← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 79 OF 114

Sashe 79

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Idanunta nakan littafin tana bin pages bayan pages tana dubawa,duk rubutun dake cikin littafin yana dauke da kwanan wata da time kowanne rubutu,duk layi daya data karanta mamaki ne yake kamata,bata fahimtar komai saidai rubutun kamar yana bada labari ne kan wani abu daya faru lokaci zuwa wani lokacin,buron hannunshi ya aje ya jingina da kujerar da yake kai gami da hade hannayenshi waje guda,ya lura da yadda ya shiga rudu kadan da mamaki,zuwa yanxu yana ganin ba wani boye boye tsakaninsu,ya kamata tasan su su wayesu duk da bata taba tambayarshi ba,tamkar ma bata damu ta sani ba
"Wanene khalipha?" Ya furta cikin sanyi yana ci gaba da kafeta da idanunsa,da hanzari ta daga kai suka hada idanu,sai taji tambayar tazo mata a banbarakwai,abinda ta jima tana tambayar kanta da kanta kenan,abinda ta jima tana son sani,saidai koda wasa bata taba gigin tambayarsa ko wani nasa ba,saboda tana ganin a matsayin wadda kamar alfarma akayi mata karanta baikai tsaikon ta tambaya din ba,sake dubanshi tayi wannan karon idanunshi nakan biron hannunshi dake jan wasu layuka saman farar takardar dake gabanshi

"Kowanne dan adam yana tare da nashi qalubalen a rayuwa,karki zaci ko tsammaci ke daya kike fadawa matsala ko kika fada,dukkan tsanani yana tare da sauqi haka ubangiji ya fada cikin qur'aninsa" sai yayi shuru yaba ajiyar numfashi,tunaninsa ya luluqa ya koma can baya wasu shekaru da suka shude.

*_muhammad khalipha_*

"Cikakken sunan mahaifinsa shine muhammad sa'id mai goro,haifaffen garin kano dan kasuwa wanda ya shahara da sana'ar saida goro a fadin qasar nan,kusan ya gaji sana'ar ne daga wajen mahaifinsa,wanda yake da mata biyu,uwargidansa ita ta haifa masa yara maza guda biyar ta shidan autarsu mace anty ruqayya,idris shine babba,hamza,habibu,munzali,sai saminu,matarshi ta biyu har ta koma ga Allah yaronta daya wato mahaifina muhammad sa'id,a sannan dukkansu suna ganin babu wani abu da mutum xai iya xama cikin sana'ar saida goro sai duka suka qita,mahaifinsa shiya karbeta hannun biyu ba tare da rainata ba,hakan ya yiwa kakana dadi saboda dama duk cikin yaran sa'id halinshi daban,sai Allah ya sanya yafi qaunarshi,dalili kenan daya saka ya dinga fuskantar qiyayyar 'yan ubanci mai zafi,sai ya tashi a kyare a tsangwame,gashi kome za'ayi masa mahaifiyarsa khadijah da ake kiranta kubra bata daga kai kotace wani abu saboda mutum ce mai tsabar haquri,haka rayuwarshi ta kasance a tsakanin 'yan uwansa,babu wata qauna sai tsabar yan ubanci da nuna banbanci,ruqayya wadda ita ta kasance qanwa gareshi kuma me binsa ita kadai take sonshi,a irin haka Allah ya yiwa mahaifin nasu rasuwa,mahaifin khalipha da innarshi suna gani akayi rabon gadon rashin gaskiya,saidai innarshi bata ce komai ba kamar yadda shima baice ba,suka rungumi abinda aka raba aka basu,sa'id bai zauna ba ya koma kasuwa,wajen abokan arziqi da sukayi zaman lafiya da mahaifinshi masu irin sana'arshi,sanin halayensa na gaskiya da amana,hankali da nutsuwa yasa suka karbeshi yaci gaba da sana'a a qarqashinsu,wato babu maraya sai rago,hakanan babu nakasashshe sai kasashshe,kyau da samartakar sa'id ko daya basu sanya masa girman kai ba ya kama sana'arsa ka'in da na'in,hakan kuwa yayi matuqar taimakawa don nasu raba abincin ci ko suturar sanyawa ba,yayin da a bangaren su hamza kuwa komai ya tsaya cak,rigima ta dinga tashi tsakaninsu,kowa yana ganin shi ya cancanci a baiwa gadonshi dana 'yan uwanshi ya juya,kowa yaja ya kafe kan ra'ayinsa,tilas aka sake gutsuraws kowa aka miqa masa nasa kason,inda mahaifiyarsu daga qarshe ta karbi nata itama dana ruqayya 'yarta,saiyw zamana komai nasu ya soma lalacewa saboda hadin kai,kowa ya tasamma cinye dukiyarsa ba tare da yasan ina tayi ba,hakanan suka dinga fada tsakaninsu kamar zasu yaqi junansu,a haka rayuwa taci gaba da garawa kowanne bangare.

Cikin shekarun da suka biyo baya Allah ya sanyawa dukiyar sa'id da innarshi albarka,yayi kudi mai ban mamaki,yasha fada cewa gaskiya da riqon amana sune ginshiqi kuma matakin nasararsa,sai abu na farko tsoron Allah da kuma bin iyaye,kuma haka yake,duk wani dan adam dake neman cimma wata nasara a rayuwarshi to yayi riqo da wadan nan matakan da taimakon ubangiji zaikai inda yasa gaba.

Zuwa sannan dukka yayyenshi sunyi aurensu,saiya zama babu da talauci ta saukar musu,ci da iyalin na neman ya gagaresu,ruqayya da suke ruqo dalilin mutuwar mahaifiyarsu saita soma passing passing daga hannun wannan zuwa na wancan,a nan ne suka soma rabowa wajenshi,kowa ya soma kwantar dakai dayi masa biyayya kamar zasu kwanta mishi,innar sa'id ita ta umarceshi da kada ya fasa taimakawa kowa a cikinsu ko bayan ranta,to shima mai sauqin raine da haquri,saboda haka sai ya zama shine lalurar duka gidajen nan gida biyar,yayin da sukaci gaba da nuna mishi soyayya da qauna ba don Allah ba,ko sau daya bai taba kawo komai a ran shi mara kyau game dasu ba,haka yaci ga ada taimaka musu har Allah ya kawo rasuwar innarshi,abinda bai sani ba shine a bayan idanunshi murna suka dinga yi da faruwar hakan,suna ganin abu mafi sauqi shine su aikashi lahira su cinye gadonshi,tunda a yanzu baida wani wanda zaici gadonshi tunda ba aure gareshi ba.

Zakaran da Allah ya nufa da cara,suna can suna nasu shirin a sanda Allah ya hada soyayyar sa'id da aishatu buzuwa daga niger,Allah shi yakai sa'id garin ta silar kasuwancinsa suka hadu da ita,soyayya suke da juna tuquru da gaske a lokacin da ayshan tuni yayanta kuma mariqinta ya bada ita ga wani dan uwansu,sam tama mance da wannan batun don bashi takeso ba,ba tsoro ta aika sa'id gaban yayan nata ya gabatar da kansa a wajensa,yayi mamakin yadda aysha ta manta da batun da sukayi da ita,amma ya kauda wannan yayi masa bayanin cewa an bayar da ita,aysha ta sakawa ranta sai sa'id yayan nata ya dage sai wanda ya zaba mata,duk da bata taba fito na fitodashi kan lamarin ba amma duk wanda ya santa yana kallonta yasan tana cikin damuwa,abinci na mata wuyar ci,da yaga dai da gaske take saiya amshi neman aurenta da sa'id yake,amma bisa sharadin idan ta tafi dadi ko wuya karya dawo musu da ita,tace ta amince da hakan,saboda dukka wata nagarta da mace ke nema wajwn mijin aure sa'id nada ita,wanda ko kwatan haka bata gani ba daga wajen wanda yayan nata ya zaba mata ba,duk da yake dan uwanta amma tasan yana da raunin nagarta,akan wannan sharadin akayi aurensu,ya daukota daga nijer zuwa nigeria,yayi mata dukkan wani gata,ya riqe anni da kyau cikin qauna da soyayya da kuma kulawa da juna,itama ta riqeshi da irin biyayyar nan da akasan matan aure nada dashi.
[26/02, 8:54 PM] +234 810 044 6653: 43

Soyayya suke gudanarwa mai kyau da tsafta,ya karbo ruqayya daga hannun 'yan uwanta ya dawo ma da anni ita,hakan ya yiwa anni da bata da kowa dadi,saitake kallon ruqayya a matsayin 'yar uwa,suna zamansu lafiya,yayin da daga gefe guda 'yan uwan sa'id nacin dunduniyarshi duk da cewa shine komai nasu,cinsu,shansu,suturarsu,karatun yaransu,kuka da lafiyarsu da sauransu duk yana wuyanshi,haihuwar farko anni ta haifi muhammad khalipha,nan fa hankulansu suka sake tashi saboda suna ganin sun rasa damarsu,tunda har ya haifi da namiji tasu ta qare,suna ji suna gani suka haqura,suka ci gaba da tatsarshi da tatsar dukiyarshi ta hanyoyi daban daban,yaki halal yaki haram,haihuwa ta biyu anni ta samu mace,ruqayya nata murna ta samu 'yar uwa amma ana yayeta ta rasu,a haihuwa ta uku ma sai aka sake samun namiji haka ta hudu,sai ata biyar Allah ya kawo hajar.......,har a sannan daga dangin anni ba wanda ya nemeta,ita kuwa kullum zancansu na cikin bakinta,saidai tasan bata isa ta matsa kusa da inda suke ba saboda sun mata sharadi tun farko.

Dukkan wani qauna tattali da soyayya tamu tana kan hajar mu duka baki dayanmu,kasancewarta auta kuma mace a cikinmu,hatta da anni na qaunar hajar,yarinyar hallayyarta daban take,tana da haquri,sanyin hali shuru shuru da rashin surutu tun tana qaramarta,tana da biyayya bata da rashin kunya sam.

Hajar nada shekara goma aka aurar da anty ruqayya,mijinta ma'aikacin gwamnatin tarayya ne,tu a alokaci. Gwamnati na tura ma'aikatanta qarin karatu qasashen waje aka turashi ya dauki ruqayya suka tafi,wata hudu da tafiyarsu babban tashin hankali ya samu iyalin muhammad sa'id mai goro,Allah ya daukeshi sakamakon jinya da yayi wadda batagi ta wata guda ba,tashin hankalin da matarsa da iyalansa suka shiga a sannan bazaiyiwu baki ya musaltashi ba,da qyar aka samu kan iyalin nasa saboda kowa a cikinsu a dimauce yake,ruqayya batasan da wannan ba sam saboda a lokacin wayar tafi da gidanka bata yawaita ba ba'asan number ko layin da za'a sami mijinta a sanar masa ba.

Ba yadda bawa ya iya da hukuncin Allah,haka daga bisani suka haqura suka dauki dangana.

Kwana uku kacal 'yan uwan alhj sa'id suka soma zirya kan dukiyarsa da abinda ya bari,yau suce a bada muqullin kaza,gobe suce meye password na safe dinshi,jibi suce a bada muqullin mota,gata suce ina takaddun kaza,a lokacin anni da kallo kawai take binsu,kasancewar har yau batayi normal ba,saboda mutuwar tayi mata duka bana wasa ba,alhj sa'id shine gatanta uwa kuma uba a gareta,ko mutuwar iyayenta bata shiga wannan yanayin ba saboda a sannan bata da wani shekaru duka duka bata wuce shekara uku a duniya ba,haka suka dinga karbar abubuwa d'ai d'ai da d'ai d'ai ba tare data ce musu komai ba,uwa uba bata da kowa bare yace zai tsaya mata,khalipha da yake shine babba a sannan bazai wuce shekara goma sha shida ba,duk da haka yaso tasowa da nuna rashin amincewarsa kan abinda ke faruwa,to amma qarancin shekaru da kuma duk sanda ya doshi anni da maganar maimakon ta bashi hadin kai sai kawai ta saka kuka,tana ganin kamar ta dukiya kawai suke bayan wanda suka rasa yafi dukiyar da duk abinda ke cikinta,hakan yasa ya janye ba mataimaki babu mai qwarara masa gwiwa.
Chapter 79 · 0% Book details