Sashe 59
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ranar a nan ta wuni gaba daya,ko da su atika zasu shiga girkin dare a lokacin bata jima da gama sallar la'asar ba binsu tayi kitchen din,kusan ranar gaba daya ita tayi girkin daren sai tattaimaka mata da suka dinga yi da wasu abubuwan,da fari qin sakar mata sukayi suna tsoro suna dari dari,daga bisani dole suka sakar mata din ganin yadda take komai cikin qwarewa,a nan suka saba sosai dasu atikan kamar sun jima tare,qarfe shida suka gama ta baro kitchen din ta koma sashensu ta shiga wanka.
A hankali ta tura qofar dakin kaman yana nan duk da tasan baya nan din,gefan akwatunanta ta nufa ta bude,doguwar riga ta ciro ta ajeta saman akwatin sannan ta shiga bandakin ta tura qofar ta sama tara ruwan dumi,ba jimawa ya cika ta soma wankan tana jin dadin dumin ruwan da yadda yake bada qamshi shi da kansa ruwan,ita kadai cikin ranta take jinjina gayu irin na khalipha da son qamshi.
Shida saura ya shigo gidan kamar yadda ya saba sai daya biya yaga anni kafin ya wuce sashensa,annin tana ta qorafin wunin da yayi yauma a waje,dariya kawai yake yana jinjina yadda anni keso ayshan,ya sani duk don saboda ita yayi hakan,tabe baki rahama tayi bayan ya wuce wadda ke zaune gefan annin tana latsa waya ta kalleta
"Nikam wannan auren soyayya akayi?,ango da sai kayi satima kuna gida daya baka ganshi ba amma shi kwana biyu kacal ya soma fita yana wuni?,kodai bata iya kula da miji bane?"
"Banda abinki rahama wannan ai zancanku ne keda yayan naki" anni ta fada tana miqewa don da wuri take daura alwala kafin a kira sallah ta shige toilet abinta,hada ido sukayi da amal,saita saka dariya wadda tayi ne kawai don ta qular da rahaman itama ta miqe ta bar falon ta shige dakinta
Cikin satin aysha ta soma koyan mota sosai ta hannun aliyyu,wanda sam khalipha ya hana mus'ab yace haidar din ya fishi nutsuwa,tun tana dari dari da su har ta soma sakin jiki,haidar nada kirki qwarai,yana da daraja mutum,yadda yake bata girma abun har kunya yake bata,idan taga yadda yake tsarewa rahama da amal gida idan baiga dama ba sai abun yayita bata mamaki,suna kamanceceniyar halayya da khalipha ta wani fannin,zamanta cikin gidan sai ya soma yi mata dadi,ta soma sakewa musamman idan tana tare da anni,duk wata kunya da surukuta anni ta soketa tsakaninsu,sukan zauna su taba hira duk da har yanzu bata iya bude baki sosai tayi magana yadda ya kamata mai tsaho,saidai tana qoqari matuqa wajen ganin ta saba dasu din.
Sati uku da biki ta soma warwarewa sosai,janta a jiki nuna mata ita watace da mu'amala mai kyau shi ya taimaka wajen samuwar wannan sauyin,saidai abu daya da bata jin dadinshi shine yanayin yadda rahama take mu'amalantarta,takan bata girma dai dai gwargwado,hakanan bata shiga sabgar da bata shafeta ba kamar yadda haka halayyarta take tun a gida,saidai duk wani motsi na ayshan a idonta yake kamar wadda aka baiwa gadinta,hakanya sanya itama ta iya takunta take matuqar taka tsantsan da ita.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Parlour din asma'un cike yake da qawayenta na makaranta wanda ta gayyacesu suzo gidanta kwanaki sati hudu da tarewarta,manyan qawayenta ne da take ji da su ko ince a kullum take qoqarin yin abinda zata burgesu su fahimci cewa ita din ba qaramar mace bace,a ranar ta baiwa yarinyar da aka kawo mata a matsayin 'yar aiki qwaya daya 'yat qabilar igbo umarnin ta dafa musu abinci har kala uki,baya ga snacks da lemuka da aka jibge tsakiyar falon,anaci ana kwasar shafta.
Gaba daya hankalinsu yayi gaba babu wadda taji kota lura da shigowarshi,fuskarshi tamke yake bin kowacce da kallo,sai a sannan suka ankara da shigowar tasa,nusaiba itace ta soma masa magana cikin wasa irin na qawar amarya
"Ango kace kana kusa da dawowa ma kenan.....dama kai muke jira ai" maimakon ya sake mata su gaisa kaman yadda suka saba yi a lokacin hidimar biki saitaji yaja tsaki tare da yin gaba ya haye sama,dukansu baki galala suka bishi da kallp har ya gama hawan
"Ke....haka naki mijin kuma yake?" Cewar daya daga cikin qawayen tana riqe da haba cikin mamaki
"Wannan ko anya asma'u?,kinga kallon raini da wulaqancin da yake mana kuwa?"dayar ta kuma fadi
" ni ban gaji wulaqanci ba wlh,oya ku tashi kawai mu wuce"cewar husna babbar qawar asma'un da take ji da ita,sai a sannan da taga suna shirin miqewa asma'u da wani baqinciki ya qumeta da azabar kunya ta magantu
"Babu wannan maganar don Allah kuyi zamanku ina zuwa....yana da fushi ne zai iya yiwuwa a waje aka bata mishi rai bari naje" ta fada da sauri tare da miqewa tayi hanyar stairs ranta na bala'in baci.
Tura qofar dakin tayi,saita sameshi yana tsaye ya kwabe rigarshi saura singlet yana shirin cire dogon wandonshi ta shigo,cikin nuna bacin rai da fusata ta kalleshi
"Haba hamid....ya zaka kunyatani gaban qawayena don Allah?,me suka taba yi maka zaka yi musu wannan wulqancin?,so kake suje gaba su samu abin bada labari?" Bai tankata ba har sai daya cire wandon saura gajeran wando kawai sannan ya dago ya dubeta cikin qanqan da idanu
"Ke,an gaya miki bansan ciwo kudi ba?,ko an gaya miki tsintosu nake?,ohk kin zaci za'a ci gaba da yadda aka saba ko?,toni ba haka nake ba,nasan ciwon kudi nasan mutunci da darajarsu,haka kawai ki taramin garadan qawayenki ki kwaso abinci da abun shan da a qalla zamuyi sati muna ci ki jibge musu don tsabar burga?,to wallahi kiyi gaggawar zuwa ki sallameshi ki kuma kwashemin kayan abincina ki maida store" tsantsar bacin rai da mamaki ne qarara ya bayyana a fuskar asma'u,tana jin ya xama lallai ta nunawa hamid bacin ranta qarara saboda gaba
"Me kake nufi hamid?,qawayen nawa?,to wallahi babu inda zasu,kayan abinci kuma da kake magana ai daga gidanmu aka hadoni da shi ko?" Dawowa yayi da baya maimakon daa da yayi gaba zai shiga wanka
"Haka kika ce?,don an kawo wadan nan matsoyatan kayan abincin kike gaya min haka?,ohk fine....ki gayamin nawa na kashe miki wanda sunyi ninkin baninkin kudin kayan abincin da aka kawo min?,koni na gayawa iyayenko ina da buqatarsu ma?,a matsiyaci kika aureni?,tunda ba zaki iya sallamarsu ba ni zan iya" ya fadi yana nufar qofa,da mamaki ta soma tsaidashi saboda singlet da gajeran wandon dake jikinsa amma ko juyowa baiyi ba bare ya saurareta.
Kaf dinsu saida kowacce ta miqe tsaye a tsorace ganin mijin qawar taso a haka,dubansu yayi sannan ya soma magana
"Kafin na qirga biyar kowacce a cikinku ta kwashi matattun qafafunta tabar min gida tunda yunwa ce ta kawoku,kada wadda ta sake zuwa min gida tasha min koda ruwa ne bare abinci,ku cika cikinku a gidajen ubanku kafin kuxo" cikin bacin rai husna da take jin tafi qargfin wulaqanci ta soma maida masa martani,kanta yayo wanda hakan ya sanya suka qarasa ficewa a guje ba shiri ba tare da sun tsaya daukan kayayyakinsu ba,bayansu yabi cikin daga murya yake baiwa inyamurin mai gadinsu umarni cikin karyayyen turanci
"Maza ka sakar musu karnukan nan su qarasa rakasu" jin abinda yake fada ya sakasu qara mai,taimakon da Allah yayi musu daya motar da suka zo cikinta tana qofar gidan basu shigo da ita ba saboda motocin hamid guda uku dake harabar wajen data asma'u daya data zo da ita ta cike wajen.
A tsaye a falon ya tadda asma'u tana qwallar takaici tare da tunanin anya kan hamid daya kuwa?,lafiyarsa qalau?,kodai ya soma bin hudubar yayyensa mata randa sukazo da sunan sunzo ganin amarya da sukaji suna gaya masa
"Wannan matar taka sai kayi da gaske,makarantarsu daya da nabihat,bata da kirki batason talaka,dagawa gareta da girman kai,hakanan kudinka takeso tosai kayi tsayin daka idan ba haka ba rainaka zatayi wallahi" abu daya ne bata sani ba,hamid mutum ne mai shegen son abun dunuya,yana da dukiya amma ta cinsa ne iya shi kadai,ko sanda yana gida wani abun sai ya rataya a jikin mahaifinsa yayi masa bazai taba qwandala tashi ba,irin yaran nan ne dako.iyayensu basa iya taimakawa banda Allah yasa mahaifin nasa yana da wadata shima,saidai matsalarsa daya mahaifin nasa,mutum ne da bashi da tattali,yana da son nunawa duniya shi wani ne ko nawa zai kashe akan haka zai iya,ya kuma yi nasara don sunansa ya dan fita,sakamakon yadda yake nuna qaryar arziqi don baikai nan ba.
A parlour ya taras da ita zaune tana gunjin kuka,kota kanta baibi ba ya wuce zuwa sama abunshi ya dauki wankanshi.
A hankali ta tura qofar dakin kaman yana nan duk da tasan baya nan din,gefan akwatunanta ta nufa ta bude,doguwar riga ta ciro ta ajeta saman akwatin sannan ta shiga bandakin ta tura qofar ta sama tara ruwan dumi,ba jimawa ya cika ta soma wankan tana jin dadin dumin ruwan da yadda yake bada qamshi shi da kansa ruwan,ita kadai cikin ranta take jinjina gayu irin na khalipha da son qamshi.
Shida saura ya shigo gidan kamar yadda ya saba sai daya biya yaga anni kafin ya wuce sashensa,annin tana ta qorafin wunin da yayi yauma a waje,dariya kawai yake yana jinjina yadda anni keso ayshan,ya sani duk don saboda ita yayi hakan,tabe baki rahama tayi bayan ya wuce wadda ke zaune gefan annin tana latsa waya ta kalleta
"Nikam wannan auren soyayya akayi?,ango da sai kayi satima kuna gida daya baka ganshi ba amma shi kwana biyu kacal ya soma fita yana wuni?,kodai bata iya kula da miji bane?"
"Banda abinki rahama wannan ai zancanku ne keda yayan naki" anni ta fada tana miqewa don da wuri take daura alwala kafin a kira sallah ta shige toilet abinta,hada ido sukayi da amal,saita saka dariya wadda tayi ne kawai don ta qular da rahaman itama ta miqe ta bar falon ta shige dakinta
Cikin satin aysha ta soma koyan mota sosai ta hannun aliyyu,wanda sam khalipha ya hana mus'ab yace haidar din ya fishi nutsuwa,tun tana dari dari da su har ta soma sakin jiki,haidar nada kirki qwarai,yana da daraja mutum,yadda yake bata girma abun har kunya yake bata,idan taga yadda yake tsarewa rahama da amal gida idan baiga dama ba sai abun yayita bata mamaki,suna kamanceceniyar halayya da khalipha ta wani fannin,zamanta cikin gidan sai ya soma yi mata dadi,ta soma sakewa musamman idan tana tare da anni,duk wata kunya da surukuta anni ta soketa tsakaninsu,sukan zauna su taba hira duk da har yanzu bata iya bude baki sosai tayi magana yadda ya kamata mai tsaho,saidai tana qoqari matuqa wajen ganin ta saba dasu din.
Sati uku da biki ta soma warwarewa sosai,janta a jiki nuna mata ita watace da mu'amala mai kyau shi ya taimaka wajen samuwar wannan sauyin,saidai abu daya da bata jin dadinshi shine yanayin yadda rahama take mu'amalantarta,takan bata girma dai dai gwargwado,hakanan bata shiga sabgar da bata shafeta ba kamar yadda haka halayyarta take tun a gida,saidai duk wani motsi na ayshan a idonta yake kamar wadda aka baiwa gadinta,hakanya sanya itama ta iya takunta take matuqar taka tsantsan da ita.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Parlour din asma'un cike yake da qawayenta na makaranta wanda ta gayyacesu suzo gidanta kwanaki sati hudu da tarewarta,manyan qawayenta ne da take ji da su ko ince a kullum take qoqarin yin abinda zata burgesu su fahimci cewa ita din ba qaramar mace bace,a ranar ta baiwa yarinyar da aka kawo mata a matsayin 'yar aiki qwaya daya 'yat qabilar igbo umarnin ta dafa musu abinci har kala uki,baya ga snacks da lemuka da aka jibge tsakiyar falon,anaci ana kwasar shafta.
Gaba daya hankalinsu yayi gaba babu wadda taji kota lura da shigowarshi,fuskarshi tamke yake bin kowacce da kallo,sai a sannan suka ankara da shigowar tasa,nusaiba itace ta soma masa magana cikin wasa irin na qawar amarya
"Ango kace kana kusa da dawowa ma kenan.....dama kai muke jira ai" maimakon ya sake mata su gaisa kaman yadda suka saba yi a lokacin hidimar biki saitaji yaja tsaki tare da yin gaba ya haye sama,dukansu baki galala suka bishi da kallp har ya gama hawan
"Ke....haka naki mijin kuma yake?" Cewar daya daga cikin qawayen tana riqe da haba cikin mamaki
"Wannan ko anya asma'u?,kinga kallon raini da wulaqancin da yake mana kuwa?"dayar ta kuma fadi
" ni ban gaji wulaqanci ba wlh,oya ku tashi kawai mu wuce"cewar husna babbar qawar asma'un da take ji da ita,sai a sannan da taga suna shirin miqewa asma'u da wani baqinciki ya qumeta da azabar kunya ta magantu
"Babu wannan maganar don Allah kuyi zamanku ina zuwa....yana da fushi ne zai iya yiwuwa a waje aka bata mishi rai bari naje" ta fada da sauri tare da miqewa tayi hanyar stairs ranta na bala'in baci.
Tura qofar dakin tayi,saita sameshi yana tsaye ya kwabe rigarshi saura singlet yana shirin cire dogon wandonshi ta shigo,cikin nuna bacin rai da fusata ta kalleshi
"Haba hamid....ya zaka kunyatani gaban qawayena don Allah?,me suka taba yi maka zaka yi musu wannan wulqancin?,so kake suje gaba su samu abin bada labari?" Bai tankata ba har sai daya cire wandon saura gajeran wando kawai sannan ya dago ya dubeta cikin qanqan da idanu
"Ke,an gaya miki bansan ciwo kudi ba?,ko an gaya miki tsintosu nake?,ohk kin zaci za'a ci gaba da yadda aka saba ko?,toni ba haka nake ba,nasan ciwon kudi nasan mutunci da darajarsu,haka kawai ki taramin garadan qawayenki ki kwaso abinci da abun shan da a qalla zamuyi sati muna ci ki jibge musu don tsabar burga?,to wallahi kiyi gaggawar zuwa ki sallameshi ki kuma kwashemin kayan abincina ki maida store" tsantsar bacin rai da mamaki ne qarara ya bayyana a fuskar asma'u,tana jin ya xama lallai ta nunawa hamid bacin ranta qarara saboda gaba
"Me kake nufi hamid?,qawayen nawa?,to wallahi babu inda zasu,kayan abinci kuma da kake magana ai daga gidanmu aka hadoni da shi ko?" Dawowa yayi da baya maimakon daa da yayi gaba zai shiga wanka
"Haka kika ce?,don an kawo wadan nan matsoyatan kayan abincin kike gaya min haka?,ohk fine....ki gayamin nawa na kashe miki wanda sunyi ninkin baninkin kudin kayan abincin da aka kawo min?,koni na gayawa iyayenko ina da buqatarsu ma?,a matsiyaci kika aureni?,tunda ba zaki iya sallamarsu ba ni zan iya" ya fadi yana nufar qofa,da mamaki ta soma tsaidashi saboda singlet da gajeran wandon dake jikinsa amma ko juyowa baiyi ba bare ya saurareta.
Kaf dinsu saida kowacce ta miqe tsaye a tsorace ganin mijin qawar taso a haka,dubansu yayi sannan ya soma magana
"Kafin na qirga biyar kowacce a cikinku ta kwashi matattun qafafunta tabar min gida tunda yunwa ce ta kawoku,kada wadda ta sake zuwa min gida tasha min koda ruwa ne bare abinci,ku cika cikinku a gidajen ubanku kafin kuxo" cikin bacin rai husna da take jin tafi qargfin wulaqanci ta soma maida masa martani,kanta yayo wanda hakan ya sanya suka qarasa ficewa a guje ba shiri ba tare da sun tsaya daukan kayayyakinsu ba,bayansu yabi cikin daga murya yake baiwa inyamurin mai gadinsu umarni cikin karyayyen turanci
"Maza ka sakar musu karnukan nan su qarasa rakasu" jin abinda yake fada ya sakasu qara mai,taimakon da Allah yayi musu daya motar da suka zo cikinta tana qofar gidan basu shigo da ita ba saboda motocin hamid guda uku dake harabar wajen data asma'u daya data zo da ita ta cike wajen.
A tsaye a falon ya tadda asma'u tana qwallar takaici tare da tunanin anya kan hamid daya kuwa?,lafiyarsa qalau?,kodai ya soma bin hudubar yayyensa mata randa sukazo da sunan sunzo ganin amarya da sukaji suna gaya masa
"Wannan matar taka sai kayi da gaske,makarantarsu daya da nabihat,bata da kirki batason talaka,dagawa gareta da girman kai,hakanan kudinka takeso tosai kayi tsayin daka idan ba haka ba rainaka zatayi wallahi" abu daya ne bata sani ba,hamid mutum ne mai shegen son abun dunuya,yana da dukiya amma ta cinsa ne iya shi kadai,ko sanda yana gida wani abun sai ya rataya a jikin mahaifinsa yayi masa bazai taba qwandala tashi ba,irin yaran nan ne dako.iyayensu basa iya taimakawa banda Allah yasa mahaifin nasa yana da wadata shima,saidai matsalarsa daya mahaifin nasa,mutum ne da bashi da tattali,yana da son nunawa duniya shi wani ne ko nawa zai kashe akan haka zai iya,ya kuma yi nasara don sunansa ya dan fita,sakamakon yadda yake nuna qaryar arziqi don baikai nan ba.
A parlour ya taras da ita zaune tana gunjin kuka,kota kanta baibi ba ya wuce zuwa sama abunshi ya dauki wankanshi.