Sashe 91
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wajen videos ta shiga,films ne na soyayya sunfi talatin,kuma duka na jaruman nan da ranar ya tayata kallon fim din ta gudu ta barshi,murmushi ta saki ita daya tana rufe fuskarta kamar yana ganinta,wato yana sane kenan,shi da yace aure takeso?,yace kuma me take gani haka,wani murmushin ya sake subuce mata ba tare data shirya ba,tuna maganarshi ta dazun tayi,hakan ya sanyata zama dirshan ta jawo wayarta,a qalla ta kusa kashe minti talatin tana rubuta saqon tana gogewa,inda daga bisani tayi bismillah kawai ta tura,saikuma tayi tsam tana tuna abinda ta tura din,kamar ta wuce makadi da rawa,tunda ya riga daya shiga haka ta haqura ta koma ta kwanta tana kunna daya daga cikin fina finan ta soma kalla.
Gurine da sau tari yakan je ya zauna kawai idan zaiyi karatu ko zai duba wasu mihimman abubuwa da suka shafi kamfaninsu wanda ya zama dole ya duba din,a yau dai babu ko daya daga ciki,yana zaune ne kawai yana shan ni'imar da Allah ya yiwa wajen,bai jima da gama waya da anni ba a nan ya jiyo kamar hayaniya,ta gaya mishi su amal ne ke rigima da zeenart,dama dazun nan ta gama yi musu shari'a,sosai ranshi ya baci ya dinga fada yana fadin basu isa su hanawa uwarshi zama lafiya ba,don haka kowacce ta kama gabanta,dama shi sun isheshi baisan ubanme suke zaune gidan sukeyi ba,annin ce ta dakatar dashi,tace suma duk abinda zayayi zai zama ne saboda Allah ya fifitasu a kansu,bayan basu suka tsamo kansu daga halin da suke ciki ba ganin dama ce ta ubangiji da baiwarsa,hakan ya haqura,amma yayi waya da haidar ya gaya mishi lallai kome ake ciki zaman kowa ya saitu a gidan,amma karya bari anni ta sani saboda zata hana ruwa gudu ne,ya sani haidar din kome zaiyi tamkar yana nan ne,da wannan tunanin da baci da ranshi yayi yaji shigowar saqon,da fari banza yayi dashi sai wani bari na zuciyarshi ya dinga azalzalarsa da ya duba din,fuska a tamke ta soma danna wayar sai gashi ya buge da sakin sassanyar murmushi,gyara zamanshi yayi sosai ya soma maida mata reply.
Tsaida kallon tayi da taji shigowar saqo cikin mamakin ganin number khalipha ce,tana duba saqon tana murmushi,wani abu ya dinga tsumata,saita biye mishi ta sake maida masa amsa,wasa wasa sai da suka dauki mintuna goma suna musayar saqonni,wanda sai daga baya aysha ta dinga duba saqonnin tana zaro ido,ya akayi ta rubuta wannan kalaman?,sai taji kamar yana gabanta saboda kunyar data kamata.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Suna kan hanyar dawowa daga daga aji ita da hanan da suka kammala daukan karatu kisan lokaci daya wayarta ta dauki kida,tana dubawa taga mero ce,cikin zumudi ta daga wayar ta kara a kunneta,gaisawa sukayi daga bisani take shaida mata ta haihu jibi suna,cikin bata rai aysha tace
"Yanzu qawa ki haihu kamarni sai yau kwana biyar nake ji?,ai shikenan babu komai na gode
"Don Allah indo kiyi haquri,wallahi wayarce ta samu matsala saida habu ya sauyamin wata yanzu yanzu aka kawota kena fara kira wallahi" sai a sannan aysha ta saki ranta,hira suka dan taba daga bisani tayi mata alqawarin halartar sunan.
Sai data zo kwanciya ta tura masa masa saqo kamar yadda ta saba koda yaushe ya kuma zame mata jiki,ta gaya mishi zuwa takai din,tana kwance idanunta a lumshe tana tsammanin jin reply kamar yadda ta saba sai taji shuru,duka sai taji yau babu dadi wani banbarakwai,tun tana sauraro har bacci ya dauketa.
Qarfe uku na yammacin washegari suna tsaka da kammala shirinsu na tafiya takai,hanan ita zata mata rakiya wannan karon,ana ya gobe suna ta shirya zasu daman ta dawo ranar sunan saboda washegari tara na safe zasuyi presentation,saidai gaba daya hankalinta kacokam yana kan wayarta,tun jiya data tura mishi saqo har yau bata ji daga gareshi ba,sai taji gaba daya bata dokin tafiyar.
Tana riqe da powder tana shafawa wayar tata ta dauki ruri,da sauri ta aje powder din ta rarumi wayar tana duba mai kiran,khalipha ne kamar yadda tasa capital K a sunanshi,cikin hanzari ta daga ta kara a kunnenta tana aje boyayyar ajiyar zuciya,saidai tuni ya jita,sallama yayi mata sai a sannan ta tuna cewa batayi masa sallama ba,a kunyace ta amsa tana gaidashi,ya amsa mata,shuru tayi tana saurarenshi sanda yake amsa mata gaisiwarta,sai taji muryarshi ta canza ba yadda ta santa ba,kamar ma baida lafiya
"Tun jiya banji daga gareka ba,Allah yasa lafiya"
"Naga saqonki amma ban iya maida reply ba,bana jin dadi ne" hankalinta ne taji ya tashi,take zuciyarta ta karye
"Subhanallahi,me ya sameka ya khalipha?" Karo na farko bakinta yayu subutar ambatar sunanshi,raunin dake muryarta ya fiti qarara,yadda ta ambaci sunan nasa yayi masifar yi masa dadi,har yaji me yasa tunda baice mata bashi da lafiya ba don ya samu irin wannan kukawar daya samu a yanzu?
"Dont bother....ciwon kaina ne ya tashi,kuma baiyi wani worst ba" hawaye ne taji yana son sauko mata saboda tuna silar samuwar ciwon kan nashi,karo na farko da taji bakinta da zuciyarta na Allah wadai da masu hali irin na ahalinsu ita da khalipha,mutanen da basu san qima da martabar zumunci ba,mutanen da basu haifarwa da rayuwarsu komai ba face wani tabo da miki da suka bar zuciyoyi da rayuwarsu,take tafiyarta takai ta fice mata a rai baki daya fit,banda daraj da qimar da mero keda ita a wajenta da ta fasa ba zata dara koda nan da can ba
"Dont cry mana pls...so kike ki daga min hankali?" Ya tambayeta da sassanyar muryarshi da ciwon ya sake sanyayar da ita,cikin mamakin yadda ya fahimci kukanta ba tare daya ganta ba ta goge qwallar data soma sauko mata
"Am sorry" ta fada a hankali
"Allah ya baka lafiya....amma karkace zaka zauna a gida hakanan da ciwo,pls i beg you"idonsa ya lumshe yana jin gardin kulawa daga wajen wata mace baya ga uwa
"In sha Allah,but pls stop crying....will you?" Kai ta kada sannan tace
"Is ohk"
"Ma sha Allah,kin shirya tafiyan?"
"Eh,yanzu muke shiryawa"
"Yayi.....bana son tafiyarki ke daya"
"Eh tare da hanan ne,yanzun zamu wuce tasha mu samu qaramar mota"
"What!,motar me?,no...ki jira nan da minti arba'in akwai wanda na turo zaizo ya kaiku,ban yarda ki sake hawa motar haya ba"
"Thank you" ta fada cikin wani tune mai sanyi wanda ya ratsa zuciyarshi har ya sashi lumshe idanu,ya dora hannunshi saman kanshi ya shafeshi kadan,sai yaji kamar an rage masa ciwon dake damunsa.
Minti arba'in da biyar dai dai ta sake ganin kiran khalipha
"Ki sameshi a wajen hostel ya iso"
"Ohk,shukran" ta fadi tana sauya yanayin muryarta
"Eheeenn" ya iya fadi kawai ta katse wayar ta dubi hanan
"Mu wuce ya iso", ga mamakinta motoci uku ne tsaye suna jiranta,idanu suka hada da hanan dariya ta saki
"Wannan yaya naki yana ji dake,wannan 'yar uwa ce da alama ta musamman wadda babu kamarta" ta fadi tana sheqewa da dariya,shuru ayshan tayi mata kawai tana murmushi don nata da abun fada,kamar yadda suka saba treating nata cikin girmamawa idan khalipha na nan yanzu ma haka ne,su suka bude mata gidan baya suka shiga ita da hanan kana suka rufe suka tashi motocin a hankali har suka fice daga cikin makarantar kana suka harba kan titi.
A hankali ya sauke wayar yana tariyar muryarta da maganganunta a kwanyarsa yana sakin murmushi,sai yaji wani sauqi na musamman ya samu a gareshi,zamewa yayi ya kwanta ta gefan damanshi idanunshi a rufe yana ci gaba da tuna ta.
A hankali yaji kamar ana shafashi,da fari yayi tsammanin irin mafarkin da yakanyi lokaci zuwa lokaci ne,sai kuma yaji sam ba haka bane wannan ya wuce mafarki,da hanzari ya bude idanunshi,sai yaci karo da lili,tube take haihuwar uwarta tana masa wani mayen kallo,cikin azama da zafin nama ya zabura ya miqe wanda hakan yayi sanadiyyar harbata da yayi ta fado daga saman gadon,cikin tsananin bacin rai yake huci,fuskarnan tuni ta hada ja,dubanta yake zuciyarsa na masa zafi ya soma mata magana cikin harshen turanci
"Ban hanaki zuwa min gida ba?,ke wace iriyar shaidaniya ce?" Duk data bugu hakan bai hanata tashi ba tana daurewa zafin data ji,don a duniya bata da burin daya wuce ta mallaki khaliphan,jikinta ta soma girgizawa cikin son jan hankali
"Bazan iya daina zuwa gidanka ba khalipha,ka saki ranka da jikinka mu more rayuwarmu,wai meye kake tsoro a ciki ne kodon kai farin shiga ne?,babu komai fa,ko masu irin addininku nawa ne muke tare dasu,saikai ne zaka dinga wani nuna addininka ya hanaka bayan munsan komai,kawai ka saki jiki saika fara zaka gane me nake nufi" ('yan uwa musulmi mu kula da kyau,duk lokacin da kaje ka aikata wani abu ba dai dai ba tamkar kana wakilatar sauran musulmai 'yan uwanka ne,duk sanda kayi wani mummunan abu kana sunan musulmi kamar kayi tarnishing image na musulmai ne,don duk wanda bai taba cin karo da mumini na qwarai ba sai ya fara cin karo da gurbatacce zai ma dukkan musulmi kudin goro ne yace halinsu daya,Allah ya tsare mu ya tsare mana imaninmu gaba daya amin).
Gigitacciyar tsawa ya daka mata yana gaya mata karta qaraso inda yake,saidai bata ji kashedinsa ba taci gaba da takowa cikin wani shu'umin murmushi har ta iso gabanshi,hannunshi yasa gaba daya ya hankadata baya ta kifa,wanda hakan yasa ta bude sosai ta kuma ji zafi,cikin kakkausar murya yace ta fita daga gidan gaba daya ya bata minti biyar,idan kuma ta wuce haka zata gamu da fushinsa da bacin ranshi,yana gama fada mata haka ya wuce toilet ya kulle kanshi.
A toilet sit ya zauna yana dafe da kanshi da ya sake tsananta masa,tabbas badon mace bace babu abinda zai hanashi yi mata dan banzan duka,shu'umancin lili yana neman wuce tunaninsa,lallai dole ya yiwa kansa rigakafi,saboda shi dan adam ne kamar kowa,zuciya kuma bata da qashi,hakanan tana tare da shaidan.
Sai bayan minti goma sha biyar ya fito daga toilet din bayan ya daura alwala,ba kowa cikin dakin don haka ya fita ya dudduba gidan ko ina ya tabbatar ta fita sannan ya kulle gidan ya koma bedroom dinsa ya samu waje ya kwanta yana maida numfashi.
Tsakanin takai da wudil ba wani nisa bane ko tazara mai yawa,saboda haka nan da nan suka iso
Gurine da sau tari yakan je ya zauna kawai idan zaiyi karatu ko zai duba wasu mihimman abubuwa da suka shafi kamfaninsu wanda ya zama dole ya duba din,a yau dai babu ko daya daga ciki,yana zaune ne kawai yana shan ni'imar da Allah ya yiwa wajen,bai jima da gama waya da anni ba a nan ya jiyo kamar hayaniya,ta gaya mishi su amal ne ke rigima da zeenart,dama dazun nan ta gama yi musu shari'a,sosai ranshi ya baci ya dinga fada yana fadin basu isa su hanawa uwarshi zama lafiya ba,don haka kowacce ta kama gabanta,dama shi sun isheshi baisan ubanme suke zaune gidan sukeyi ba,annin ce ta dakatar dashi,tace suma duk abinda zayayi zai zama ne saboda Allah ya fifitasu a kansu,bayan basu suka tsamo kansu daga halin da suke ciki ba ganin dama ce ta ubangiji da baiwarsa,hakan ya haqura,amma yayi waya da haidar ya gaya mishi lallai kome ake ciki zaman kowa ya saitu a gidan,amma karya bari anni ta sani saboda zata hana ruwa gudu ne,ya sani haidar din kome zaiyi tamkar yana nan ne,da wannan tunanin da baci da ranshi yayi yaji shigowar saqon,da fari banza yayi dashi sai wani bari na zuciyarshi ya dinga azalzalarsa da ya duba din,fuska a tamke ta soma danna wayar sai gashi ya buge da sakin sassanyar murmushi,gyara zamanshi yayi sosai ya soma maida mata reply.
Tsaida kallon tayi da taji shigowar saqo cikin mamakin ganin number khalipha ce,tana duba saqon tana murmushi,wani abu ya dinga tsumata,saita biye mishi ta sake maida masa amsa,wasa wasa sai da suka dauki mintuna goma suna musayar saqonni,wanda sai daga baya aysha ta dinga duba saqonnin tana zaro ido,ya akayi ta rubuta wannan kalaman?,sai taji kamar yana gabanta saboda kunyar data kamata.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Suna kan hanyar dawowa daga daga aji ita da hanan da suka kammala daukan karatu kisan lokaci daya wayarta ta dauki kida,tana dubawa taga mero ce,cikin zumudi ta daga wayar ta kara a kunneta,gaisawa sukayi daga bisani take shaida mata ta haihu jibi suna,cikin bata rai aysha tace
"Yanzu qawa ki haihu kamarni sai yau kwana biyar nake ji?,ai shikenan babu komai na gode
"Don Allah indo kiyi haquri,wallahi wayarce ta samu matsala saida habu ya sauyamin wata yanzu yanzu aka kawota kena fara kira wallahi" sai a sannan aysha ta saki ranta,hira suka dan taba daga bisani tayi mata alqawarin halartar sunan.
Sai data zo kwanciya ta tura masa masa saqo kamar yadda ta saba koda yaushe ya kuma zame mata jiki,ta gaya mishi zuwa takai din,tana kwance idanunta a lumshe tana tsammanin jin reply kamar yadda ta saba sai taji shuru,duka sai taji yau babu dadi wani banbarakwai,tun tana sauraro har bacci ya dauketa.
Qarfe uku na yammacin washegari suna tsaka da kammala shirinsu na tafiya takai,hanan ita zata mata rakiya wannan karon,ana ya gobe suna ta shirya zasu daman ta dawo ranar sunan saboda washegari tara na safe zasuyi presentation,saidai gaba daya hankalinta kacokam yana kan wayarta,tun jiya data tura mishi saqo har yau bata ji daga gareshi ba,sai taji gaba daya bata dokin tafiyar.
Tana riqe da powder tana shafawa wayar tata ta dauki ruri,da sauri ta aje powder din ta rarumi wayar tana duba mai kiran,khalipha ne kamar yadda tasa capital K a sunanshi,cikin hanzari ta daga ta kara a kunnenta tana aje boyayyar ajiyar zuciya,saidai tuni ya jita,sallama yayi mata sai a sannan ta tuna cewa batayi masa sallama ba,a kunyace ta amsa tana gaidashi,ya amsa mata,shuru tayi tana saurarenshi sanda yake amsa mata gaisiwarta,sai taji muryarshi ta canza ba yadda ta santa ba,kamar ma baida lafiya
"Tun jiya banji daga gareka ba,Allah yasa lafiya"
"Naga saqonki amma ban iya maida reply ba,bana jin dadi ne" hankalinta ne taji ya tashi,take zuciyarta ta karye
"Subhanallahi,me ya sameka ya khalipha?" Karo na farko bakinta yayu subutar ambatar sunanshi,raunin dake muryarta ya fiti qarara,yadda ta ambaci sunan nasa yayi masifar yi masa dadi,har yaji me yasa tunda baice mata bashi da lafiya ba don ya samu irin wannan kukawar daya samu a yanzu?
"Dont bother....ciwon kaina ne ya tashi,kuma baiyi wani worst ba" hawaye ne taji yana son sauko mata saboda tuna silar samuwar ciwon kan nashi,karo na farko da taji bakinta da zuciyarta na Allah wadai da masu hali irin na ahalinsu ita da khalipha,mutanen da basu san qima da martabar zumunci ba,mutanen da basu haifarwa da rayuwarsu komai ba face wani tabo da miki da suka bar zuciyoyi da rayuwarsu,take tafiyarta takai ta fice mata a rai baki daya fit,banda daraj da qimar da mero keda ita a wajenta da ta fasa ba zata dara koda nan da can ba
"Dont cry mana pls...so kike ki daga min hankali?" Ya tambayeta da sassanyar muryarshi da ciwon ya sake sanyayar da ita,cikin mamakin yadda ya fahimci kukanta ba tare daya ganta ba ta goge qwallar data soma sauko mata
"Am sorry" ta fada a hankali
"Allah ya baka lafiya....amma karkace zaka zauna a gida hakanan da ciwo,pls i beg you"idonsa ya lumshe yana jin gardin kulawa daga wajen wata mace baya ga uwa
"In sha Allah,but pls stop crying....will you?" Kai ta kada sannan tace
"Is ohk"
"Ma sha Allah,kin shirya tafiyan?"
"Eh,yanzu muke shiryawa"
"Yayi.....bana son tafiyarki ke daya"
"Eh tare da hanan ne,yanzun zamu wuce tasha mu samu qaramar mota"
"What!,motar me?,no...ki jira nan da minti arba'in akwai wanda na turo zaizo ya kaiku,ban yarda ki sake hawa motar haya ba"
"Thank you" ta fada cikin wani tune mai sanyi wanda ya ratsa zuciyarshi har ya sashi lumshe idanu,ya dora hannunshi saman kanshi ya shafeshi kadan,sai yaji kamar an rage masa ciwon dake damunsa.
Minti arba'in da biyar dai dai ta sake ganin kiran khalipha
"Ki sameshi a wajen hostel ya iso"
"Ohk,shukran" ta fadi tana sauya yanayin muryarta
"Eheeenn" ya iya fadi kawai ta katse wayar ta dubi hanan
"Mu wuce ya iso", ga mamakinta motoci uku ne tsaye suna jiranta,idanu suka hada da hanan dariya ta saki
"Wannan yaya naki yana ji dake,wannan 'yar uwa ce da alama ta musamman wadda babu kamarta" ta fadi tana sheqewa da dariya,shuru ayshan tayi mata kawai tana murmushi don nata da abun fada,kamar yadda suka saba treating nata cikin girmamawa idan khalipha na nan yanzu ma haka ne,su suka bude mata gidan baya suka shiga ita da hanan kana suka rufe suka tashi motocin a hankali har suka fice daga cikin makarantar kana suka harba kan titi.
A hankali ya sauke wayar yana tariyar muryarta da maganganunta a kwanyarsa yana sakin murmushi,sai yaji wani sauqi na musamman ya samu a gareshi,zamewa yayi ya kwanta ta gefan damanshi idanunshi a rufe yana ci gaba da tuna ta.
A hankali yaji kamar ana shafashi,da fari yayi tsammanin irin mafarkin da yakanyi lokaci zuwa lokaci ne,sai kuma yaji sam ba haka bane wannan ya wuce mafarki,da hanzari ya bude idanunshi,sai yaci karo da lili,tube take haihuwar uwarta tana masa wani mayen kallo,cikin azama da zafin nama ya zabura ya miqe wanda hakan yayi sanadiyyar harbata da yayi ta fado daga saman gadon,cikin tsananin bacin rai yake huci,fuskarnan tuni ta hada ja,dubanta yake zuciyarsa na masa zafi ya soma mata magana cikin harshen turanci
"Ban hanaki zuwa min gida ba?,ke wace iriyar shaidaniya ce?" Duk data bugu hakan bai hanata tashi ba tana daurewa zafin data ji,don a duniya bata da burin daya wuce ta mallaki khaliphan,jikinta ta soma girgizawa cikin son jan hankali
"Bazan iya daina zuwa gidanka ba khalipha,ka saki ranka da jikinka mu more rayuwarmu,wai meye kake tsoro a ciki ne kodon kai farin shiga ne?,babu komai fa,ko masu irin addininku nawa ne muke tare dasu,saikai ne zaka dinga wani nuna addininka ya hanaka bayan munsan komai,kawai ka saki jiki saika fara zaka gane me nake nufi" ('yan uwa musulmi mu kula da kyau,duk lokacin da kaje ka aikata wani abu ba dai dai ba tamkar kana wakilatar sauran musulmai 'yan uwanka ne,duk sanda kayi wani mummunan abu kana sunan musulmi kamar kayi tarnishing image na musulmai ne,don duk wanda bai taba cin karo da mumini na qwarai ba sai ya fara cin karo da gurbatacce zai ma dukkan musulmi kudin goro ne yace halinsu daya,Allah ya tsare mu ya tsare mana imaninmu gaba daya amin).
Gigitacciyar tsawa ya daka mata yana gaya mata karta qaraso inda yake,saidai bata ji kashedinsa ba taci gaba da takowa cikin wani shu'umin murmushi har ta iso gabanshi,hannunshi yasa gaba daya ya hankadata baya ta kifa,wanda hakan yasa ta bude sosai ta kuma ji zafi,cikin kakkausar murya yace ta fita daga gidan gaba daya ya bata minti biyar,idan kuma ta wuce haka zata gamu da fushinsa da bacin ranshi,yana gama fada mata haka ya wuce toilet ya kulle kanshi.
A toilet sit ya zauna yana dafe da kanshi da ya sake tsananta masa,tabbas badon mace bace babu abinda zai hanashi yi mata dan banzan duka,shu'umancin lili yana neman wuce tunaninsa,lallai dole ya yiwa kansa rigakafi,saboda shi dan adam ne kamar kowa,zuciya kuma bata da qashi,hakanan tana tare da shaidan.
Sai bayan minti goma sha biyar ya fito daga toilet din bayan ya daura alwala,ba kowa cikin dakin don haka ya fita ya dudduba gidan ko ina ya tabbatar ta fita sannan ya kulle gidan ya koma bedroom dinsa ya samu waje ya kwanta yana maida numfashi.
Tsakanin takai da wudil ba wani nisa bane ko tazara mai yawa,saboda haka nan da nan suka iso