaba dayi tausayinta na ratsashi,a hankali ya laluba hannunta dayan wanda ba qarin ruwa ya sanya tafin hannunshi cikin nata,tasowarta tun daga quruciya,irin gwagwarmayar data fuskanta cikin rayuwata har zuwa yau,wani rauni zuciyarshi keson yi,dauko tashi rayuwar a baya yayi ya soma hadata data aysha,sai yaga ta wani fanni rayuwarsu na kamanceceniya,yanayin gwagwarmayar da fadi tashi,qalubale mai tarin yawa,a hankali zucuyarsa yaji tana gaya masa cikin nutsuwa da yanayi mai ratsa jiki,wataqila rayuwarsu tayi kamanceceniya ne saboda sun dace da juna,wataqila Allah ya shigo da kowa cikin rayuwar d'ayanshi saboda dacewar hakan,ba shakka babu wani abu yanzu dazai goge mata dukka wani tabo na rayuwarta idan ba soyayya ba,saidai ta yaya zai sanyata ta soshi?tana buqatar soyayya lallai ba shakka Allah ya aikosu ne cikin rayuwar junansu saboda kowanne nada buqatar dan uwanshi,cikin zaren tunaninsa har baisan sanda ya matse hannunta cikin nashi ba
"Ayshaaahh" ya furta cikin wani irin sanyi.

Tamkar cikin mafarki taji muryar na kiranta,muryar da bazaiyuwu ta mance da itaba tsahon rayuwarta,sai taji kamar umarni yake mata ta bude idonta,a hankali cikin bacci take bude idanun nata,fuskarshi ta soma gani zaune dirshan a gabanta,saita soma zaton cikin mafarki ne,saboda haka ta bude bakinta daya mata nauyi
"Ya khalipha taqi saurarona,taqi ta kalleni,bata sona,ummi bata sona waye zai soni?" Matsowa da fuskarshi yayi gab da tata har suna musayar numfashi,cikin muryar da babu maijin amonta koda mutum na cikin dakin yace da ita
"Ni muhammad khalipha,ni zan soki aysha idan kin yarda" shuru tayi tana tunanin idanu biyu ne ko a farke,yanayin yadda numfashinsa mai cakude da qamshin turarensa ke bugun fuskarta yasa ta tabbatar a farke take,nauyin maganarsa yasa ta lumshe ido kaman wadda ta koma.bacci,saidai ba haka bane,abu biyu ke mata kara kaina,lafuxansa da haduwarta da ummi yau wanda lamarin kecin jiki da zuciyarta,ci gaba yayi da duban fuskarta dayau tayi masa kyau muraran fiye da kowanne lokaci,ya gane ba bacci ta koma ba amma ba aqalla yana jin bari ya bata space sai yaja da baya ya jingina jikinsa da kujerar da yake kai.

Batasan awa nawa ta kwashe a haka ba,itadai taji shigowar likita,bata ankara ba ta ji hannunshi saman kanta yana kiran sunanta,idanunta ta runtse gam,saiya duqa saitin kunnenta
"Taimaka ki tashi likita ya shigo" hannunta ya kama ba yadda ta iya ta miqe ta zauna sosai da taimakonsa,saiyaqi matsawa saidaya gyara mata dankwalinta ya lullubata shi kaman mayafi.

'Yan tambayoyi likitan yayi mata ya sake gwada ta sannan ya dubi khalipha,cikin harshen yarbanci sukai magana wanda bata ji komai suke cewa ba,daga bisani likitan ya juya ya fita,kujerar tasa ya sake komawa ya matso da ita dab da aysha har qafarshi na gogar tata,yayi qoqarin su hada idanu amma taqi yarda da hakan,baisan me yasa take da matsananciyar kunya irin haka ba
"Yanzu me zakici?" Kai ta kada
"Babu komai"
"Bazaiyiwu ba" ya fada yana danna wayarshi,kira yayi na mintina sannan ya kashe
"Humaira" ya kira sunanta a tausashe,
"Humaira" ya sake kiran sunan nata duka tana jinsa,kasa dagowa tayi ta dubeshi sai amsawa da tayi kawai
"Dubana nakeso kiyi" shi baisan me kusancinsu haka ke haifar mata ba,baisan me take ji idan ya kira sunanta ba,yana shirin sake cewa wani abu akayi knocking qofar ya tashi ya bude ya amshi saqon ya dawo ya zauna inda ya tashi.

Saman cinyarta ya aje ledar da aka kawo,ya fidda duk abinda ke ciki ya shirya sannan yace mata bayan ya debo abincin cikin cokali
"Uhmm,bismilah"
"Na....."
"Shhhhshh...." Ya fada yana dora yatsanshi akan lebansa
"Banason kice komai just open ur mouth" hakanan ta bude bakinta ya dunga bata abincin a hankali har suka kammala,shi ya taimaka mata tayi alwala tayi sallah sannan yace mata
"Zamu iya komawa gida?" Kai ta gyada don itadinma bason zaman asibitin take ba,cikin mintuna qalilan drivern ya iso,tana rungume jikinshi har suka isa hotel din da suka sauka.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Shuru falon saika dauka babu kowa a ciki,dukka yaran baki dayansu jikinsu a sanyaye suke,abincin da suka saba zama suci tare koda yaushe yau ba wanda yaci na kirki,hasalima basma da mai bi mata yusrah har yanzu suna zaune wajen amma babu wanda yaci abincin a cikinsu,tunda take dasu irin hakan bata taba faruwa tsakaninsu ba,tasan kuma bai rasa nasaba da ganin basma ba cikinbwalwala ba ya shafi duka sauran,saboda suna da hadin kai tsakaninsu yaran gaba daya,sharesu tayi itama tanata qoqarin ganin tayi al'amuranta kamar yadda ta saba,saidai kuma hakan taci tura,don itama juya abincin kawai take ba tare data ci komai ba,shurun ne ya isheta sai ta daga kai cikin hade fuska
"Kai abba,hadim ku dauki abincinku kuci"kai suka girgixa a tare
"mun qoshi ummi"
"Ku dauki abincinku kuci nace!" Ta sake maimaita musu cikin tsawa da qaraji,wanda ya sanya babu shiri suka ja kwanon abincin gabansu suka soma kaiwa baki kamar basaso
"Yusra basma,zoki zuba abinci kuci" ta fada tana tsareta da ido,Dole yusra taja itama plate din ta soma ci kamar dole,yayin da basma ta tashi daga falon da gudu ta shige daki tana sakin kuka,ta jima tana tausayin anty indo,tun batasan ciwon kanta ba har zuwa yanzu,da kallo ummi ta bita,cikin zuciyarta takewa inna yelwa Allah ya isa,har zuwa yanzu bata daina ganin illar matar da sharrinta ba har ya zuwa yanzu?,saita danne abinda ke taso mata ta zubawa yarn ido dake cin abinci kamar dole,a haka babansu yayi sallama,dukkaninsu suka miqe suka taryeshi,saidai ba yadda suka saba ba,tunda yaga hakan yasan lallai akwai abinda ya faru,ko kuma ta tuna da ayshan ne kamar yadda aka saba,zama yayi saman kujera bayan yaran sun koma sun zauna ya tambaya yana dubam fuskarsu daya bayan daya
"Me ya faru?" Sai suka soma kallon kallo aka rasa mai bada amsa,yusrah ce tayi qarfin halin cewa
"Anty indo ce tazo gidan nan dazu ita da mijinta" zumbur ummi ta miqe tabar falon,saiya bita da kallo har ta shige dakinsu,sake duban yarab yayi yana sake tambayarsu,yusrah ta kwashe komai ta gaya masa,ya jima yana nazari kafin daga bisani yace
"Shikenan kuci abincinku,kar wanda yasa damuwa a ranshi,zanje naga umminku" ya fadi yana miqewa suka amsa da to abba gaba dayansu.

*************************

Zaune take saman kujerar dake cikin dakin hotel din wadda ke daura da gadon baccinsu,tana sanye cikin kayan bacci masu kyau da kauri kanta yana da mayafi,tana nade saman kujerar idanunka kan t.v da suke hasko wani wasa,saidai kusan fiye da rabin hankalinta ya karkata ne kan tunanin abinda ya faru da ita dazun da safe tsakanina da umminta,shawarar da basma ta bata tana mata yawo cikin qwaqwalwarta,khalipha ne yayi clapping hannunshi gaban fuskarta wanda ya dawo da ita daga tunanin data tafi,yana tsaye a kanta yana dubanta
"Kin saba alqawarinmu,kin manta?" Dan siririn murmushi ya subuce daga lebanta,sam ta mance da maganar daya gaya mata kafin ya shiga wanka,saita maxe kawai,yanayin yadda ta basar din saiya burgeshi,ta tsuke dan bakinta waje guda ba tare data sani bama,agogo ya kalla yaci ace sun kwanta bacci saboda haka ya qarasa ya kashe kayan kallon yana fadin
"Time for sleep" maimakon ta tashi ta hau gado saita gyara zamanta a saman kujerar alamar anan take shirin kwana,dubarta yayi sai baice komai ba yaci gaba da shirin kwanciya barci,sai daya kammala komai zuwa sannan tana zaune idanunta nakan system dinshi daya kunne ya aje a wajen zaiyi aiki,tanata nuno hotunan dake cikinta daya bayan daya,takawa yayi ya kashe qwan dakin ya kunna mara haske,a nutse ya qarasa gaban kujerar ya zauna gab da ita har kafadunsu na gogar juna,ta jishi sarai amma sai taqi nuna hakan,tadanja wani littafi dake gefan system din din bataso ya fuskanci kamar tunani taci gaba dayi,system din yaja gabanshu yana dauke idanunshi daga kanta ya soma aikinsa,wanda galibi na office ne wanda ya kamata ace a matsayinsa na shugaba ya dubasu da kanshi.
Chapter 78 · 0% Book details