Sashe 39
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Harararta da aysha tayi yasa ta dauke kanta gefe guda tana dariyarta hankali kwance
"Kai.." Aliya ta fada lokaci daya dariyarta tana daukewa,saita waiwayo ta dubi aysha
"Aysha.....kaman angonki fa na gani hakimce cikin motocin can" ta fada tana nuna mata motoci ukun da suka wuce a jere iri daya,bin motocin tayi da kallo kafin ta maida idonta kan aliya tana murmushi
"Dama kina gulmar wata ba dole idonki ya dinga miki gano miki abinda ba haka ba....mutumin da muka rabu da shi yanzu yanzu a gida"
"Allah seriouse aysha shi na gani...don har mun hada idanu sai naga ya dage glass din motar" wannan karon sai da aysha tayi 'yar qaramar dariya
"Idan shi kika gani yaushe ya zama haka?...yaushe ya sayi dukkan wadan nan motocin yanzu yanzu kenan daga fitowarsa daga gidanmu ko?,may be shi da oganshi ne,don kusan ko yaushe yana gaya min suna tare" Ja aliya tayi ta tsaya,yanayinta ya koma da gaske take irin yanayin da tasan ayshan zata fahimceta
"Wallahi Allah da gaske nake miki aysha khalipha na gani a cikin motocin can,kuma alamu duka sun nuna cewa ba wani yake ja ba shi ake ja motarshi ce,kayan jikinsa fa ba irin wanda muka ganshi da su bane yanzu" shiru dukka sukayi aliya na kallon aysha cikin tantama,yayin da aysha ta soma shiga tunani gami da shakka,ajiyar zuciya aliya ta saki sannan tace
"Allah aysha tun asali sam khalipha baiyimin kama da wanda ke cikin babu ko yake samu a qarqashin wani ba....kin taba qare masa kallo da kyau kuwa tun daga kanshi har zuwa tafin qafa?" Dariya ce ta kubcewa aysha duk da yanayin fargaba data soma shiga
"Aliya ta yaya zan iya kallon wani namiji haka tun daga kansa zuwa qafa koda kuwa mijina ne?" Idanu aliya ta zaro
"Mijinki?...kina nufin ba zaki iya masa wannan kallon ba....lallai aysha akwai aiki a gabanki" qaramin murmushi ta saka tana kada kai
"Muje don Allah....shi din talaka ne kamata hakan shi ya qara min qwarin gwiwar amincewa zama da shi....ba da sunan miji ba...da sunan yaya dan uwa...'yan uwan da na rasa nake fata wannan karon nayi gam da katar da su kuma managarta,bana jin akwai wani ha'inci ko qarya tsakanina da shi"
"Idan kuma abinda idanuna suka gani gaske ne kinga shikenan...shikenan kaya sun tsinke a gindin kaba" aliya ta fada tana dariya
"U r mad aliya...ba don wannan zan zauna da shi ba...na amince ne saboda naga irina ne shi,kaman yanayin rayuwarmu daya ne...idan kuma har da gasken ne....bazan iya shiga cikinsu ba na zauna,ban masa qarya ba ban boye masa komai nawa ba,ban boye masa wacece ni" dukan kafadarta aliya tayi tace
"Shutup my friend....bana son wannan maganar taki ma...muje don Allah" daga haka suka ci gaba da takawa ba tare da sun sake bi ta kan maganar ba.
Numfashi ya sauke gami da lumshe bayan sun wucewa ganinsu aliya,yana sane ya sha mur ya dauke kai gamida dagr glass din sama don tayi tsammanin cewa bashi bane idanunsa ya bude sannan yace
"Jibril"
"Na'am sir"
"Daga yau bana son a sake saukemin glass din mota qasa idan bani na bada umarni ba"
"Yes sir,in sha Allahu" daga haka motar ta dauki shiru,addu'a yake cikin ranshi Allah yasa basu ganeshi ba,don ba yanzu ya shirya bayyanar komai ba.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Biki saura kwanaki uku gidan mommy ya soma cika da jama'a 'yan uwa da abokan arziqi,kowa zancan bikin asma'u kawai yake,da yawansu ma basusan cewa itama aysha nata auren za'ayi ba,idan sun tambaya ma takan ce a can qauyen iyayenta za'ayi,eh haka ne ayshan take cewa,don itama ta matsu ta wuce qauyen nasu,ko banza naka naka ne.
Cikin kwanakin zuwa gyaran jikin sai ya soma yi mata wahala saboda hidimar baqin dake gidan,awanninta kaso mafi yawa a kitchen take yinsu,duk da itama hakan ya mata dadi don bata ga meye na wani yin gyaran jiki ba,hakan kamar wani rawar kaine a wajenta ko wuce gona da iri,don haka sai take noqewa take fakewa da cewa gidan cike yake da baqi,hakan ya fusata aliya kan zasu maidata 'yar aikinsu,ta dage kan sai ta tattara kayanta ta dawo gidansu,da qyar ta shawo kanta ta nuna mata ranat juma'a ma zasu wuce takai baki daya tunda asabar ne daurin auren.
Tun ranar laraba aka fara gudanar da bikin,gidan kuwa ya cika ya tumbatsa da 'yan uwa da hamshaqan qawayen asma'u,tun ranar ta soma shiga ta kece raini,bridal shower suka fara yi sannan sauran events din suka biyo baya,ayshan kam mafi yawan lokaci idan bata tana kitchen ko dakinta,don data je gyaran jikin da aliya ta tilastata take dawowa,yawanci da aliyan suke zuwa,saidai ita bata shigowa gidan tunda aka fata bikin a qofar gida suke rabowa ta koma ta wuce nasu gidan.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*KO KUMA*
(07067124863)
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
24
Ranar laraba da safen mommy ta kirata dakinta,sanda ta shiga akwai qannen mummyn a ciki da wasu daga cikin 'yan uwanta zazzaune,wasu a gefan gado wasu saman tiles,binta sukayi da kallo sannan suka soma qus qus a tsakaninsu,hakanan jikinta ya bata da ita suke duk da bata iya jin me suke fada amma jikinta ya bata,tana iya jin sautin dariya dariya qasa qasa daga bakunan wasu daga cikin 'yammatan dake cikin dakin,saidai batasan meye abin dariyar ba,jikinta dai atamfa ce riga da zani sai hijabi data dora iya gwiwa kanta babu dankwali,sai tudun gashinta dake matse a cikin ribbom.
A ladabce ta tsugunna a bayan mummy wadda ke gaban wardrobe tana fidda kayan da zata sanya anjima,ba tare data waiwayo ba tace
"Gobe wasu daga 'yan uwanki zasu zo daga qauye,za'a je ayi miki jere....ya kamata ki sanar da shi zuwan nasu,ya bayar da muqullin gidan ko ya rakasu,don ba lallai su su sake gane hanyar gida ba bare gidan kanshi"
"Kawai mummy ya rakamun" inji nusaiba qawar asma'u tayi caraf ta fada,cikin muryarta kana iya jiyo sautin dariyar dakeson fitowa,nusaiban 'yace ga yayar mummyn,qawancensu yayi daidai saboda hali da yazo daya,tana son harkar girma itama,tana son fantamawa,tana son kuma mu'amala da masu hannu da shuni
"Ko yazo ko ya samo wanda xai rakaku...don ko su halima sunce ma ba zasu iya gane hanyar gidan ba" dariya nusaiba ta sake da alama tasan komai ko an bata labari,sai ta kuma waske tana wa farida cousin dinta dake zaune kusa da ita magana
"Toh mummy" ta fada tana miqewa jiki a salube,tana qirga iya kwanakin daya rage zata sake shiga wata sabuwar rayuwar,ko ya zata kaya da ita ita kuma?.
Zata fice sukayi clashing da naana,qawa ce ga asma'u,amma ta zama kamar 'yar gida saboda yadda ake buga qawance,duban juna sukayi naana ta saki dariya,abinda tsahon sanin da aysha tayi mata bata taba yi mata ba,face kallon banza da kallon raini dake shiga tsakaninsu,saboda asma'u ta riga ta gama dorasu kan turba
"Amarya amarya" naanan ta fada,kallo daya aysha tayi mata ta dauke kanta ta wuce,karon farko da hawaye taji sun cika idanunta,karon farko data ji damuwa ta sosa zuciyarta,gefan gadonta ta zauna,tana qoqarin tsaida hawayen,saidai bata da wannan ikon,saboda zuciyarta na buqatar rage nauyin da ta jima tana dauka,cikin muryar kuka ita kadai cikin daki take cewa
"Ya Allah...kaine mafi jin qan masu jin qai...kaine mafi tausayin masu tausayi...kaine mai tallafar raunana...ya Allah...ka fini sanin wace ce ni...ka fini sanin dalilinka na sanya rayuwata a wannan bigiren,ka fini sani gobe da jibina har zuwa qarshe na,Allah kai kace mu roqeka zaka amsa mana,ya Allah....kayi ruqo da hannayena...ka yiwa rayuwa ta jagoranci...Allah karka barni dai dai da qiftawar ido ya Allah...." Ta qarashe addu'ar tana fashewa da kuka wanda ya tilastata cusa kanta cikin fulalluka don gudun fitowar sautin kukan nata.
Ta jima tana kokawa ita kadai....ta dade tana fitar da ruwan hawaye kafin ta lallashi zuciyarta.
Qarfe shida na yammaci sanda 'yammatan amarya ke shirye shiryen zuwa bridal shower aka ce mata ta fito ga 'yan uwanta nan daga takai,gabanta na dukan uku uku ta zira hijabinta ta tako zuwa falon gidan inda aka aje su don bana ce aka saukesu ba,duba da yadda yawanci mutanenmu na birni ke raina mutanen karkakara,bayan mutane ne da Allah ya musu baiwa iri daban daban masu tarin yawa fiye da mu din,fargabarta na su waye suka zo?,yaya zasu zauna da su a muhalli guda ba tare da bacin rai ko samun wata tangarda ba?.
Murmushi mai tafe da hawaye ne kan fuskarta ganin mutanen da suka zo matan,mero ce da gwaggo asabe,sai inna kulu da kuma karima matar kawunta
"Sannunku da zuwa gwaggo kunsha hanya" ta fada itama tana zama qasan carfet cikinsu kamar yadda ta samesu zaune a nan,ko banza taji dadin gani masoyan nan nata biyu meronta da kuma gwaggo asabe,akace naka naka ne hakan take,sai ta dinga jin dadi da nutsuwa har cikin ranta,bakinta yaqi rufuwa gata ga meronta,falon jama'ar dake kai kawo sunyi yawa,hakan ya sanya ta kwashesu zuwa cikin dakinta,ba wanda ya damu da su don ba wanda ya qara bi ta kansu ma,hira suka balle sosai da ita,kusan duk rabi labarin na garinsu ne,kamar aliya tasan da zuwansu saiga wayarta,ta gaya mata zuwan nasu take tace gata nan zuwa,babu jimawa sai gata kuwa da kulolin abinci,duk da gidan basu da damuwar abinci amma bata son aysha ta damun kanta wajen sai tayi girki,don dama ba'a son ranta ana mata gyaran jiki take shiga kitchen ba cewar aliya.
Sanda ta qaraso gidan an ragu sosai duk an dode zuwa wajen da za'a gudanar da bridal shower din,hakan yasa ta dan jima suna hira da su,da yake itama sam bata da qyamatar mutane,hakan tana da fira fiye da aysha da kuna saurin sabo.
Sunzo mata da gudunmawar da aka tara mata,wanda duka duka abinda suka kawo din bai kai ya kawo ba,ba kuma don basu da shi bane,a'ah...,qarfin abinma dai gwaggo asabe ce da mero,har cikin zuciyarta sai taji dadin gudunmawar duk da qanqantarta,wannan ce rana ta farko da zata bigi qirji tace ga wani abu da suka taba yi mata,dalili kenan data ji dadin abun ta kuma bashi girma.
"Kai.." Aliya ta fada lokaci daya dariyarta tana daukewa,saita waiwayo ta dubi aysha
"Aysha.....kaman angonki fa na gani hakimce cikin motocin can" ta fada tana nuna mata motoci ukun da suka wuce a jere iri daya,bin motocin tayi da kallo kafin ta maida idonta kan aliya tana murmushi
"Dama kina gulmar wata ba dole idonki ya dinga miki gano miki abinda ba haka ba....mutumin da muka rabu da shi yanzu yanzu a gida"
"Allah seriouse aysha shi na gani...don har mun hada idanu sai naga ya dage glass din motar" wannan karon sai da aysha tayi 'yar qaramar dariya
"Idan shi kika gani yaushe ya zama haka?...yaushe ya sayi dukkan wadan nan motocin yanzu yanzu kenan daga fitowarsa daga gidanmu ko?,may be shi da oganshi ne,don kusan ko yaushe yana gaya min suna tare" Ja aliya tayi ta tsaya,yanayinta ya koma da gaske take irin yanayin da tasan ayshan zata fahimceta
"Wallahi Allah da gaske nake miki aysha khalipha na gani a cikin motocin can,kuma alamu duka sun nuna cewa ba wani yake ja ba shi ake ja motarshi ce,kayan jikinsa fa ba irin wanda muka ganshi da su bane yanzu" shiru dukka sukayi aliya na kallon aysha cikin tantama,yayin da aysha ta soma shiga tunani gami da shakka,ajiyar zuciya aliya ta saki sannan tace
"Allah aysha tun asali sam khalipha baiyimin kama da wanda ke cikin babu ko yake samu a qarqashin wani ba....kin taba qare masa kallo da kyau kuwa tun daga kanshi har zuwa tafin qafa?" Dariya ce ta kubcewa aysha duk da yanayin fargaba data soma shiga
"Aliya ta yaya zan iya kallon wani namiji haka tun daga kansa zuwa qafa koda kuwa mijina ne?" Idanu aliya ta zaro
"Mijinki?...kina nufin ba zaki iya masa wannan kallon ba....lallai aysha akwai aiki a gabanki" qaramin murmushi ta saka tana kada kai
"Muje don Allah....shi din talaka ne kamata hakan shi ya qara min qwarin gwiwar amincewa zama da shi....ba da sunan miji ba...da sunan yaya dan uwa...'yan uwan da na rasa nake fata wannan karon nayi gam da katar da su kuma managarta,bana jin akwai wani ha'inci ko qarya tsakanina da shi"
"Idan kuma abinda idanuna suka gani gaske ne kinga shikenan...shikenan kaya sun tsinke a gindin kaba" aliya ta fada tana dariya
"U r mad aliya...ba don wannan zan zauna da shi ba...na amince ne saboda naga irina ne shi,kaman yanayin rayuwarmu daya ne...idan kuma har da gasken ne....bazan iya shiga cikinsu ba na zauna,ban masa qarya ba ban boye masa komai nawa ba,ban boye masa wacece ni" dukan kafadarta aliya tayi tace
"Shutup my friend....bana son wannan maganar taki ma...muje don Allah" daga haka suka ci gaba da takawa ba tare da sun sake bi ta kan maganar ba.
Numfashi ya sauke gami da lumshe bayan sun wucewa ganinsu aliya,yana sane ya sha mur ya dauke kai gamida dagr glass din sama don tayi tsammanin cewa bashi bane idanunsa ya bude sannan yace
"Jibril"
"Na'am sir"
"Daga yau bana son a sake saukemin glass din mota qasa idan bani na bada umarni ba"
"Yes sir,in sha Allahu" daga haka motar ta dauki shiru,addu'a yake cikin ranshi Allah yasa basu ganeshi ba,don ba yanzu ya shirya bayyanar komai ba.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Biki saura kwanaki uku gidan mommy ya soma cika da jama'a 'yan uwa da abokan arziqi,kowa zancan bikin asma'u kawai yake,da yawansu ma basusan cewa itama aysha nata auren za'ayi ba,idan sun tambaya ma takan ce a can qauyen iyayenta za'ayi,eh haka ne ayshan take cewa,don itama ta matsu ta wuce qauyen nasu,ko banza naka naka ne.
Cikin kwanakin zuwa gyaran jikin sai ya soma yi mata wahala saboda hidimar baqin dake gidan,awanninta kaso mafi yawa a kitchen take yinsu,duk da itama hakan ya mata dadi don bata ga meye na wani yin gyaran jiki ba,hakan kamar wani rawar kaine a wajenta ko wuce gona da iri,don haka sai take noqewa take fakewa da cewa gidan cike yake da baqi,hakan ya fusata aliya kan zasu maidata 'yar aikinsu,ta dage kan sai ta tattara kayanta ta dawo gidansu,da qyar ta shawo kanta ta nuna mata ranat juma'a ma zasu wuce takai baki daya tunda asabar ne daurin auren.
Tun ranar laraba aka fara gudanar da bikin,gidan kuwa ya cika ya tumbatsa da 'yan uwa da hamshaqan qawayen asma'u,tun ranar ta soma shiga ta kece raini,bridal shower suka fara yi sannan sauran events din suka biyo baya,ayshan kam mafi yawan lokaci idan bata tana kitchen ko dakinta,don data je gyaran jikin da aliya ta tilastata take dawowa,yawanci da aliyan suke zuwa,saidai ita bata shigowa gidan tunda aka fata bikin a qofar gida suke rabowa ta koma ta wuce nasu gidan.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*KO KUMA*
(07067124863)
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
24
Ranar laraba da safen mommy ta kirata dakinta,sanda ta shiga akwai qannen mummyn a ciki da wasu daga cikin 'yan uwanta zazzaune,wasu a gefan gado wasu saman tiles,binta sukayi da kallo sannan suka soma qus qus a tsakaninsu,hakanan jikinta ya bata da ita suke duk da bata iya jin me suke fada amma jikinta ya bata,tana iya jin sautin dariya dariya qasa qasa daga bakunan wasu daga cikin 'yammatan dake cikin dakin,saidai batasan meye abin dariyar ba,jikinta dai atamfa ce riga da zani sai hijabi data dora iya gwiwa kanta babu dankwali,sai tudun gashinta dake matse a cikin ribbom.
A ladabce ta tsugunna a bayan mummy wadda ke gaban wardrobe tana fidda kayan da zata sanya anjima,ba tare data waiwayo ba tace
"Gobe wasu daga 'yan uwanki zasu zo daga qauye,za'a je ayi miki jere....ya kamata ki sanar da shi zuwan nasu,ya bayar da muqullin gidan ko ya rakasu,don ba lallai su su sake gane hanyar gida ba bare gidan kanshi"
"Kawai mummy ya rakamun" inji nusaiba qawar asma'u tayi caraf ta fada,cikin muryarta kana iya jiyo sautin dariyar dakeson fitowa,nusaiban 'yace ga yayar mummyn,qawancensu yayi daidai saboda hali da yazo daya,tana son harkar girma itama,tana son fantamawa,tana son kuma mu'amala da masu hannu da shuni
"Ko yazo ko ya samo wanda xai rakaku...don ko su halima sunce ma ba zasu iya gane hanyar gidan ba" dariya nusaiba ta sake da alama tasan komai ko an bata labari,sai ta kuma waske tana wa farida cousin dinta dake zaune kusa da ita magana
"Toh mummy" ta fada tana miqewa jiki a salube,tana qirga iya kwanakin daya rage zata sake shiga wata sabuwar rayuwar,ko ya zata kaya da ita ita kuma?.
Zata fice sukayi clashing da naana,qawa ce ga asma'u,amma ta zama kamar 'yar gida saboda yadda ake buga qawance,duban juna sukayi naana ta saki dariya,abinda tsahon sanin da aysha tayi mata bata taba yi mata ba,face kallon banza da kallon raini dake shiga tsakaninsu,saboda asma'u ta riga ta gama dorasu kan turba
"Amarya amarya" naanan ta fada,kallo daya aysha tayi mata ta dauke kanta ta wuce,karon farko da hawaye taji sun cika idanunta,karon farko data ji damuwa ta sosa zuciyarta,gefan gadonta ta zauna,tana qoqarin tsaida hawayen,saidai bata da wannan ikon,saboda zuciyarta na buqatar rage nauyin da ta jima tana dauka,cikin muryar kuka ita kadai cikin daki take cewa
"Ya Allah...kaine mafi jin qan masu jin qai...kaine mafi tausayin masu tausayi...kaine mai tallafar raunana...ya Allah...ka fini sanin wace ce ni...ka fini sanin dalilinka na sanya rayuwata a wannan bigiren,ka fini sani gobe da jibina har zuwa qarshe na,Allah kai kace mu roqeka zaka amsa mana,ya Allah....kayi ruqo da hannayena...ka yiwa rayuwa ta jagoranci...Allah karka barni dai dai da qiftawar ido ya Allah...." Ta qarashe addu'ar tana fashewa da kuka wanda ya tilastata cusa kanta cikin fulalluka don gudun fitowar sautin kukan nata.
Ta jima tana kokawa ita kadai....ta dade tana fitar da ruwan hawaye kafin ta lallashi zuciyarta.
Qarfe shida na yammaci sanda 'yammatan amarya ke shirye shiryen zuwa bridal shower aka ce mata ta fito ga 'yan uwanta nan daga takai,gabanta na dukan uku uku ta zira hijabinta ta tako zuwa falon gidan inda aka aje su don bana ce aka saukesu ba,duba da yadda yawanci mutanenmu na birni ke raina mutanen karkakara,bayan mutane ne da Allah ya musu baiwa iri daban daban masu tarin yawa fiye da mu din,fargabarta na su waye suka zo?,yaya zasu zauna da su a muhalli guda ba tare da bacin rai ko samun wata tangarda ba?.
Murmushi mai tafe da hawaye ne kan fuskarta ganin mutanen da suka zo matan,mero ce da gwaggo asabe,sai inna kulu da kuma karima matar kawunta
"Sannunku da zuwa gwaggo kunsha hanya" ta fada itama tana zama qasan carfet cikinsu kamar yadda ta samesu zaune a nan,ko banza taji dadin gani masoyan nan nata biyu meronta da kuma gwaggo asabe,akace naka naka ne hakan take,sai ta dinga jin dadi da nutsuwa har cikin ranta,bakinta yaqi rufuwa gata ga meronta,falon jama'ar dake kai kawo sunyi yawa,hakan ya sanya ta kwashesu zuwa cikin dakinta,ba wanda ya damu da su don ba wanda ya qara bi ta kansu ma,hira suka balle sosai da ita,kusan duk rabi labarin na garinsu ne,kamar aliya tasan da zuwansu saiga wayarta,ta gaya mata zuwan nasu take tace gata nan zuwa,babu jimawa sai gata kuwa da kulolin abinci,duk da gidan basu da damuwar abinci amma bata son aysha ta damun kanta wajen sai tayi girki,don dama ba'a son ranta ana mata gyaran jiki take shiga kitchen ba cewar aliya.
Sanda ta qaraso gidan an ragu sosai duk an dode zuwa wajen da za'a gudanar da bridal shower din,hakan yasa ta dan jima suna hira da su,da yake itama sam bata da qyamatar mutane,hakan tana da fira fiye da aysha da kuna saurin sabo.
Sunzo mata da gudunmawar da aka tara mata,wanda duka duka abinda suka kawo din bai kai ya kawo ba,ba kuma don basu da shi bane,a'ah...,qarfin abinma dai gwaggo asabe ce da mero,har cikin zuciyarta sai taji dadin gudunmawar duk da qanqantarta,wannan ce rana ta farko da zata bigi qirji tace ga wani abu da suka taba yi mata,dalili kenan data ji dadin abun ta kuma bashi girma.