Sashe 100
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Duk wata juriyarta taji tana neman ta qare,saboda haka saita sauko ta soma zuba mishi abinci
"Sannu,ko zaka daure kaci wannan?" Kai ya girgiza mata yana bata hannunshi alamun ta taho
"Bashi nake buqata ba ke nake buqata...." Idanunta ta janye daga cikin nashi tana jin yadda zuciyarta ke zillo,tana addu'a cikin ranta,Allah ya sanya abinda take ji game da khalipha shima yana ji a kanta,Allah yasa yadda take fama da qaunarshi cikin zuciyarta shi dinma haka ne,tana tsaka da wannan tunanin ta tsinceshi zaune gefanta,yana gab da ita qwarai ta yadda har cinyoyinsu na gogar juna,hannunta ya laluba ya saka cikin nashi bayan ya fuskanceta sosai
"Uwaishah....bazan iya boyemiki abinda nake ji a kanki ba,wata iriyar qauna da banda anni ba wata diya mace da nake jin ina yiwa irinta,abun tamkar jarrabi,duk yadda naso na kauda shi abun ya ci tura,dukkanin qarfina ya qare akan kauda afkuwar abun don baki cikakkiyar dama,ina ganin tamkar idan naci gaba dajin haka a kanki kamar na cutar da damar da nace zan baki ne...kamar na karya alqawarin da nayi na cewa zan dauke ki ne tamkar qanwata...eh duk da cewa har yau ina ganin wasu dabi'un naki ina kuma kallonki kamar hajar din saboda kamanceceniyar dabi'unku,kunyi kama sosai ta wannan fannin....uwaishah....inaji a jikina kamar Allah ya aikomu cikin rayuwar juna ne saboda mu taimaki juna,saboda mu qaunaci junanmu,saboda kuma ya duba koken kowanne dayanmu,yaga cewa mu zamu fi kowa fuskantar yana yinmu da irin rayuwar da muke da buqata....uwaisha zuciyata ya soma qaunarki a wani lokaci da bansan yaushe bane,ban tantance hakan ba sai daga bisani,kota yaya nema humaira kin cancanci soyayya,kin tsallake dukkan wasu tarakuna dana d'ana,wanda mata da yawa suka gaza tsallakeshi,kinci jarabawar da mata bila'adadin suka kasa jumurin cinta,hakan kadai ya isa ya tabbatarmin da cewa kedin ta daban ce....humaira ina miqo qoqon barana da ki soni ki qaunace ni,bana son ki soni saboda wani abu na daban,bana son ki duba komai ko kice zaki soni saboda kaza,nafison ki soni saboda ni nidin khalipha,ina son ki soni saboda zuciyar taki tana sona bawai don wani dalili ba na daban,don Allah.....uwaish....ki soni,kiso khalipha"tuni hawaye ya jiqe mata fuskarta,ta kasa barin idanunta abude,yau wai ita aysha ake furtawa cewa ana sonta?,yau ita ake bayyanawa wasu kalamai da bata tsammanin samuwarsu ba cikin duniyarta?,ita akewa wannan matsanancin son?,wai yau itace mutum mai daraja kamar khalipha ke roqon ta soshi?,wace irin qauna haka khalipha ke mata a rayuwa?,koda bai roqi ta soshi ba tana ji jini da tsoka khalipha halittar da za'a sota ce,tana ji har cikin zuciya tuhi da gangar jikinta khalipha wani abu ne na musamman da Allah S W T ya ajewa rayuwarta ne,to waishinma idan bata so khalipha ba wa zata so a rayuwarta?,baisan cewa ta jima tana qaunarshi ba amma saita tsammaci saboda kyautata matan da yakene take jin haka akanshi?,son khalipha ya zame mata wajibi cikin rayuwarta haka take ji
"Pls uwaisha.....idan ban miki ba kika ce bakisona zan haqura don na cika alqawarinki.....saidai bani da tabbacin yadda rayywata zata kasance anan gaba....bansan ta yadda akai soyayya ta yimin shigar ba zata ba....." Ya fada raunin da bata taba ji cikin muryarsa ba yau ta jishi muraran
"A duniya baya ga anni bana jin akwai wata halitta dake sonka sama dani...!"ta furta kalaman na fita daga cikin ruhi da zuciyarta.
"Ka cancanci dukkan wata soyayya ta diya mace,bawai don abinda ka shiga rayuwata ka yimin ba,a'ah dukkan nagartarka na tattare da kai kuma ita zata iya siya maka kowacce irin soyayya,ina qaunarka ya khalipha....." Dukkanin idanunshi ya waro waje yana jin yadda zuciyarshi take qara bugawa da sauri da sauri wanda hakan ya qara tsananta ciwon kanshi,daga gefe daya kuma wani irin yanayin farinciki da baxai iya fasalta irinshi ba ya dinga sauka cikin zuciyarshi a hankali,sai ya sake matsawa jikinta sosai muryarshi na dan rawa
"Da gaske uwaishhhh....da gaske kina sona?" Kai ta gyada masa don tabbatar masa,saboda bakinta ya kasa cewa komai,itama bugun da zuciyarta yake ya sanya jikinta yi sanyi,baiyi wata wata ba ya rungumeta cikin jikinsa tsam,a cikin kunnenta yake rada mata saboda baya jin zai iya magana mai qarfi,ji yake kaman numfashinsa zai dauke,yana jin kamar kanshi zai rabe biyu
"Na....gode uwaishhh....na gode" abinda bakinsa ya dinga furtawa kenan tsahon wani lokaci ba tare daya barta ta bar jikinsa ba.
A hankali ta lura da yadda jijiyar kansa ke harbawa d'il d'il da yadda jikinsa ya dauki zafi,zare jikinta tayi cikin damuwa tana dubanshi,cikin wata murya mai laushi
"Ya khalipha......jikinka ya dauki zafi sosai,ciwon kan nan ya kamata ya barka haka,ya kamata kaje kaga likita,bakaci abinci ba tunda ka dawo?,na zuba maka abinci kaci don Allah kasha magani saika kwanta,wala'alla ka sake samun relief"
"Kece abincin kuma kece maganin gaba daya uwaishhhh,zamanki a jikina ya fiye min komai" ya fada yana bata hannunshi,batayi musu ba ta miqa masa yayi mata jagora zuwa jikinsa na sake rungumeta fiye da d'azu
"Rungume ni sosai uwaishaahh....sanyi nake ji" ya furta cikin rada,hannayenta ta sanya itama gaba daya ta zagayeshi da shi,duk da bai ratsashi ba amma hakan ya qara masa dumi a jikinsa yadda yakeso,shuru ne mai dadi ya ratsa dakin,wanda ya bawa dukka zukatan yin tunani mai kyau yadda ya kamata,ta tsakiyar shurun bacci ya shigo yayi awon gaba dasu gaba daya,wani bacci wanda ya zama na musamman a garesu ita dashi baki daya.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tara saura na safe tana tsaye cikin kyakkyawan kitchen din tana shirya musu breakfast,kusan mintuna ashirin kenan data sato jiki ta fito ta barshi a cikin daki,aikinta take hankali kwance tana yi tana sake kallon kitchen din,ko ina cikin gidan mai kyau ne,iya bedroom din kawai zuwa kitchen data gani ya tafi da ita sosai,komai ya tsaru yadda ya kamata,kana kallo kasan aikin masu ilimi ne.
A qalla ya dauki mintuna goma tsaye yana morewa kallonta,karon farko da yaga ayshan sosai,cikakkiyar mace wadda Allah yayiwa baiwar kyau sura da diri,yadda yake ganin dabi'unta kyawawa masu kyau haka Allah ya kyautata halittarta,yana son ya isa gareta ya rungumeta cikin jikinsa suyi aikin tare,saidai kuma ya tabbatar idan yayi hakan dukkan wani lissafinsa da yake qoqarin tattarawa zai ruguje ne,hakanan zai kasa cika muradi da alqawarin da ya dauka ma ranshi,wani alqawari da yake fatan Allah ya cika mishi shi nan kusa,duk da haka sai ya gaza daurewa,ya saki hannayenshi ya soma takawa cikin sanda har ya isa bayanta dab da ita,caraf yayi ya ruqo qugunta sannan ya dan karata a jikinsa yana cewa
"Assalamu alaiki" ba qaramin firgita tayi ba wanda har yasa ta kusa yin bari,saidai Allah ya tsare farantan gabanta ne guda biyu kawai na roba suka biyota,sallamarsa ita ta sanya mata nutsuwa,ta sauke gauruwar ajiyar zuciya,dariya ya dinga mata mai kama da murmushi bayan ya juyo da ita yana duban qwayar idanunta,sai ya tuna sanda ta shiga bandaki ta kulle kanta,yana qoqarin biye dariyarshi yace
"Ba shakka uwaisha tah gwanar tsoro ce,na manta sanda aka gudu bandaki ana nada haquri fa" ya fada yana kashe mata ido daya,murmushin daya qawata fuskarta ta saki tana dan cije lebanta,tana son ta rama tana dan jin nauyinshi,sai kawai tadan saka tafin hannunta ta bugu qirjinsa kadan
"Wash!" Ya fada yana saka hannun nasa yana dafe inda ta doka din,cikin zaro ido tace
"Lafiya meya faru?"
"Zuciyata" ya fada yana narkewa gami da zuba mata narkakkun idanunshi da suka zame mata kamar dabaibayi,cikin qarfin hali tace
"Me ya sameta?"
"Kin mata rauni bad'ini shine zaki sake mata wani a zahiri" murmushi ne ya subuce mata,saita dan taka kadan ta hade tazarar dake tsakinsu,
"Ni bakasan tawa zuciyar ta zama raurananniya ba kake son sake razana ta?"bakinta saitin wuyanshi take maganar,yadda hucin numfashinta dana bakinta yake sauka saman wuyan nashi,lumshe ido yayi tsigar jikinsa na tashi,ajiyar zuciya ya sauke ya bude idon nashi,sai sannan ya lura data janye daga yadda ta tsaya dazu,kamota ya sakeyi gab dashi sosai suka soma musayar numfashi,idanunshi cikin nata suna kallon juna na wani lokaci,da sauri ya saketa yana maida numfashi gami da qoqarin yiwa kanshi linzami da saiti,aikinta taci gaba da qoqarin ci gaba dayi saidai ta lura ta soma hada shirme.
Dariya ya dan saki yana tsaye bayanta yana kallonta bayan ya gama samo nutsuwarshi,ya gama karantarta tsaf,saidai dole dukansu su jira lokaci,hannunta ya riqe da sauri
" yi haquri madam,wallahi kika zuba wannan abincin bazai ciwu ba yau kam"sai a sannan ta dubi abinda take,gishiri ne ta ciko cokali dashi zata zuba cikin qwan da baifi hudu ba,saita sakar masa cokalin gishirin kunya tana kamata
"Nikam.bansan ma waya cs miki ki taso kibar aikinki ba ki barni ina jin sanyi kizo dora abinci,mu tafi kawai an yafe miki" ya fada yana shirin kama hannunta,saita langwabar da kai a narke tana cewa
"Pls ya khalipha....na kusa gamawa,ka bari na qarasa idan ba haka ba zai zama asara,abincin jiya da darema saidai abadashi Allah yasa ma ba mai yawa bane"
"Kai...gsky to matsa na tayaki ki qarasa,wannan muryar bazan iya tafiya nabar mai ita ba" dariya yaso bata,haka ya iya soyayya?,dama haka masoya suke ji cikin zukatansu?,haka ya tsaya daga bayanta yana tayata qananun abinda zai iya,duk da kusan wayo yayi mata morewa kallonta kawai yake,idan ya kasa daurewa yadan matsa kadan ya rage zafi da haka suka kammala komai tare.
"Sannu,ko zaka daure kaci wannan?" Kai ya girgiza mata yana bata hannunshi alamun ta taho
"Bashi nake buqata ba ke nake buqata...." Idanunta ta janye daga cikin nashi tana jin yadda zuciyarta ke zillo,tana addu'a cikin ranta,Allah ya sanya abinda take ji game da khalipha shima yana ji a kanta,Allah yasa yadda take fama da qaunarshi cikin zuciyarta shi dinma haka ne,tana tsaka da wannan tunanin ta tsinceshi zaune gefanta,yana gab da ita qwarai ta yadda har cinyoyinsu na gogar juna,hannunta ya laluba ya saka cikin nashi bayan ya fuskanceta sosai
"Uwaishah....bazan iya boyemiki abinda nake ji a kanki ba,wata iriyar qauna da banda anni ba wata diya mace da nake jin ina yiwa irinta,abun tamkar jarrabi,duk yadda naso na kauda shi abun ya ci tura,dukkanin qarfina ya qare akan kauda afkuwar abun don baki cikakkiyar dama,ina ganin tamkar idan naci gaba dajin haka a kanki kamar na cutar da damar da nace zan baki ne...kamar na karya alqawarin da nayi na cewa zan dauke ki ne tamkar qanwata...eh duk da cewa har yau ina ganin wasu dabi'un naki ina kuma kallonki kamar hajar din saboda kamanceceniyar dabi'unku,kunyi kama sosai ta wannan fannin....uwaishah....inaji a jikina kamar Allah ya aikomu cikin rayuwar juna ne saboda mu taimaki juna,saboda mu qaunaci junanmu,saboda kuma ya duba koken kowanne dayanmu,yaga cewa mu zamu fi kowa fuskantar yana yinmu da irin rayuwar da muke da buqata....uwaisha zuciyata ya soma qaunarki a wani lokaci da bansan yaushe bane,ban tantance hakan ba sai daga bisani,kota yaya nema humaira kin cancanci soyayya,kin tsallake dukkan wasu tarakuna dana d'ana,wanda mata da yawa suka gaza tsallakeshi,kinci jarabawar da mata bila'adadin suka kasa jumurin cinta,hakan kadai ya isa ya tabbatarmin da cewa kedin ta daban ce....humaira ina miqo qoqon barana da ki soni ki qaunace ni,bana son ki soni saboda wani abu na daban,bana son ki duba komai ko kice zaki soni saboda kaza,nafison ki soni saboda ni nidin khalipha,ina son ki soni saboda zuciyar taki tana sona bawai don wani dalili ba na daban,don Allah.....uwaish....ki soni,kiso khalipha"tuni hawaye ya jiqe mata fuskarta,ta kasa barin idanunta abude,yau wai ita aysha ake furtawa cewa ana sonta?,yau ita ake bayyanawa wasu kalamai da bata tsammanin samuwarsu ba cikin duniyarta?,ita akewa wannan matsanancin son?,wai yau itace mutum mai daraja kamar khalipha ke roqon ta soshi?,wace irin qauna haka khalipha ke mata a rayuwa?,koda bai roqi ta soshi ba tana ji jini da tsoka khalipha halittar da za'a sota ce,tana ji har cikin zuciya tuhi da gangar jikinta khalipha wani abu ne na musamman da Allah S W T ya ajewa rayuwarta ne,to waishinma idan bata so khalipha ba wa zata so a rayuwarta?,baisan cewa ta jima tana qaunarshi ba amma saita tsammaci saboda kyautata matan da yakene take jin haka akanshi?,son khalipha ya zame mata wajibi cikin rayuwarta haka take ji
"Pls uwaisha.....idan ban miki ba kika ce bakisona zan haqura don na cika alqawarinki.....saidai bani da tabbacin yadda rayywata zata kasance anan gaba....bansan ta yadda akai soyayya ta yimin shigar ba zata ba....." Ya fada raunin da bata taba ji cikin muryarsa ba yau ta jishi muraran
"A duniya baya ga anni bana jin akwai wata halitta dake sonka sama dani...!"ta furta kalaman na fita daga cikin ruhi da zuciyarta.
"Ka cancanci dukkan wata soyayya ta diya mace,bawai don abinda ka shiga rayuwata ka yimin ba,a'ah dukkan nagartarka na tattare da kai kuma ita zata iya siya maka kowacce irin soyayya,ina qaunarka ya khalipha....." Dukkanin idanunshi ya waro waje yana jin yadda zuciyarshi take qara bugawa da sauri da sauri wanda hakan ya qara tsananta ciwon kanshi,daga gefe daya kuma wani irin yanayin farinciki da baxai iya fasalta irinshi ba ya dinga sauka cikin zuciyarshi a hankali,sai ya sake matsawa jikinta sosai muryarshi na dan rawa
"Da gaske uwaishhhh....da gaske kina sona?" Kai ta gyada masa don tabbatar masa,saboda bakinta ya kasa cewa komai,itama bugun da zuciyarta yake ya sanya jikinta yi sanyi,baiyi wata wata ba ya rungumeta cikin jikinsa tsam,a cikin kunnenta yake rada mata saboda baya jin zai iya magana mai qarfi,ji yake kaman numfashinsa zai dauke,yana jin kamar kanshi zai rabe biyu
"Na....gode uwaishhh....na gode" abinda bakinsa ya dinga furtawa kenan tsahon wani lokaci ba tare daya barta ta bar jikinsa ba.
A hankali ta lura da yadda jijiyar kansa ke harbawa d'il d'il da yadda jikinsa ya dauki zafi,zare jikinta tayi cikin damuwa tana dubanshi,cikin wata murya mai laushi
"Ya khalipha......jikinka ya dauki zafi sosai,ciwon kan nan ya kamata ya barka haka,ya kamata kaje kaga likita,bakaci abinci ba tunda ka dawo?,na zuba maka abinci kaci don Allah kasha magani saika kwanta,wala'alla ka sake samun relief"
"Kece abincin kuma kece maganin gaba daya uwaishhhh,zamanki a jikina ya fiye min komai" ya fada yana bata hannunshi,batayi musu ba ta miqa masa yayi mata jagora zuwa jikinsa na sake rungumeta fiye da d'azu
"Rungume ni sosai uwaishaahh....sanyi nake ji" ya furta cikin rada,hannayenta ta sanya itama gaba daya ta zagayeshi da shi,duk da bai ratsashi ba amma hakan ya qara masa dumi a jikinsa yadda yakeso,shuru ne mai dadi ya ratsa dakin,wanda ya bawa dukka zukatan yin tunani mai kyau yadda ya kamata,ta tsakiyar shurun bacci ya shigo yayi awon gaba dasu gaba daya,wani bacci wanda ya zama na musamman a garesu ita dashi baki daya.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tara saura na safe tana tsaye cikin kyakkyawan kitchen din tana shirya musu breakfast,kusan mintuna ashirin kenan data sato jiki ta fito ta barshi a cikin daki,aikinta take hankali kwance tana yi tana sake kallon kitchen din,ko ina cikin gidan mai kyau ne,iya bedroom din kawai zuwa kitchen data gani ya tafi da ita sosai,komai ya tsaru yadda ya kamata,kana kallo kasan aikin masu ilimi ne.
A qalla ya dauki mintuna goma tsaye yana morewa kallonta,karon farko da yaga ayshan sosai,cikakkiyar mace wadda Allah yayiwa baiwar kyau sura da diri,yadda yake ganin dabi'unta kyawawa masu kyau haka Allah ya kyautata halittarta,yana son ya isa gareta ya rungumeta cikin jikinsa suyi aikin tare,saidai kuma ya tabbatar idan yayi hakan dukkan wani lissafinsa da yake qoqarin tattarawa zai ruguje ne,hakanan zai kasa cika muradi da alqawarin da ya dauka ma ranshi,wani alqawari da yake fatan Allah ya cika mishi shi nan kusa,duk da haka sai ya gaza daurewa,ya saki hannayenshi ya soma takawa cikin sanda har ya isa bayanta dab da ita,caraf yayi ya ruqo qugunta sannan ya dan karata a jikinsa yana cewa
"Assalamu alaiki" ba qaramin firgita tayi ba wanda har yasa ta kusa yin bari,saidai Allah ya tsare farantan gabanta ne guda biyu kawai na roba suka biyota,sallamarsa ita ta sanya mata nutsuwa,ta sauke gauruwar ajiyar zuciya,dariya ya dinga mata mai kama da murmushi bayan ya juyo da ita yana duban qwayar idanunta,sai ya tuna sanda ta shiga bandaki ta kulle kanta,yana qoqarin biye dariyarshi yace
"Ba shakka uwaisha tah gwanar tsoro ce,na manta sanda aka gudu bandaki ana nada haquri fa" ya fada yana kashe mata ido daya,murmushin daya qawata fuskarta ta saki tana dan cije lebanta,tana son ta rama tana dan jin nauyinshi,sai kawai tadan saka tafin hannunta ta bugu qirjinsa kadan
"Wash!" Ya fada yana saka hannun nasa yana dafe inda ta doka din,cikin zaro ido tace
"Lafiya meya faru?"
"Zuciyata" ya fada yana narkewa gami da zuba mata narkakkun idanunshi da suka zame mata kamar dabaibayi,cikin qarfin hali tace
"Me ya sameta?"
"Kin mata rauni bad'ini shine zaki sake mata wani a zahiri" murmushi ne ya subuce mata,saita dan taka kadan ta hade tazarar dake tsakinsu,
"Ni bakasan tawa zuciyar ta zama raurananniya ba kake son sake razana ta?"bakinta saitin wuyanshi take maganar,yadda hucin numfashinta dana bakinta yake sauka saman wuyan nashi,lumshe ido yayi tsigar jikinsa na tashi,ajiyar zuciya ya sauke ya bude idon nashi,sai sannan ya lura data janye daga yadda ta tsaya dazu,kamota ya sakeyi gab dashi sosai suka soma musayar numfashi,idanunshi cikin nata suna kallon juna na wani lokaci,da sauri ya saketa yana maida numfashi gami da qoqarin yiwa kanshi linzami da saiti,aikinta taci gaba da qoqarin ci gaba dayi saidai ta lura ta soma hada shirme.
Dariya ya dan saki yana tsaye bayanta yana kallonta bayan ya gama samo nutsuwarshi,ya gama karantarta tsaf,saidai dole dukansu su jira lokaci,hannunta ya riqe da sauri
" yi haquri madam,wallahi kika zuba wannan abincin bazai ciwu ba yau kam"sai a sannan ta dubi abinda take,gishiri ne ta ciko cokali dashi zata zuba cikin qwan da baifi hudu ba,saita sakar masa cokalin gishirin kunya tana kamata
"Nikam.bansan ma waya cs miki ki taso kibar aikinki ba ki barni ina jin sanyi kizo dora abinci,mu tafi kawai an yafe miki" ya fada yana shirin kama hannunta,saita langwabar da kai a narke tana cewa
"Pls ya khalipha....na kusa gamawa,ka bari na qarasa idan ba haka ba zai zama asara,abincin jiya da darema saidai abadashi Allah yasa ma ba mai yawa bane"
"Kai...gsky to matsa na tayaki ki qarasa,wannan muryar bazan iya tafiya nabar mai ita ba" dariya yaso bata,haka ya iya soyayya?,dama haka masoya suke ji cikin zukatansu?,haka ya tsaya daga bayanta yana tayata qananun abinda zai iya,duk da kusan wayo yayi mata morewa kallonta kawai yake,idan ya kasa daurewa yadan matsa kadan ya rage zafi da haka suka kammala komai tare.