← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 114

Sashe 54

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon farko wajen ya burgeta sosai,komai a tsare a tsaftace kamar sashen mace,qamshi yake fiddawa sosai da alama qamshin ya kama wajen,babban parlour wanda ke tsare da kujeru blue black,rugs da curtains dun falon duka kalarsu kenan,sai kayan kallo daga gefe daya wanda aka musu bango gudada yasha ado mai daukan hankali,daga kowanne kusurwa na falon manyan hotunan khalipha ne window size kaman zaiyi magana,wanda suka fitar da ainihin halittar da Allah yayi masa,kowanne hoto akwai murmushi kan fuskarshi,akwai dakuna guda uku,daya bedroom ne biyun suna rufe batasan ko meye a cikinsu ba,saidai dayan dakin study room ne da wanda ya maidashi kaman qaramin office dinshi na gida wanda aka daga bayanshi aka yiwa wata qofa ta glass da zaka iya habgo bayan gidan dake cike da shuke shuke,isaka mai kyau takam shigo masa shi yasa yake jin dadin zaman wajen sosai,dayan kuma ya barshi ne a dakinsa na motsa jiki wanda shima yana da wata qofae daban bayan ta cikin falon.

Dubanta yayi har yanzu fuskatta na qunshe yace mata
"Ga guri ki xauna....." Soma takawa tayi a hankali wanda ada tana tsaye daga bakin qofar falon,cikin rashin sani santsin door mat din dake bakin qofar ya debeta
"Subhanallahi" ya fada da sauri,Allah ya taqata ta dafe qofar qirjinta na bugawa,tsayawa yayi cak sannan ya sake dubanta
"Ki cire wannan lullubin haka....ni wanki ne ba wani abu ba" ya fada ranshi daya
"Me dame kike buqatar a dauko miki a can gidan?" Ya tambayeta yana jin banbarakwai don bai saba hada daki da kowa ba bare mace bayan ta zauna kan daya daga cikin kujerun
"Kayan sawa na suna nan cikin akwati"
"Kawai?" Ya sake tambayarta,kai ta kada masa sai ya juya ya fice,dai dai sanda mai aikin ta sako kai da kayan abincin,cak ta tsaya ta duqar da kanta cikin girmamawa ba tare da tace komai ba,hannu ya sa ya karbi farantin daga hannunta ta juya ta koma dama tasan dokar ba'a shiga mishi bangare.

Da sallama ya sake shiga ta amsa tana dubanshi,sai suka hada ido,ta sake jan mayafin nata gaba kadan,tabe baki yayi cikin ranshi yana fadin
"Sai wani faman rufe fuska kaman mara gaskiya,ko tana tunanin ina kallonta ne?" Itako cikin ranta cewa take
"Me yasa yakemin hidima da kanshi" ta fadi haka ne saboda matsayin data lura yana da shi,saman dan teburin dake daura da ita ya dora farantin sannan ya juya ya fice.

Sashen anni ya koma,tana zaune yanzun saman kujerar falo,dubanshi tayi
"Sai ina kuma?,zama ya kamata kayi khalipha sosai da ita har ta sake damu,na lura tana da baqunta sosai"agogonshi ya duba sannan yace
"Ba abinda aka taho dashi daga can gidan anni,dole naje naga me za'a dauko din kafin agama gyaran nan,sannan kuma ma ina da baqo.....na masa alqawarin zamu hadu yau,ina zaton kin sanshi abokin hudar abba ne tun yana raye....saidai kaman yaro yake a wajenshi,so sun saba tun a sannan abba na ara mishi kudade daga bisani ya maidowa abba da kudinsa idan ya juya an samu riba,to yanaso ne yanzun yaci gaba da wannan mu'amalar da ni,ina da dan alamun tambaya ne akan kasuwancin nashi,sannan ina tantama kan yiwuwar harkar tamu da shi saboda yanayin yadda na lura da rashin iya tattalinsa,da kuma rashin qwarewarsa wajen juya kudi gaskiya akwai matsala"ajiyar zuciya anni ta sauke
"Tunda har yana hurda da mahaifinka a baya bai kamata ka hanashi ba,abinda zakayi shine ka bashi a matsayin gwaji...sai kaga me zai biyo baya ko?" Kai ya gyada
"Haka ne anni....sai aci gaba da yi mana addu'a"
"In sha Allah....Allah yayi jagora"
"Amin" ya amsa sannan sukayi sallama ya fice.

Ruwan tea kawai ta iya sha cikin kayan da aka kawo din don ba kasafai ta fiye ciye ciye ba,hakanan ma ita sam yau bata jin yunwa,da haka ta hade kayan waje guda ta jingina da kujerar,zuciyarta da gangar jikinta najin gajiya na sauka kadan kadan daga jikinta,idanunta na gilmawa cikin falon tana yaba tsarinsa da kyansa,kwata kwata baiyi kama da falon namiji ba,da daya da daya tana kallon komai har idanunta ya sauka kan hoton khalipha wanda yake opposite dinta.

Yana sanye da kufta ruwan hanta,da hula dara da rufaffen takalmi,yayi murmushi sosai yana kallon kyamarar ya daga hannun damanshi sama kaman yana yiwa wani bye bye,sosai take kallon hoton tana qarewa khaliphan kallo,karo na farko data taba tsayawa ta kalleshi tun daga kanshi zuwa qafa
"Fatabarakallahu ahsanul khaliqin" ta furta a ranta,sai yanxu ta yadda da zancan aliya data ke gaya mata khalipha mai kyau ne,irin kyan da ba kasafai ake samun maza da shi ba,banda yau da zata iya rantsewa shacu fadin aliya ne tunda bata taba tsayawa ta kalleshi haka ba,a karan kanta taji tana jaddawa dawa kanta tayi iyakar iyawarta wajen tsayawa a matsayin qanwarsa,tabbas koba dade koba jima matar khalipha na tafe.

Daga wannan tunaninta ya gangaro kan mahaifiyarta,tunanin da rana bata fitowa ta fadi ba tare data yishi ba sau babu adadi,a hankali take nazarin labarin da gwaggo asabe ta bata,tana tuna duk wata kalma guda daya ta cikin labarin bata bari ta subuece mata ba,umminta tayi nisa,nisan da ba'ajin kira,abun ya ratsata shekarun da aka dauka ba wasa bane,wa zata kama?,wa zai taimaketa,wa zai taimaka mata ta dawo da umminta hayyacinta?,a qalla a yanzu ta samu sauqin wasu abubuwan ta wasu fannin,tunda har gashi dangin ummin da dangin mahaifinta suka iya tarayya waje guda lokacin bikinta,abinda iya zamanta bata taba gani ba,kusan yanzu babbar matsalarta shine yadda zata farkar da ummin nata,yadda zata samu soyayyar uwa kamar kowanne d'a
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil,wa ufawwidu amri ilallah,innallaha basirun bil ibaad" ta shiga maimaitawa sau babu adadi kan Allah ya kawo mata dauki,a haka bacci yazo yayi awon gaba da ita.

Bata tashi farkawa ba sai dai dai lokacin sallar azahar,duka sai take jin wani iri babu dadi jikinta saboda bata saba zaman dabe ba haka ba a gida,toilet ta laluba a nan parlourn ta daura alwala ta tada sallah.

Daga can wajen anni kuwa duka hankalinta na wajen aysha har sanda aka kammala abincin rana,da kanta tasa aka shirya komai tacewa mai aikinta ta dauka ta kai mata,karba amal tayi ta wuce da shi don tana son sake tabbatarwa da kanta haka ayshan take?

Tana shirin fita daga kitchen din haidar ya shigo,baya ta danja kadan ya samu ya shigo din saboda tasan halinshi sarai,haka nan yaqi jininsu batasan dalili ba,saidai dalilin kusa yayi shige dana khalipha ne,a sanda dukkan abinda ke faruwar ya farun haidar nada dan sauran wayo,yana tuna wasu abubuwa daga ciki,yana da zuciya sosai shi yasa shima ya kasa mantawa,dalili kenan ma da sukaqi zaman gidan gaba daya da aka tashi hidimar bikin,suka koma gidan wani abokinsu shi da mus'ab dake bayan layinsu.

A ladabce kaman yadda suka saba ya gaida anni
"Ina mus'ab ne?,ai an gana bikin sai ku dawo gida hakanan ko?"
"Yau in sha Allahu....munyi missing dinki anni..." Murmushi kawai tayi tana dubanshi sanda yake duba abinda aka dafa,donshi ba daga nan ba wajen son abinci musamman mai dadi,kusan halayensa suna mata kamanceceniya dana khalipha.

Sanda ta shiga tana zaune saman abun sallah data samu kan hannun kujera,da murmushi kan fuskar ayshan ta amsa mata sallamar,amal din ta qaraso ciki idonta na kan ayshan wadda,ranta yacu gaba da suya irin na kishi gami da fargaba,lallai adazune ma bata kalleta sosai ba qila saboda kada wani ya gano kallon qurillar da take mata
"Ya bakici komai ba?" Amal din ta fada tana bubbuda abincin,murmushi ta sakeyi
"Naci mana"bata sake cewa komai ba don bata jin zata iya sake cewa din ta aje mata wancan kwandon ta dauki dayan ta fice,sai ayshan ta bita da kallo saboda ta fuskanci kaman ta dan sauya,gabanta ya fadi taji babu dadi a ranta,wataqila taji rashin dadi ne saboda bata ci wani abu ba a dazun,ita kuma taci iyakar cikinta kenan,bazata so ta soma bata musu ba daga kwana daya tak cikin gidan,saboda haka ta sauko ta zuba abincin cikin plate,ita kanta tasan ba zata iya cinyewa ba amma haka ta dinga cusawa har sai data ji tana son yiwa kanta illa sannan ta rufe.

Ba dadi haka cikinta yayi mata,hakan ya saka ta tashi ta soma dan kade kade a falon da goge ko zai zazzage,abinka da wadda ta saba sai kawai ta zarce da shara,ta gyara falon sosai duk da ba'a hargitse yake ba,amma komai nason gyara take ya sake kyau da qyalli,sanda ta gama uku ta gota,sai ta sake alwala ta kuma zama tana jiran sallar la'asar,ita irin wannan zaman sam bata saba da shi ba,shi yasa take jinta kamar cikin kurkuku.

_Ya Allah ka rabamu da sharrin mutum da aljan_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*KO KUMA*
07067124863

*DB*

31

Ana gama sallar la'asar mai aikin anni tayi knocking qofar,bata tambayi waye ba don tasan koma waye dan cikin gidan ne
"Anty....anni tace in duba mata lafiyarki" murmushi tayi tana jin dadi har cikin ranta,ganin ta sake samun dadin masoya a fadin duniya
"Lafiya lau...ko zaki yimin jagora na koma ciki?"
"Babu damuwa" itama ta amsa sauqin kan aysha na burgeta,takalmanta kawai ta zira ta maida qofar ta rufe kamar yadda ta sameta tabi bayan mai aikin suka jera
"Anty meye sunanki ne na gaskiya"
"Aisha sunana....zanfi jin dadi idan kika kirani da shi" bako ta kama sannan tace
"Wane mutum...uwar masu gida ce fa,ni na soma sunan anni kenan ai" murmushi aysha tayi har cikin ranta taji dadi,haka suka ci gaba da takawa raliya na sakowa ayshan hira jifa jifa.
Chapter 54 · 0% Book details