Sashe 6
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayoyi ya fito da su guda biyu irin wanda asma'un ta zaba tace tana so iri daya sak komai da komai,wayace sabuwar shigowa mai dan karen tsada da kyau ya miqawa asma'un,cike da murna da zumudi ta amsa tana jujjuyata ranta fari qal,saidai tuni murnarta ta koma ciki sanda taga ya miqawa aysha irin tata wayar sak,farincikin dake kan fuskarta ya koma bacin rai,ya sake fito da wasu dogayen riguna masu azabar kyau guda shida ya raba musu uku uku,cikin sanyin jiki da fargaba aysha ta miqa hannu zata amsa,yayin da idanunta ya sauka kan mommy da asma'u,mommyn dai ta share kaman bata gani ba,yayin da asma'u idanunta ke kan ayshan,haka ta amsa cikin sanyin jiki tana jerama daddyn godiya da addu'ar Allah ya qaro budi,wasu kayan ya sake fitarwa ya turawa mommyn yana cewa
"Ga kayan su safina nan,saiki san yadda zaki gobe ki aika musu da saqonsu nima na huta"
"Tohm" ta amsa wanda ga duk wanda yai tsai da hankalinsa zai fuskanci ranta a bace yake,muqullin mota sabuwa dal ya ciro ya miqa mata yana fadin
"Ga taki tsarabar saiki barni na sarara" sai a sannan fuskarta ta washe ta koma kaman da,cike da murna tasa hannu biyu ta karba tana masa godiya
"Ta wajenki saiki barwa su asma'u da aysha su ajje tasun ko?"
"Kan uba" kalmar data subuce daga bakin asma'u,motar data jima da ciwa burin daddyn nata yasa mommy ta bar mata shine yanzun zaice wani wai ita da aysha?,wallahi ko sama da qasa zasu hadu ba zata yi sharing motar nan da ita ba
"Me kike fada asma'u?" Daddyn ya tambayeta yana mai zuba mata ido don yaso yaji kalmarta ta farko
"A'ah mamaki nake daddy,mun gode Allah ya qara budi"
"Ameen" ya fada yana rufe jakarsa,aysha na gefe baki daya a takure
"Alla ya qaro arziqi daddy mun gode,Allah ya saka da alkhairinsa" ta furta a sanyaye
"Amin aisha....amin" ya fada cikin jin dadi,a tajure take,saboda ji take kaman idanun mommy da asma'u na kanta har yanzu,hakan ya sanya ta miqe tare da fakewa da cewa zata duba farfesun naman kan ragon da takewa mommy a kitchen tayi shigewarta kitchen din,zamanta tayi a can tana duba farfesun tare da sake gyara freezer din da suke zuzzuba kayan girke girke da suke da saurin lalacewa har naman ya nuna,zuwa sannan bata jiyo muryar kowa a falon,hakan ya tabbatar mata sun bar gurin kenan,don haka ta juye naman a warmer ta gyara wajen ta baro kitchen din.
Asma'u kadai ta taras ta nutse cikin kujera,idanunta saman t.v saidai ba ita take kallo ba,ta cika tayi fam,ta soma gajiya da yadda daddyn ke dai daita da 'yar qauyen yarinyar a komai nata,da kafin zuwanta duka batasan irin wannan ba,ita kadai ta rage a gabansu sai abinda ta zaba ake mata,komai nata daban yake ba tare da an hadata da kowa ba,kallon baqin ciki tabi aysha da shi wadda ta giftata ta nufi dining ta dora warmer din.
Tana saukowa daga wajen mommy na shigowa falon,cikin hanzari asma'u ta miqe ta gyara zamanta sosai cikin bacin rai ta soma fada kaman zata saki kuka
"Yanzu fisabillilahi mommy ni an kyauta min kenan?,babu dama nace ina son abu sai daddy ya hadani da yarinyar nan,yanzu kaman ni ace in saka kaya iri daya da nata,na riqe waya irin tata,mu shiga mota daya tayi driving nayi,mu shiga makaranta a gani ai wallahi sai friends dina su rainani" mommyn dake shirin zama nan wajen tace
"To ya zakiyi husna,sarai kinsan halin mahaifinku,idan yayi niyyar abu babu kai hanashi" ta sake narkewa kaman mai shirin fidda qwalla tace
"Ni wallahi na fahimci kawai daddy ya shurya zubda min mutunci na da ajina,ke ba sai kiyiwa tufkar hanci ba mommy,gaskiya bazan yarda ba nidai kawai ki karbi wayar kya siya mata wata,koni na saka hamid ya kawo mata dai dai ita daga kamfaninsu tunda sun fara qananun wayoyi daga 50k zuwa sama"
"To ai shikenan indai kinsan zaki kawo mata watan,banson ne daddynku ya fuskanci bata hannunta ya daga ma mutane hankali....aysha" mommy ta qwala mata kira wadda ita tuni har ta isa dakinta ma tana shirin daura alwala tayi shafa'i da wutiri,sai ta fasa ta fita kiran mommyn
"Wayar da daddynku ya baku dazu zaki kawomin na ajjiye miki wajena,za'a kawo miki wata wannan bai kamata ki fara amfani da irinta ba tun yanzu" cike da rashin damuwa ta nunawa mommyn inda kayan suke,don tunda aka soma dramer tasan akwai abinda zai biyo baya shinyasa ma bata debe kayan ba,asma'un ita taje ta birkita kayan ta dauko wayar tana jifan ayshan da harara kamar ita ta cewa daddyn ya aikata hakan ko tana da masaniyar zai aikata din
"A'ah dawo ki debi sauran kayan mana ya zaki barsu nan?" Mommy tace da aysha wadda take niyyar komawa dakinta,bata ce komai ba ta dawo ta kwashesu tana fadin
"An gode".
" ke kawo....zonan mu ga"asma'u ta fada cikin hargagi,ba musu ta dawo da baya ta sake zube kayan a gabanta,hannu ta saka ta bibbirkita ta ciro doguwar riga guda daya wadda bata da kalarta cikin wadda daddyn ya raba musu,gefanta ta jefa tana cewa
"Jeki wannan ta yimin,kamar ma tafi tawa tsada,ina da wata idan na shiga daki zan dauko miki a amadadinta" Tsaki asma'u taja bayan ayshan ta shiga dakin
"Rigima ce fa kawai irin ta daddynku,ita kanta yarinyar na fuskanci rayuwa bata dameta ba,yarinyar data taso a qauye saika dinga siyan kaya na manyan kudi kana bata,harda abinda batasan darajarsa ba ma....miqo min wayar" mommy ta fada tana miqawa asma'u hannu,saita noqe
"Namecy zan bawa ita mommy please" dan zare ido mommy tayi
"Ke bana son sakarci bani nace" cikin shagwaba tace
"Habba mana mommy,kinsan 'yar waye ne cikin garin nan?,wallahi nasan na bata wannan wayar as a gift ba qaramin daga min aji kyautar zatayi ba" harara mommyn ta watsa mata
"Yar banza,sai shegen son suna da tara qawaye"
"Thank you my mommy,i love you so much" ta fada tana tsalle hadi da faduwa saman kujerar cikin farinciki,ta tabbata gobe zatayi abunda kowacce saita kalleta cikin qawaye,haka nan husna zata sake ganin darajarta da yadda da irin kudin nasu gidan,duk da qawaye ne amma gasa ce sosai a tsakaminsu,kowacce so take tayi abinda zata burge daga,kowacce so take 'yar uwarta taga ta fita,kowacce so take ta ganta itace a gaba ta baro daya a baya,su kansu basu san cewa abota suke mara ma'ana ba,har hassada da qyashi da kishi ya shigo cikin tarayyarsu yayi kane kane ba tare da sun sani ba,abu daya ne ya hana mommy amshe wayar jin cewa 'yar wani za'a bawa,kasancewarta mace mai son mu'amala da manyan mutane,tana son a ganta tana mu'amala da wani,wanin ma da yayi suna ya kuma shahara,haka dabi'arta take a jininta take,kusan ba'a qasa yaranta suka dauki wannan dabi'a,za'a iya cewa duk cikinsu mutum daya ce ta banbanta da su,halayenta kusan irin na mahaifinta ne,hakan ya sanya babu jituwa ko alaqa mai qarfi tsakaninta da asma'u,saboda banbancin ra'ayi da hali.
A hankali yake kurbar lemon dake cikin tambulan din qarau na glass sake gabanshi,yayi kyau cikin shigar da yafiyi shigar suit musamman idan ranakun aiki ne,yanayin zamanshi a wajen da yadda yake kai lemon bakinsa lokaci lokaci kadai ya isa ya gaya maka nutsuwar da yake sa ita uwa uba aji da kyau da Allah ya bashi,kusan babu budurwar da zata shigo wajen bata kalleshi ba,masu rawar kan cikinsu kanyi sha'awar dosar sa su taya hajarsu saboda alamun malasa da suke hangowa tattare da shi,saidai basu iya qarasawa saboda kwarjinin da yake da shi suke karya kwana su sauya hanya.
Agogonsa ya sake dubawa ya yarfar da hannu gami da jan tsaki,banda haduwarsu da mas'ood yau ta zama dole baiga abinda zai sashi zaman wajen ba,sam wajen baiyi masa ba,akwai yawaitar cakudedeniyar maza da mata abinda yafi tsana,yana da kishi qwarai duk da cewa kuwa baida qanwa mace,a zahiri zaka ce bai damu da motsin dake faruwa a wajen ba,saidai a badini yana zaune ne yana sake.nazarta da karatun halayyar 'yammatan zamani,abubuwa da yawa sun faru da suka bashi mamaki suka kuma sake sa mishi tsanar zaman wajen,yana mamakin yadda yammatan ke shigowa,wata tsakiyar maza biyu wata namiji daya,ba wani kunya ko takatsantsan da aka san diya mace da ita,ta zauna cikinsu suci abinci ko abinsha suna hira kaman zasu tafa,wasunsu ma sukan kebe can baya suje susha shisha,wanda shi a wajenshi bata da maraba da taba wiwi da sholisho,hakan take ko a wajen malaman lafiya,zuqa daya ta shishar dai dai yake da ka zauna kasha karan taba sigari guda dari biyu,yana da yaqinin mafi yawansu ba nan suka cewa iyayensu zasu ba,suna iya qarya da sunan mabanbantan wurare da sunan cewa can suka nufa,su binne iyayen har su zo su koma basu fuskanci komai ba.
Dogon tsaki ya kuma ja yana niyyar dauke kanshi wata mota ta shigo wajen,hakanan yaji ta dauki hankalinsa,bawai don kyanta ko bai taba ganin irinta ba,a'ah,hasalima shekararsa uku da hawanta,duk da ba ita yake kallo kai tsaye ba amma hankalinshi na wajen.
kaman a mafarki yaga khadija na fitowa daga gaban motar bayan matashin dake tuqa motar ya zagayo ya bude mata,yana iya ganin sanda ta sauya hijabin jikinta da mayafi sannan ta fito,tare suka jero har zuwa kan daya daga cikin kujeru da teburan dake wajen suna wa juna magana.
Sosai mamaki ya kamashi,don bai tsammaci ganinta a ire iren guraren nan ba tare da wani namiji,da kuma shiga irin ta jikinta,aljihunsa ya laluba sai yaji wayarshi da yake kiranta da ita,yaji dadin hakan,don dama ya taho da ita ne saboda yana da plan din daga nan ya leqa wajenta.
"Ga kayan su safina nan,saiki san yadda zaki gobe ki aika musu da saqonsu nima na huta"
"Tohm" ta amsa wanda ga duk wanda yai tsai da hankalinsa zai fuskanci ranta a bace yake,muqullin mota sabuwa dal ya ciro ya miqa mata yana fadin
"Ga taki tsarabar saiki barni na sarara" sai a sannan fuskarta ta washe ta koma kaman da,cike da murna tasa hannu biyu ta karba tana masa godiya
"Ta wajenki saiki barwa su asma'u da aysha su ajje tasun ko?"
"Kan uba" kalmar data subuce daga bakin asma'u,motar data jima da ciwa burin daddyn nata yasa mommy ta bar mata shine yanzun zaice wani wai ita da aysha?,wallahi ko sama da qasa zasu hadu ba zata yi sharing motar nan da ita ba
"Me kike fada asma'u?" Daddyn ya tambayeta yana mai zuba mata ido don yaso yaji kalmarta ta farko
"A'ah mamaki nake daddy,mun gode Allah ya qara budi"
"Ameen" ya fada yana rufe jakarsa,aysha na gefe baki daya a takure
"Alla ya qaro arziqi daddy mun gode,Allah ya saka da alkhairinsa" ta furta a sanyaye
"Amin aisha....amin" ya fada cikin jin dadi,a tajure take,saboda ji take kaman idanun mommy da asma'u na kanta har yanzu,hakan ya sanya ta miqe tare da fakewa da cewa zata duba farfesun naman kan ragon da takewa mommy a kitchen tayi shigewarta kitchen din,zamanta tayi a can tana duba farfesun tare da sake gyara freezer din da suke zuzzuba kayan girke girke da suke da saurin lalacewa har naman ya nuna,zuwa sannan bata jiyo muryar kowa a falon,hakan ya tabbatar mata sun bar gurin kenan,don haka ta juye naman a warmer ta gyara wajen ta baro kitchen din.
Asma'u kadai ta taras ta nutse cikin kujera,idanunta saman t.v saidai ba ita take kallo ba,ta cika tayi fam,ta soma gajiya da yadda daddyn ke dai daita da 'yar qauyen yarinyar a komai nata,da kafin zuwanta duka batasan irin wannan ba,ita kadai ta rage a gabansu sai abinda ta zaba ake mata,komai nata daban yake ba tare da an hadata da kowa ba,kallon baqin ciki tabi aysha da shi wadda ta giftata ta nufi dining ta dora warmer din.
Tana saukowa daga wajen mommy na shigowa falon,cikin hanzari asma'u ta miqe ta gyara zamanta sosai cikin bacin rai ta soma fada kaman zata saki kuka
"Yanzu fisabillilahi mommy ni an kyauta min kenan?,babu dama nace ina son abu sai daddy ya hadani da yarinyar nan,yanzu kaman ni ace in saka kaya iri daya da nata,na riqe waya irin tata,mu shiga mota daya tayi driving nayi,mu shiga makaranta a gani ai wallahi sai friends dina su rainani" mommyn dake shirin zama nan wajen tace
"To ya zakiyi husna,sarai kinsan halin mahaifinku,idan yayi niyyar abu babu kai hanashi" ta sake narkewa kaman mai shirin fidda qwalla tace
"Ni wallahi na fahimci kawai daddy ya shurya zubda min mutunci na da ajina,ke ba sai kiyiwa tufkar hanci ba mommy,gaskiya bazan yarda ba nidai kawai ki karbi wayar kya siya mata wata,koni na saka hamid ya kawo mata dai dai ita daga kamfaninsu tunda sun fara qananun wayoyi daga 50k zuwa sama"
"To ai shikenan indai kinsan zaki kawo mata watan,banson ne daddynku ya fuskanci bata hannunta ya daga ma mutane hankali....aysha" mommy ta qwala mata kira wadda ita tuni har ta isa dakinta ma tana shirin daura alwala tayi shafa'i da wutiri,sai ta fasa ta fita kiran mommyn
"Wayar da daddynku ya baku dazu zaki kawomin na ajjiye miki wajena,za'a kawo miki wata wannan bai kamata ki fara amfani da irinta ba tun yanzu" cike da rashin damuwa ta nunawa mommyn inda kayan suke,don tunda aka soma dramer tasan akwai abinda zai biyo baya shinyasa ma bata debe kayan ba,asma'un ita taje ta birkita kayan ta dauko wayar tana jifan ayshan da harara kamar ita ta cewa daddyn ya aikata hakan ko tana da masaniyar zai aikata din
"A'ah dawo ki debi sauran kayan mana ya zaki barsu nan?" Mommy tace da aysha wadda take niyyar komawa dakinta,bata ce komai ba ta dawo ta kwashesu tana fadin
"An gode".
" ke kawo....zonan mu ga"asma'u ta fada cikin hargagi,ba musu ta dawo da baya ta sake zube kayan a gabanta,hannu ta saka ta bibbirkita ta ciro doguwar riga guda daya wadda bata da kalarta cikin wadda daddyn ya raba musu,gefanta ta jefa tana cewa
"Jeki wannan ta yimin,kamar ma tafi tawa tsada,ina da wata idan na shiga daki zan dauko miki a amadadinta" Tsaki asma'u taja bayan ayshan ta shiga dakin
"Rigima ce fa kawai irin ta daddynku,ita kanta yarinyar na fuskanci rayuwa bata dameta ba,yarinyar data taso a qauye saika dinga siyan kaya na manyan kudi kana bata,harda abinda batasan darajarsa ba ma....miqo min wayar" mommy ta fada tana miqawa asma'u hannu,saita noqe
"Namecy zan bawa ita mommy please" dan zare ido mommy tayi
"Ke bana son sakarci bani nace" cikin shagwaba tace
"Habba mana mommy,kinsan 'yar waye ne cikin garin nan?,wallahi nasan na bata wannan wayar as a gift ba qaramin daga min aji kyautar zatayi ba" harara mommyn ta watsa mata
"Yar banza,sai shegen son suna da tara qawaye"
"Thank you my mommy,i love you so much" ta fada tana tsalle hadi da faduwa saman kujerar cikin farinciki,ta tabbata gobe zatayi abunda kowacce saita kalleta cikin qawaye,haka nan husna zata sake ganin darajarta da yadda da irin kudin nasu gidan,duk da qawaye ne amma gasa ce sosai a tsakaminsu,kowacce so take tayi abinda zata burge daga,kowacce so take 'yar uwarta taga ta fita,kowacce so take ta ganta itace a gaba ta baro daya a baya,su kansu basu san cewa abota suke mara ma'ana ba,har hassada da qyashi da kishi ya shigo cikin tarayyarsu yayi kane kane ba tare da sun sani ba,abu daya ne ya hana mommy amshe wayar jin cewa 'yar wani za'a bawa,kasancewarta mace mai son mu'amala da manyan mutane,tana son a ganta tana mu'amala da wani,wanin ma da yayi suna ya kuma shahara,haka dabi'arta take a jininta take,kusan ba'a qasa yaranta suka dauki wannan dabi'a,za'a iya cewa duk cikinsu mutum daya ce ta banbanta da su,halayenta kusan irin na mahaifinta ne,hakan ya sanya babu jituwa ko alaqa mai qarfi tsakaninta da asma'u,saboda banbancin ra'ayi da hali.
A hankali yake kurbar lemon dake cikin tambulan din qarau na glass sake gabanshi,yayi kyau cikin shigar da yafiyi shigar suit musamman idan ranakun aiki ne,yanayin zamanshi a wajen da yadda yake kai lemon bakinsa lokaci lokaci kadai ya isa ya gaya maka nutsuwar da yake sa ita uwa uba aji da kyau da Allah ya bashi,kusan babu budurwar da zata shigo wajen bata kalleshi ba,masu rawar kan cikinsu kanyi sha'awar dosar sa su taya hajarsu saboda alamun malasa da suke hangowa tattare da shi,saidai basu iya qarasawa saboda kwarjinin da yake da shi suke karya kwana su sauya hanya.
Agogonsa ya sake dubawa ya yarfar da hannu gami da jan tsaki,banda haduwarsu da mas'ood yau ta zama dole baiga abinda zai sashi zaman wajen ba,sam wajen baiyi masa ba,akwai yawaitar cakudedeniyar maza da mata abinda yafi tsana,yana da kishi qwarai duk da cewa kuwa baida qanwa mace,a zahiri zaka ce bai damu da motsin dake faruwa a wajen ba,saidai a badini yana zaune ne yana sake.nazarta da karatun halayyar 'yammatan zamani,abubuwa da yawa sun faru da suka bashi mamaki suka kuma sake sa mishi tsanar zaman wajen,yana mamakin yadda yammatan ke shigowa,wata tsakiyar maza biyu wata namiji daya,ba wani kunya ko takatsantsan da aka san diya mace da ita,ta zauna cikinsu suci abinci ko abinsha suna hira kaman zasu tafa,wasunsu ma sukan kebe can baya suje susha shisha,wanda shi a wajenshi bata da maraba da taba wiwi da sholisho,hakan take ko a wajen malaman lafiya,zuqa daya ta shishar dai dai yake da ka zauna kasha karan taba sigari guda dari biyu,yana da yaqinin mafi yawansu ba nan suka cewa iyayensu zasu ba,suna iya qarya da sunan mabanbantan wurare da sunan cewa can suka nufa,su binne iyayen har su zo su koma basu fuskanci komai ba.
Dogon tsaki ya kuma ja yana niyyar dauke kanshi wata mota ta shigo wajen,hakanan yaji ta dauki hankalinsa,bawai don kyanta ko bai taba ganin irinta ba,a'ah,hasalima shekararsa uku da hawanta,duk da ba ita yake kallo kai tsaye ba amma hankalinshi na wajen.
kaman a mafarki yaga khadija na fitowa daga gaban motar bayan matashin dake tuqa motar ya zagayo ya bude mata,yana iya ganin sanda ta sauya hijabin jikinta da mayafi sannan ta fito,tare suka jero har zuwa kan daya daga cikin kujeru da teburan dake wajen suna wa juna magana.
Sosai mamaki ya kamashi,don bai tsammaci ganinta a ire iren guraren nan ba tare da wani namiji,da kuma shiga irin ta jikinta,aljihunsa ya laluba sai yaji wayarshi da yake kiranta da ita,yaji dadin hakan,don dama ya taho da ita ne saboda yana da plan din daga nan ya leqa wajenta.