← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 96 OF 114

Sashe 96

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Da sallama ta shiga falon daddyn,yana zaune qasan carfet ya jingina da kujera,mummy na gefanshi tana hada mishi abinci,a ladabce ta qarasa gabanshi ya zube tana gaidashi da dubashi da jiki,fuskarshi fal da fara'a yake amsa mata,sannan ta waiwaya rana gaida mummy,da qyar take amsa mata,itakam a rayuwa ta rasa me ta yiwa mummyn,idan ma har zamansu ne tare bataso a baya ai zuwa yanzu yaci ace ta aje komai tunda tabar musu gidan,zata tashi daddyn ya tsaidata,hira suke sosai wadda suka jima basuyi irinta ba da daddyn,taji dadin hirar tasu ita kanta ba kadan ba,daga bisani tayi sallama da daddyn bayan ta aje masa kudi masu yawa,da fari qin amsa yayi yace shime bata ne ai
"Nasani daddy kafi qarfinsu,amma abinda kayimin a rayuwa kafi qarfin komai a wajena,badon baka dashi ba na baka,saidon bansan me zan baka din ba,amma wannan ka amsa daddy kasa min albarka ka nuna jin dadinka wannan shine kadai zai faranta min ,ya kuma tabbatarmin da kaji dadin kyauta ta"
"Shikenan indon baffale,Allah yayi miki albarka ya albarkacu rayuwarki,jiyan ma munyi waya da maigidan naki ya dubani da jiki,Allah yayi muku albarka"
"Amin daddy" ta amsa kanta a qasa tana jin wani abu cikin ranta,yaushe khalipha ya kira daddyn amma ita ya shareta,toko laifi tayi masa?,da wannan tunanin ta baro sashen daddyn ta dawo sashen mummy,asma'u ta tadda kawai a falon,sai anty halima dake dakin mummy tana bacci,saura duka sun tafi,da murmushi kan fuskarta ta dubi ayshan
"Ina mai gidan ya kika barshi?"
"Yana lafiya" ta bata amsa fuskarta a sake,saidai zuciyarta cike fal da mamaki,dama akwai sanda asma'u zata tambayi lafiyar khaliphan,tsaki asma'un taja wanda ya katse tunanin ayshan ta sauke wayar data kanga akunne
"Pls aysha bani aron wayarki don Allah zanyi wata waya,bashi nake bin wata mata idan na kira taga numberta ce sai taqi dagawa" wayar tata ta ciro daga jakarta ta miqa mata sannan ta miqe,alwala dama takeso ta daura zatayi sallar la'asar ,don haka ta shige toilet din dake parlour din donta daura alwala.

Cikin hanzari ta dauki abinda zata dauka a wayar sannan ta fita ta aje mata wayar tana murmushi cikin ranta,sanda ta fito daukar wayar tayi ta sanya cikin jakarta sannan ta tada sallah,bayan ta idar ta yiwa mummy sallama ta baro gidan.

Tana cikin revers zata fice daga gidan taga anty halima da asma'u sun fito,da alama wani waje zasu je,hakan ya sanya ta dakata har suka qaraso gab da ita,cikin murmushi tace
"Anty naga kamar wani waje zaku"
"Eh ya akayi?"
"Ku shigo saina rage muku hanya" ta fada tana bude musu qofar motar
"A'ah,jeki kawai" anty halima ta fada tana yin gaba asma'u ta bita a baya,sai dataga sun wuce sannan ta tashi motar itama ta fice a gidan tana girgiza kai kawai cike da mamakinsu,har yau ace jiya iyau alqarasu?,Allah ya kyauta ta furta a sarari sanda take hawa saman titi.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Duk yadda yaso daurewa cikin kwanakin gaba daya juriyarshi ta qare,ya tabbatar wa kansa da cewa soyayya ce ta kamashi,soyayya aysha ce ta masa kamu bana wasa ba,irin soyayyar da bai zaci zai bawa wata diya mace irinta ba,cikin daren ya kasa bacci gaba daya sai juyi da yakeyi,ji yake idan har baiji muryarta ba wani abu xai iya faruwa dashi,dole ya janyo wayarshi yayi kiran layinta.

A lokacin itama tana cikin falon sashensu tana karatu,don tun sanda annin ta tafi bata fiya zama a wancan falon ba,don gaba daya ta kame kanta itama saboda su rahama,sai taso ma sannan suke ganinta,tayi qoqarin dai killace duk wani abu daya kamata,tun randa aka rasa atamfar anni daya cikin ukun data bayar akai mata dinki,idanunta ta daga kawai ta dubi wanda ke kiran,sunanshi ta gani saman screen dinta yana yawo,wani abu mai kama da jan aji ya motsa mata,saita share kiran har ya katse,sake kiranta yayi karo na biyu,nan ma tana sane ta basar da kiran,don ta tabbata cewa lafiya lau ya daina kiranta da replying saqonninta.

Zama yayi daram kan gadonshi sanda yake sake kiranta karo na uku,jikinsa har dan rawa yake yana addu'ar ta amsa ba tare ma da yasan yana yi ba,baisan cewa haka ya damu da ita ba,baisan cewa haka yayi kewarta ba,baisan cewa haka soyayyarta ta kamashi da zafi ba sai yanzu,bata daga din ba sai gab da zata yanke ta kara a kunneta hadi da yin sallama,wata ajiyar zuciya ya sauke da qarfi a sarari wadda ta ratsa dodon kunnen aysha,saita lumshe idanu tana jin muryarshi yana amsa sallamarta
"Uwaishah...." Sai taji sunan yayi mata dadi qwarai har data lumshe ido
"Ya Allah,what a nice name" ta fada cikin zuciyarta,tana jin zuciyarta na mata nauyi dauke da wani abu mai wuyar fassara,gaidashi ta soma yi ya amsa murya can qasa sannan yace
"Uwaish bakya kewata ko?,duk yadda naso na daure na kasa,wannan abun ba lafiya ba" idanu ta zaro don bata fahimci kalmarsa ta qarshe ba
"Me ya sameka kuma ya khaliphah?" Yadda ta ambaci sunanshi karon farko saida murmushi ya subucr daga lebansa
"Asiri kika yimin ko ayeesha?" Gabanta ne ya fadi sosai,tsoro ya kamata,sai zuciyarta ta karye,tuni hawaye suka tsattsafo cikin idanunta
"Ya khalpha?,asiri fa?,na rasa wa zan yiwa asiri saikai?,don Allah ka yimin bayani waya gaya maka haka?" Ta qarashe muryarta na rawa,dariya sosai take cinsa saiya kanne
"Ki jirani zan gaya miki" ya fadi yana katse wayar saboda ya kasa boye dariyarsa,baiso kuma taji,wayar na hannunshi yana jujjuyaya yana kallonta,iya muryarta kawai daya ji ta kwantar masa da.hankali sosai,hakanan cikin jikinsa yaji ayshan kuka take,saboda haka saiya rubuta mata texs

_idan kikayi kuka toki tabbatarwa kanki da kanki baki da gaskiya,hakanan idan kika damu to shima baki da gaskiya,just in kin yarda da.kanki fell free kawai,ki tanadi abinda zaki kare kanki idan nazo tuhumarki_

Saqon nashi ta dinga maimaita karantawa,saita samu kanta da share hawayen fuskarta,ta dinga maimaita karanta saqon nashi,ta wani bangaren yana mata kama da gaske,ta wani bangaren kuma yafi mata kama da wasa da tsokana,to amma yaushe suka fara haka da khaliphan?,sai taji matuqar kewarshi,tana son ganin fuskarshi mai kyau da kwarjini,hakan ya sanya ta ture litattafanta ta jawo system dinta ta shiga inda ya adana mata hotunanshi ta hau kalla daya bayan daya.

Nishadi yake ji sosai cikin zuciyarshi,saiya sauka daga saman gadonshi ya soma duba abubuwa masu amfani a wajensa ya fara hadasu waje guda,bayan ya hau net ya duba idan zai samu jirgin da zai tashi gobe zuwa nijeria ya sayi ticket.

Yana tsaka da wannan kira ya sake shigo masa,sai yabar abinda yake ya duba kiran,salim ne saboda haka ya tabbatar kiran mai muhimmanci ne
"Ya salim ya ake ciki"
"Am sorry boss,zarginka ya tabbata kan mutumin nan....yana amsar kudaden ne yana safarar miyagun qwayoyi,idan ya samu ribar yake dauka ya dawo maka da kudadenka,yanzu haka a rahoton da na samu sunyi niyyar fitar da wasu qwayoyi an kama yaransu,suna kuma gab da fadin sunayen su waye" idanunshi ya runtse sosai,dama ya jima yana tantamar bawa mutumin bashi,banda anni ta sanya baki tun a wancan lokacin da bazai bada ba,lallai ya zama dole ya samu mutumin
"Good job salim,ku jira zuwa ne gobe,but bana son kowa ya sani"
"Thank you boss,Allah ya kawoka lafiya"
"Amin" ya amsa yana katse wayar,ya cillata gefa yana furzar da iska mai dumi daga bakinsa,lalllai bazaiwa mutumin nan ta sauqi ba duk tsufarshi saiya gane baida wayo,ya bata mishi rai qwarao,amma daya tuna chaptershi da ayeeshanshi sai ya saki murmushi yaci gaba da shirinsa yana imagining haduwarsu gobe.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Kwance take saman gadonta,wanda a sannan kusan sha daya da rabi na dare,har a sannan hamid bai dawo ba,ta riga data saba da rashin dawowar tashi wani lokacima sai tsakiyar dare,a da tana damuwa saidai a yanzu sam babu abinda ya shafeta dashi,neman hanyar rabuwarsu kadai ya rage mata donta cimma muradinta.

Cikin shakku da tantama ta soma kiran number khalipha ta farko,nan na'ura ta sanar mata number a kashe take,hakan ya sanya ta tafi kiran daya layin nashi.
Chapter 96 · 0% Book details