Sashe 113
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Baby farha nada wata biyu yace zasu koma ya kammala jarrabawarsa,da fari anni taso yabarsu a gida yaje yayi ya dawo,amma daga bisani ya gaya mata akwai yiwuwar zamanshi a can hakanan suka tarkata suka tafi kowa na kewat baby farha,sun zagaya sallama har takai,zuwa wannan lokacin inna yelwa ta sake sanyi qwarai,ta tabbatar jahilci ya taka muhimmiyar rawa wajen faruwar dukkan abinda ya faru,khalipha bai tafi ba sai daya assasa islamiyya can garin ta matan aure da yara,wanda ya dauko ingantattun malamai masana sunnar Allah da ma'aiki suka hau koyar da al'ummar garin ka'in da na'in,suka yi nasarar yaqar duk wani baqin tunani,da baqar alaqa da dangantaka dake tsakanin fulani da manoma,basu bar qasar ba sai da aka sanya ranar aliya da mahmoud,wanda ya matsa qwarai yana ganin kamar zai rasa aliyar ne ko kuma taqi bashi dama.
Ta bangaren haidar ma tunda yaga basma ya soma kai kawo,wanda daga qarshe ya bayyana muradinsa,ayshan dai batasan ya ake ciki ba har suka bar nigeria zuwa cyprus.
Randa zasu tashin suna tsaka da shiri aka ce ana sallama dashi,hakanan ya fito bai kammala shiryawa ba don yayi mamakin wanda ke nemansa a irin wannan lokacin ya fito zuwa falon da yake ganawa da baqinsa.
Kawu hamza,kawu munzali,kawu habibu da kawu saminu,dukkansu suna zaune qasan tile din dake malale a dakin,suna zaune tsumu tsumu kamar wadanda aka tsoma kaza cikin ruwa,kallo daya zaka yi musu kasan cewa dukkaninsu suna jin jiki na rayuwa dana abinda suka aikata.
Dubansu yake yayin da kowa ya gyara zama yana miqo gaisuwa,amsa musu yayi kadaran kadaham kafin shuru ya biyo baya an rasa wanda zai soma magana a cikinsu,kawu saminu ne yayu qarfin halin soma neman musu yafiyar khalipha,don dukkansu mutuwar idris ta zame musu izinina,daga qarshe ya rufe
"Haqiqa shaidan ya taka muhimmiyar rawa wajen yi mana huduba,da banzayen zukatanmu marasa son Allah,muka bijire muka kwashe dokiyoyinku muka cinye,sannan uwa uba muka kasa kula daku muka yiwa mahaifinku butulci,mutuwar idris kawai ta isa ta nuna mana makomarku matuqar baka yafe mana ba kuma bamu nemi yafiyar Allah ba,iya halin da muke ciki ma yanzu kawai munga ishara babba,bamu da nutsuwa cikin gidajenmu da rayuwarmu,yaranmu duka kowanne da tashi matsalar Allah ya jarrabemu,ka daure badonmu ba badon halinmu ba ka yafe mana"
Iska mai zafi ya furzar da ita daga bakinsa yana qoqarin controlling kanshi,tsahon mintuna biyar shuru ya ratsa falon
"Allah ya yafe mana gaba daya" dukkansu qwalla suke sharewa suna godiya,yana tsaye yana kallonsu har suka gama ficewa daga falon sannan ya juya ya koma ciki,zuciyarshi cike fal da tunani kala kala,rayuwa ita haka take,dukkan yadda ka dauketa haka take zuwa maka,mafitarka daya kabi Allah kabi dukkan dokokinsa.
60
*_BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYU_*
Misalin sha d'aya na safe jirgin dake dauke da iyalan muhammad khalipha sa'id mai goro ya sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano dake kano.
Yarinya ce 'yar kimanin shekara goma sha uku ce a gaba riqe da hannun wani yaro d'an kimanin shekara biyar,bayanta wata matashiyar macace fara tas mai matsakaicin tsayi da dogon hanci,wadda kana mata kallo d'aya zaka tabbatar da cewa hutu jin dadi da gayu sun ratsata take biye da ita,fuskarta qunshe da murmushi wanda hakan ya bayyana dimple dinta dake kumatunta na hagu da dama,tana dauke da wani kyakkyawan yaron wanda baifi shekara uku ba,sak kamanninsa na muhammad khalipha ne mai goro,shine ya fito a qarshe yana ruqe da qananun akwatina masu kyau guda biyu,shima fuskarshi na dauke da murmushi da alama magana suke da uwargida sarautar mata ayshatu dake gabanshi
"Farha....oya bani jawad ki amshi trolly dinku" da gudu jawad ya zame hannunshi daga na farhan yana tawowa wajen aysha,harara khalipha ya jefawa aysha mai nuni da zallar qauna
"Hajar din zan baiwa daukan akwati?" Murmushi ta saki don dama ta sani hakan zata kasance,wata qauna yakewa yarinyar tamkar hajar dinsa,haka suka dinga takowa har zuwa inda motocin MAI GORO suke jiransu.
Dukka qofofin motocin a bude suke suna jiran isowar boss din nasu,suna hangosu a hanzarce suka amshi akwatunan hannunshi suka shige mota guda shi da iyalin nashi gaba daya.
Kwabe fuska jawad yayi yana duban aysha
"Anna...ba gidan anni zamu fara zuwa ba?"
"Ban sani ba tambayi abbinku" ta fada tana gyarawa fu'ad kwanciya a jikinta,duban khalipha yake yana son magana yana tsoro,saboda last time da sukazo yace ba zasu sake zuwa su kwana wajen annin ba,saboda yadda suke qiriniya da rashin ji idan sunje,yace ba zasu hana uwarshi hutawa ba,itama farha kallon abbun nasu take,ita kanta tafison gidan annin,saboda tun suna can sunyi waya dasu amra da afaf (jikokin annin yaran basma da haidar,da 'yar mus'ab),Dukkansu suna can gidan anni suna hutu daga kai khalipha yyi ya kallesu sae ya maida kai baice musu komae ba jawad ne yakasa shiru murya a sanyaye yace pls abbu akaimu gidan ammi munyi alqawarin bazamu sake pitina ba baice mishi komai ba ganin hakan shima yaron yaja bakinshi yyi shiru.
Cikin yan mintina suka isa kataparen gidansu dake nasarawa meela road tanpatsetsen gidane da khalipha ygina da yadauki shekaru yana ginashi mention house ne nagani napada a parking space duka motocin suka tsaetsaya su jibiril sukaxo suka bude musu qopa taxuro qaparta xata pito daga motar wayarta ta soma ringing saeta dakata da pitar takira farha ta daukar mata fu'ad duba mekiran tayi inna yalwa ce sae tayi mamaki data ga number nigeria da alama ta dawo gida kenan daga jinyar qaparta da khalipha yapitar da'ita saudiyya sagas a tayi tasa akunnenta gami dayin sallama dagacen bangaren inna yalwa ta amsa
"nayi sa'a kardae kice min kindawo?" Murmushi Aisha tayi gami dacewa "nima yanzu a raina nakecewa ashe kindawo"
"Eh wolh kwanana biyar kenan da dawowa ta"
"Toh yaya jikin"
"Jiki alhmdulilahi nasamu sauqi, kitayani yiwa allaji khalipha godiya Allah yasaka da alkhairi,ya qara budi"
"Amin ai babu komai,cikin satin nan ma zamu shigo takai din in sha Allahu,su mero zasu tare sabon gidansu"
"Ma sha Allahu...an gana kenan?,ke dai indo babu abinda xamu ce dake saidai godiya da fatan alkhairi keda halipha,kaf karkarar nan babu wanda baici arxiqinki ba,babu wanda arziqinki dana mai gidanki baibi ta gidansa ba,Ashe haka rayuwa take,bakasan wanda zaka ci arxiqinsa ba....ki yafemin indo bazan daina neman yafiyarki ba har abada..." Ta qarashe maganar cikin rauni da nuna nadama
"Kai inna,ya wuce fa,sai munzo din"
"Allah ya jiqan mahaifinki indo,ki gaidamin da masu gida na da kishiyata"murmushi ta saki
"zasu ji" ta fada tana kashe wayar ta maidata jaka sannan ta qara fitowa daga cikin motar,zuwa sannan tuni khalipha da sauran yaran sun shiga ciki don haka tabi bayansu a nutse,cikin taku na cikakkiyar mace mai ilimi wadda tasan abinda take,wadda ta gogu da ilimi da zaman duniya.
Bata shiga ciki ba sai data kira mummy bayan ta kira ummi ta sanar mata dawowarsu,ta tabbatar da komai na tafiya lafiya cikin sabon gidan da khaliphan yayi musu,ya dauke shima dukkan wata lalura ta mummyn,don daddy wani mutum ne mai muhimmanci shima a rayuwarshi,bazai taba manta alkhairinsa ba a gareshi,tun daga ranar da yasan abinda ke faruwa ya amshe duk wata dawainiya da da ayshan ta akarba yaci gaba da jan ragamarta,zuciyar khaliphan mai kyau ce,ya manta dukkan wata cuta da wani mai cuta yayi masa,ya rama kowacce cuta da alkhairi,hakan yasa itama ayshan ta qara qaimi,taci gaba da kyautatawa duk wani wanda ya jibanceta na kusa dana nesa.
A nutse cikin nishadi da qaunar iyalin nata ta shiga cikin gidan,ba kowa a falon sanda ta shiga katafaren falon da xai sadaka da sassa daban daban na gidan,dakunan matar gidan,dakunan yaran gidan,ban dakuna,kitchen da kuma sashen baqi mata,sai sashen mai gidan,tunda bata gansu ba tasan ba zasu wuce dakin yaran ba,murmushi ta saki ta zare mayafin rolling dake kanta ta nufi kitchen din gidan don duba masu aikin gidan wadanda dattijan mata be guda biyu rak suke mata aiki,sai guda daya da batakai shekarunsu ba,a yanzu haka tasan suna can don sunsan da dawowarsu.
A mutunce suka gaisa,kai baka ce 'yan aikinta bane,ta dudduba abinda sukeyi sannan ta gaya musu abinda zasu dafawa yara da abinda zasu hada mata wanda zata shigo da kanta ta yiwa khalipha girkinsa.
Ta bangaren haidar ma tunda yaga basma ya soma kai kawo,wanda daga qarshe ya bayyana muradinsa,ayshan dai batasan ya ake ciki ba har suka bar nigeria zuwa cyprus.
Randa zasu tashin suna tsaka da shiri aka ce ana sallama dashi,hakanan ya fito bai kammala shiryawa ba don yayi mamakin wanda ke nemansa a irin wannan lokacin ya fito zuwa falon da yake ganawa da baqinsa.
Kawu hamza,kawu munzali,kawu habibu da kawu saminu,dukkansu suna zaune qasan tile din dake malale a dakin,suna zaune tsumu tsumu kamar wadanda aka tsoma kaza cikin ruwa,kallo daya zaka yi musu kasan cewa dukkaninsu suna jin jiki na rayuwa dana abinda suka aikata.
Dubansu yake yayin da kowa ya gyara zama yana miqo gaisuwa,amsa musu yayi kadaran kadaham kafin shuru ya biyo baya an rasa wanda zai soma magana a cikinsu,kawu saminu ne yayu qarfin halin soma neman musu yafiyar khalipha,don dukkansu mutuwar idris ta zame musu izinina,daga qarshe ya rufe
"Haqiqa shaidan ya taka muhimmiyar rawa wajen yi mana huduba,da banzayen zukatanmu marasa son Allah,muka bijire muka kwashe dokiyoyinku muka cinye,sannan uwa uba muka kasa kula daku muka yiwa mahaifinku butulci,mutuwar idris kawai ta isa ta nuna mana makomarku matuqar baka yafe mana ba kuma bamu nemi yafiyar Allah ba,iya halin da muke ciki ma yanzu kawai munga ishara babba,bamu da nutsuwa cikin gidajenmu da rayuwarmu,yaranmu duka kowanne da tashi matsalar Allah ya jarrabemu,ka daure badonmu ba badon halinmu ba ka yafe mana"
Iska mai zafi ya furzar da ita daga bakinsa yana qoqarin controlling kanshi,tsahon mintuna biyar shuru ya ratsa falon
"Allah ya yafe mana gaba daya" dukkansu qwalla suke sharewa suna godiya,yana tsaye yana kallonsu har suka gama ficewa daga falon sannan ya juya ya koma ciki,zuciyarshi cike fal da tunani kala kala,rayuwa ita haka take,dukkan yadda ka dauketa haka take zuwa maka,mafitarka daya kabi Allah kabi dukkan dokokinsa.
60
*_BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYU_*
Misalin sha d'aya na safe jirgin dake dauke da iyalan muhammad khalipha sa'id mai goro ya sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano dake kano.
Yarinya ce 'yar kimanin shekara goma sha uku ce a gaba riqe da hannun wani yaro d'an kimanin shekara biyar,bayanta wata matashiyar macace fara tas mai matsakaicin tsayi da dogon hanci,wadda kana mata kallo d'aya zaka tabbatar da cewa hutu jin dadi da gayu sun ratsata take biye da ita,fuskarta qunshe da murmushi wanda hakan ya bayyana dimple dinta dake kumatunta na hagu da dama,tana dauke da wani kyakkyawan yaron wanda baifi shekara uku ba,sak kamanninsa na muhammad khalipha ne mai goro,shine ya fito a qarshe yana ruqe da qananun akwatina masu kyau guda biyu,shima fuskarshi na dauke da murmushi da alama magana suke da uwargida sarautar mata ayshatu dake gabanshi
"Farha....oya bani jawad ki amshi trolly dinku" da gudu jawad ya zame hannunshi daga na farhan yana tawowa wajen aysha,harara khalipha ya jefawa aysha mai nuni da zallar qauna
"Hajar din zan baiwa daukan akwati?" Murmushi ta saki don dama ta sani hakan zata kasance,wata qauna yakewa yarinyar tamkar hajar dinsa,haka suka dinga takowa har zuwa inda motocin MAI GORO suke jiransu.
Dukka qofofin motocin a bude suke suna jiran isowar boss din nasu,suna hangosu a hanzarce suka amshi akwatunan hannunshi suka shige mota guda shi da iyalin nashi gaba daya.
Kwabe fuska jawad yayi yana duban aysha
"Anna...ba gidan anni zamu fara zuwa ba?"
"Ban sani ba tambayi abbinku" ta fada tana gyarawa fu'ad kwanciya a jikinta,duban khalipha yake yana son magana yana tsoro,saboda last time da sukazo yace ba zasu sake zuwa su kwana wajen annin ba,saboda yadda suke qiriniya da rashin ji idan sunje,yace ba zasu hana uwarshi hutawa ba,itama farha kallon abbun nasu take,ita kanta tafison gidan annin,saboda tun suna can sunyi waya dasu amra da afaf (jikokin annin yaran basma da haidar,da 'yar mus'ab),Dukkansu suna can gidan anni suna hutu daga kai khalipha yyi ya kallesu sae ya maida kai baice musu komae ba jawad ne yakasa shiru murya a sanyaye yace pls abbu akaimu gidan ammi munyi alqawarin bazamu sake pitina ba baice mishi komai ba ganin hakan shima yaron yaja bakinshi yyi shiru.
Cikin yan mintina suka isa kataparen gidansu dake nasarawa meela road tanpatsetsen gidane da khalipha ygina da yadauki shekaru yana ginashi mention house ne nagani napada a parking space duka motocin suka tsaetsaya su jibiril sukaxo suka bude musu qopa taxuro qaparta xata pito daga motar wayarta ta soma ringing saeta dakata da pitar takira farha ta daukar mata fu'ad duba mekiran tayi inna yalwa ce sae tayi mamaki data ga number nigeria da alama ta dawo gida kenan daga jinyar qaparta da khalipha yapitar da'ita saudiyya sagas a tayi tasa akunnenta gami dayin sallama dagacen bangaren inna yalwa ta amsa
"nayi sa'a kardae kice min kindawo?" Murmushi Aisha tayi gami dacewa "nima yanzu a raina nakecewa ashe kindawo"
"Eh wolh kwanana biyar kenan da dawowa ta"
"Toh yaya jikin"
"Jiki alhmdulilahi nasamu sauqi, kitayani yiwa allaji khalipha godiya Allah yasaka da alkhairi,ya qara budi"
"Amin ai babu komai,cikin satin nan ma zamu shigo takai din in sha Allahu,su mero zasu tare sabon gidansu"
"Ma sha Allahu...an gana kenan?,ke dai indo babu abinda xamu ce dake saidai godiya da fatan alkhairi keda halipha,kaf karkarar nan babu wanda baici arxiqinki ba,babu wanda arziqinki dana mai gidanki baibi ta gidansa ba,Ashe haka rayuwa take,bakasan wanda zaka ci arxiqinsa ba....ki yafemin indo bazan daina neman yafiyarki ba har abada..." Ta qarashe maganar cikin rauni da nuna nadama
"Kai inna,ya wuce fa,sai munzo din"
"Allah ya jiqan mahaifinki indo,ki gaidamin da masu gida na da kishiyata"murmushi ta saki
"zasu ji" ta fada tana kashe wayar ta maidata jaka sannan ta qara fitowa daga cikin motar,zuwa sannan tuni khalipha da sauran yaran sun shiga ciki don haka tabi bayansu a nutse,cikin taku na cikakkiyar mace mai ilimi wadda tasan abinda take,wadda ta gogu da ilimi da zaman duniya.
Bata shiga ciki ba sai data kira mummy bayan ta kira ummi ta sanar mata dawowarsu,ta tabbatar da komai na tafiya lafiya cikin sabon gidan da khaliphan yayi musu,ya dauke shima dukkan wata lalura ta mummyn,don daddy wani mutum ne mai muhimmanci shima a rayuwarshi,bazai taba manta alkhairinsa ba a gareshi,tun daga ranar da yasan abinda ke faruwa ya amshe duk wata dawainiya da da ayshan ta akarba yaci gaba da jan ragamarta,zuciyar khaliphan mai kyau ce,ya manta dukkan wata cuta da wani mai cuta yayi masa,ya rama kowacce cuta da alkhairi,hakan yasa itama ayshan ta qara qaimi,taci gaba da kyautatawa duk wani wanda ya jibanceta na kusa dana nesa.
A nutse cikin nishadi da qaunar iyalin nata ta shiga cikin gidan,ba kowa a falon sanda ta shiga katafaren falon da xai sadaka da sassa daban daban na gidan,dakunan matar gidan,dakunan yaran gidan,ban dakuna,kitchen da kuma sashen baqi mata,sai sashen mai gidan,tunda bata gansu ba tasan ba zasu wuce dakin yaran ba,murmushi ta saki ta zare mayafin rolling dake kanta ta nufi kitchen din gidan don duba masu aikin gidan wadanda dattijan mata be guda biyu rak suke mata aiki,sai guda daya da batakai shekarunsu ba,a yanzu haka tasan suna can don sunsan da dawowarsu.
A mutunce suka gaisa,kai baka ce 'yan aikinta bane,ta dudduba abinda sukeyi sannan ta gaya musu abinda zasu dafawa yara da abinda zasu hada mata wanda zata shigo da kanta ta yiwa khalipha girkinsa.