← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 114

Sashe 90

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali ya sauke gilashin motar,qamshin turarensa da sanyin ac dake motar ya soma busowa zuwa waje,wanda hakam shi ya dauki hankalinta,qamshin turaren da take tunanin kamar ta sanshi,a hankali ta waiwayo zuwa sashen da take jin qamshin,idanunta suja sauka cikin nashi,faduwar gabar nan da'a koda yaushe takanji idan ta ganshi ita ta soma ziyartarta,sai kuma mamakin abinda ya kawoshi makarantar,duk ta watsar da wannan cikin sakanni ta sakar masa murmushi bisa shawarar zuciyarta,saita soma takowa a hankali zuwa bakin motar
"Sannu da zuwa" ta furta cikin nuna girmamawa,shima martanin murmushin ya maida mata yana mata nuni data zagayo cikin motar,ba musu ta zagaya daya bangaren ta shiga,saidai tabar murfin motar a bude,tuni drivern dama ya koma can wajen sa saura sukayi parking ya zauna a cikinsu.

Wani yanayi ne ya dinga ratsasu dukkansu tsahon mintuna ashirin kafin ya bude wani waje dage sit din gabanshi ya ciro laptop ya aje a tsakiyarsu
"Yau da daddare zamu tashi in sha Allah.....ga wannan kiyi amfani da ita a madadin waccar" sosai system din ta burgeta,da alama rahamalls sun iya kawo kaya masu kyau da inganci,don wannan tafi waccar tata kyau da tsada nesa ba kusa ba ko a ido ma
"Akwai abubuwa na akan waccan ina sonta na saba....."
"Shshshsh..." Ya fada yana dora yatsanshi kan lebanshi idonsa cikin nata
"Waccan haidar ne ya siya miki bana buqatar kuma ki amfani da ita,ni khalipha nine a haqqu da komai naki,so da wannan nakeso ki amfani,duk wani naki mai.muhimmanci na cire daga kai an dawo miki dashi nan,karma ki sake maganarta don already na riga na bayar da ita" hannu ta sanya ta dauka,bai cancanci musu ba sam sannan tace
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi ya qara budi"
"Ameen" ya amsa yana lumshe idanunsa
"Ban amince kuma naga hoton kowa ba akai" saita daga kai tana dubanshi,sam ta mace hoton haidar ne akan screen din waccar,to me kenan?
"Uhmm,zan wuce me zan samu?" Ya fada idanunsa cikin nata,
"Ba komai" ta fada tana murmushi
"Shikenan" ya fada yana daga kafada duk da bai daina kallonta ba,saita motsa kadan ta fidda qafafunta waje sannan tace
"Allah ya tsare hanya ya bada sa'a" sam kasa amsa mata yayi ba,bayason ta wuce,bayason ta tafi,hannunta ya riqo cikin xafin nama da hanzari ganin da gaske ficewar zatayi,sannan ya miqa hannunshi ya rufe murfin motar,fuskarta ya sanya a cikin tafin hannunshi ya hada tsinin hancinsa da nata,cikin sakanni kadan ya kashe mata jiki gaba daya,a hankali cikin muryar dako cikin motar kake baka isa kaji me yake cewa ba yace da ita
"Ba haka nake buqata ba,sallama nakeso irinta masoya,so nake naji ya suke ji duk lokacin da rabuwa tazo....." Idanunta ta runtse gam,wani nauyi na sauka cikin zuciyarta da gangar jikinta ma gaba daya,gaba daya ya gama saukar mata da kasala,bugun qirjinta ya dadu wanda yasanya numfashinta shima sake gudu wajen fita,qamshin lemon dake fitowa daga bakinsa yana ratsa hancinta wanda ya gauraya da turarensa,tattausan lebanta dake gogar nashi ya sanyashi kama leban nata da haqoransa yadan ciza kadan ta yadd ba zata ji zafi ba.

Knocking din qofar da akayi shi ya sanyashi sakin fuskar tata da yayiwa ruqon tsauri,kowannensu ya janye a hankali,ta bangaren aysha ake knocing din saboda haka ta juya ta dannan madannin sauke glass,gilasan suka sauka qasa,hanan ce a tsaye rungume da litattafanta
"Ina can ina bulayin nemanki,keys din daki zaki bani ban fita da nawa ba mmn hunaifa na bari a dakin"
"Ohkey" ta fada cikin sanyi tana yunqurin lalubo maqullin da tuni ya subuce qasan kujerun motar,dagowa tayi ta miqa mata idanun hanan din na kanta,kana kallon fuskarta kasan dariya take hadiyewa,kallon na kamaki ba yadda zakuyi takewa ayshan itama ta fuskanci me take nufi,saboda haka saita waiwaya sashen da khalipha ke zaune cikin sanyi tace
"Meet hanan,my roommate" cikin fara'a hanan din ta gaida khaliphan,shima a sake ya amsa mata yana tambayarta karatu tace komai lafiya
"Ranka ya dade aikinka na kyau fa,saidai a dan sassauta mata karta gagara hada masters din tata" da sauri ayshan ta kalli hanan dake dariya,maganar tata saita baiwa khalipha dariya,can cikin ranshi kuma yana mamaki kan lafazin hanan din,idanu ya kafe aysha dashi
"Wai haka humairaaah?"kunya ta mata dabaibayi sosai,tana kada kai kamar zatayi kuka tace
"Tsokana ce kawai takeyi,batasan waye kai a wajena bane" dariya sukayi hanan din da khalipha,sannan tayi sallama dasu ta wuce
"Waye ni a wajenki?" Ya jefo mata tambayar data rasa amsar daya dace ta bashi
"Matsayin daka dade da baiwa kanka"
"A yanzun idan na sauya matsayin zuwa mataki na gaba yayi dai dai?" Shuru tayi tana nazarin maganarsa,kalma ce mai harshen damo dake da buqatar nazari,hannunta taji ya kama ya sumbata na tsahon sakan goma sannan ya sake mata hannu
"Zan wuce,ki kula da kanki" sai a sannan itama taji wani iri babu dadi,addu'a tayi masa sosai sannan ta zira qafarta ta fito daga motar,harta rufe idanunsu nakan nakan na juna duk da kunyar abinda ya mata dazu dake addabarta
"Baki bani komai ba da zan dinga tunawa dashi" sadda kanta tayi tana murmushi qasan ranta,tome yakeso ta bashi?" Bata gama wannan tunanin ba ta jiyo muryarshi mai taushi
"Allah ya bamu alkhairi,saina dawo"
"Ameen" ta furta,saita kasa tafiya taci gaba da tsaiwa a wajen har ya ryfe gilasan motar ta daga tabar wajen,shi dinma ta cikin mirrow yaci gaba da kallonta har suka bacewa ganin juna.
*_Mutane masu son zuciya ma sunada rana a gareka, koba komai zasu tara maka ladansu ka karɓa a ranar da kowa ke fafutukar neman ƙari a littafin ayyukansa. Dan haka karkai baƙin ciki da zaluncin azzalumi, koda ɓatanci yay maka bisa son zuciya ribace a gareka, shi ko bai gane faɗuwace a garesa sai randa babu wata ƙofa ko damar da zai roƙi gafarar ka._*

49

Tana tsaye tamkar jiran shigowar ayshan take,koda yake hakanne ma,dafeta tayi tana dan ihu,wanda hakan ya sanya zubewarsu saman gadon maman hunaifa,qoqarin qwace kanta aysha take
"Hanan....hanan what r u doing ne?,pls" sai data gama ihunta sannan ta saki qaramar dariya
"Wallahi banga laifinki ba,wannan halitta haka aysha dole ki susuce ki sauya lokaci daya,wallahi kunyi masiiiiifar dacewa,hadin ya hadu wallahi" dubanta aysha take tana hadiye dariyarta,yayin da a zahiri tadan hade gira
"Wai....akanme kike magana ne?dawa muka dace?"
"Ban sani ba 'yar gaba da rainin hankali,kinsan Allah gulmarku kawai ke tashi a varender dana hau,ina can nemanki wajajen department dinku ina zuwa nan nace ke nake nema aka nunan inda kike,kaiiii aysha ashe ba banza ba kike figawa maza dawa ashe ke kin gama gwangwajewa abinki,kai ma sha Allah wallahi d'an d'ashi,dole mmn hunaifa tasha wannan labarin" ta lura idan bada gaske tayi ba hanan zata mata kwaroroto,kusan halinsu daya da aliya,banbancin dan kadan ne
"Wai da kiketa wannan surutun ce miki nayi saurayina ne?,toki rage zumudi wanda dai kika gani yaya na ne,kuma ga abinda yazo kawomin nan" ta fada tana nuna laptop din data aje kan dan teburin da take dora littafanta tayi karatu,dariya sosai hanan ta saki bayan fa kalli system din harda tafa hannu sannan ta samu gefan ayshan ta zauna,hannunta ta dora kan kafadarta
"A qalla na doshi shekara takwas ko bakwai ina soyayya,kin manta wace ce hanan?,to bari kiji wannan tatsuniyar taki bata samu wajen shiga ba,ko wanda ya fara soyayya yau kallo daya zai muku yasan cewa ba qaramin narkewa kukayi cikin son junanku ba,idan ma ba saurayinki bane bari na gaya miki ku binciki kanku,don ba shakka dukkaninku kuna yiwa junanku soyayya mai zafi,idanunku kawai sun isa su gayawa koma waye haka,saidai wataqila kun afka son junanku ba tare dakun sani ba,ko kuna daga cikin masu qaryata cewa sun fara son waninsu" idanu aysha kawai tasa tana kallon hanan gami da yunqurin faffasa maganar cikin kwanyarta,wanne ne a ciki?,wanne ne ba wanne ba?.

"Wa akewa irin wannan sharhin haka?" Mmn hunaifa dake shigowa ta fada bayan ta zauna saman gadon aysha
"Kinzo a dai dai,wallahi yarinyar nan ba banza ba taqi ayi mata maganar kowa,mmn hunaifa kinga guy dinta kuwa?,hasbunallahu wa ni'imal wakil,wannan shi ake kira da komai yaji,kinga wata iriyar soyayya da ake bugawa mai sanyi" ai aysha batasan ta durmawa hanan dundu ba tana fadin
"Zubaida....mmn hunaifa karki yarda da sharrinta
" a'ah nima fa dana shigo daga waje na danji ana qushin qushin,ko maganar ce?"
"Itace daiiii mamn hunaifa,hostel din nan duka ya dauka" ganin yadda hanan ke faman zubawa mmn hunaifa lbr kawai saita barta ta miqe ta cire rolling din kanta ta daurashi a matsayin dan kwali ta hau dora musu girki,don shaf ta mance ma tana jin yunwa sai yanzu,tana aikin amma tunanin maganganun hanan ke mata yawo a ka,da gaske idanunsu na bayyana soyayya kamar yadda hanan din tace?,to wai shin yama soyayyar take bare har ta ganeta,kalma daya da bata santa ba a rayuwarta wato soyayya.

A bun mamaki a daren saita kasa barci,tayita juyi tana tuna zuwan khalipha a yammacin dazu,duk wani motsai daya faru tsakaninsu sai data tunashi kar a kanta,miqewa tayi daga kwancen ta janyo syatem din daya kawo mata ta kunnata.

Hotonta ne ya mamaye screen din,wanda batasan inda ya samu hoton ba,hakanan ba zata iya tuna sanda aka dauki hoton ba,a nutse ta dinga shiga ma'ajiyar adana hotuna,hotunanshi zallah a ciki wadanda yayi masifar kyau kamar a kirashi ya amsa,ya rabata da duk wani hoto na haidar sai nashi zalla me kenan?,
"Kishi" zuciyarta ta bata amsa,kanta ta kada tana qaryata hasashen zuciyar taya,kishi ana yinsa ne ga abinda akeso ai,yaushe khalipha yace yana sonta ma da har zata zaci ganin kishi a qwayar idanunsa?,amma sone kawai yake haufar da kishi aiko?,zuciyarta ta jeho mata tambayar,saita ture gaba daya tunanin gefe guda.
Chapter 90 · 0% Book details