Sashe 108
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wani jiri taji yana niyyar kayar da ita sanda taga tarin al'umma da rumfuna tun daga qofar gidan daddy zuwa cikin harabar gidan dake a wangale,kusan tunda tazo gidan ta gama rayuwarta ciki bata taba ganin an wangale qofar gidan irin haka ba
"Ya khalipha?,me yake faruwa?,me ake haka a gidan?" Ta tambayeshi cike da tsoron amsar da zata fito daga bakinsa
"Kinga saukarmu kenan nace bari na kawoki kiga jikinsa don hankalinki yafi kwanciya,wataqila maqota ke wani sha'anin koma daurin aure ake ne,amma kinsan me za'ayi?,shiga ciki ina nan ina jiranki idan kun gaisa saiki fito mu tafi"
"To" tace tana fitowa bayan ya bude mata murfin motar da kanshi,haka kawai ta dinga jin kamar zata fadi qafafunta sunyi laushi kamar ba'a jikinta ba haka ta dinga takawa har cikin gidan.
Anni ta soma cin karo da ita,mamaki dukka saiya kamata,meya kawo anni gidan to me akeyi?,ko dama ta sansu?
"Allah ya jiqan alhj,ba shakka anyi babban rashin da aka jima ba'ayi irinsa ba" kunnenta ya dauko mata muryar wani daga can wata rumfa dake bayanta da yazo gaisuwa,bata gama wannan ba ta dinga jiyo ihun asma'u tana kiran sunan daddy,da hanzari ta taka don shiga tabi ba'asin meke faruwa sai taji gangar jikinta ta kasa daukarta,ji tayi tana sulalewa zuwa qasa,daga haka bata sake sanin abinda ke faruwa ba.
Sanda ta farka dakin ta dinga bi da kallo sai daga bisani ta gane a asibiti take,a hankali abinda ya faru ya dawo mata kanta,saita fashe da kuka tana fadin
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" a hankali wanda hakan shi ya fargar da khalipha dake saman abun sallah cewar ta farka,gaba daya hankalinshi a tashe yake cikin hanzari ya isa gabanta anni dake zaune can kan kujera ta taso itama,ta dakatar da khalipha dake shirin dagata ta zauna,saiya fasa ya tsaya saitin kanta yana shafa sumar kanta a hankali yana tayata fadin innalillahin,har tsahon wani lokaci bai hanata kuka ba hakanan basu fasa maimaita innalillahin ba tare dashi,daga bisani ne ta saki ajiyar zuciya tana cewa
"Da gaske ya khalipha daddy ya mutu?,dama sallama jiya mukayi dashi kenan a waya?" Ganin shima ba wani a nutse yake can ba saboda yanayin da ayshan ke ciki ya sanya anni matsowa
"Allahn daya haliccemu shi ya fimu sonshi,ya kuma fimu sanin dalilin daya sanya ya dauke abinshi,kada mu yiwa Allah daya bamu shi butulci"
Kai kawai take gyadawa tana ci gaba da ambaton sunan Allah,wanda shi ya dafa mata ta samu nutsuwa,sai da anni ta tabbatar ta nutsu sannan ta taimaka mata ta tashi ta zauna,khalipha ya sanya daya daga cikin yaranshi suka yiwa likitar magana,macace likitan dalili kenan ma daya sanya khaliphan ya kawota wannan asibitin,ta tabbatar mishi komai ya koma normal,saidai ta kiyaye damuwa da bacin rai ta rubuta sallama.
Gidan anni suka wuce kai tsaye tayi wanka,saidai har a sannan hankalinta bai jikinta,ta matsa sai an kaita can gidan makokin,haka khalipha ya dauketa ya kaita.
Karon farko data sake sallamawa Allah lamuranta ta tabbatar lallai mutum koshi waye ba'a bakin komai yake ba,kwana daya tak mummy da asma'u sunfi kowa fita hayyacinsu,tausayin kanta da tausayinsu ya kamata,kuka ta dinga sosai ta manta da duk wani sharadi na likita,anty safiyyace kawai mai qarfin halin lallashinsu,ranar mummy ce ke cewa aysha ta yafe mata,saboda gabanta ita da asma'u daddy ya rasu,sun tsorata matuqa da yadda mutuwa take,fitar rai ba wasa bane,kowanne dan adam lallai saiya taba yaji a jikinsa,saidai fata Allah yasa mu dace.
A nan khalipha yake barinta,kullum sai dare yake zuwa ya dauketa su koma gida,har a sannan aysha bata daina kukan rasuwar daddy ba,saidai tanayi a boye yadda khalipha bazai gani ba hankalinsa ya tashi,don dukkan wani qoqari nasa yana yi don ganin ta sake,saidai ita kanta batasan ma meke damunta ba,hatta da taste din bakinta ya sauya tun daga randa akayi mutuwar.
Ranar sadakar uku su inna yelwa suka zo,tunda sukazo aysha ta lura da ta sauya gaba daya,sai da ana hira takejin bata da cikakkiyar lafiya kwana biyu,yau da lafiya gobe babu,ba'ayi azahar ba umminta ta iso itama ita dasu basma,don ita kanta mutuwar ta daketa,taso qwarai ace Allah ya hada ganawarsu da mutumin daya ceci rayuwar 'yarta,taso sosai tayi masa godiya koda sau daya ne a rayuwarta amma Allah bai nufa ba.
Shuru dakin da suke zaune ya dauka gaba daya,baka jiyo komai sai muryar wata baiwar Allah dake harabar gidan tana wa'azi kan mutuwa,tun daga sanda mala'ikan mutuwa dubi bawa,zarar rai,wankan gawa kwanciyar kabari da yadda mala'iku kebi suna jin yadda jama'a ke fadar halayyar mamaci,da yadda hakan yake tasiri a kansa da sauransu,sosai jikin inna yelwa ya sake laqwas,tunda tazo gidan bata ji mutum daya daya fadi mummunan hali akan daddy ba,yau ga inna yelwa ga ummi,abinda ya dauki tsahon shekaru rabon daya faru,sai inna yelwa ta kasa sakewa gaba daya,sai satar kallon ummi take,ba dadewa fa fashe da kuka,ita kadai tasan me take ji a lokacin,ba abinda take tunawa sai abinda ta aiwatar a rayuwarta a baya,yanzu idan mala'ikan daukar rai ya cimmata fa?,tabbas tasan kadanne masu fadin alkhairi a kanta,idon kowa sai yayi kanta,Allah yasa dukka 'yan takai ne da wadanda suka jibanci aysha,anzo mata sosai saboda yanzun kowa neman fada yake da ita
"Don girman Allah ki yafemin naja'atu,wallahi na cuci kaina na cuci rayuwarki keda diyarki" abinda inna yelwa ta dinga fada kenan tana zabga kuka da majina,tsit dakin yayi,yayin da ummi tayi shuru tana hadiyar wani abu mai tauri,zuciyarta quna kawai take tana yunqurin danneta da cika alqawarin data dauka a gaban dakin Allah.
Inna yelwa ta jima gaban ummi tana kuka gami da gaya mata ita ta rabata da baffale,ita ta shiga tsakaninsu,lumshe idanu ummi kawai tayi,zuciyarta nason tuna mata irin abubuwan da inna yelwan tayi mataba rayuwa,yayin da daya sashen na zuciyarta ke tunasar da ita ni'ima baiwa da kuma musanyan alkhairi da Allah yayi mata ayanzu
"Na yafe miki" kalmar data baiwa inna yelwan mamaki,don bata taba tsammatar haka daga wajen ummin da sauqi ba,hakan ya sake karya mata zuciya,nadama ta shigeta sosai,tana son kallon aysha dake zaune waje daya tana jan carbi tace ta yafe mata amma tana jin kunyarta da nauyinta,tana jin idan tace ta yafe matan tamkar ta zama mai son kai ne,amma ita kadai tasan yadda akwanakin take yawan mafarkin baffale,yana kuka yana ta cuci su aysha,ta gaggauta hada tsakaninsu,ta gaggauta neman afiya da yafiyarsu,ta raba uwa da 'ya,saidai kuma cikin kyakkyawan yanayi take ganinshi,saidai kukan kawai da yake mata,babu randa zata kwanta bacci ta tashi batayi mafarkinsa ba,abun ya takurata qwarai,kusan shi ya haifar mata da lalurar da take fama da ita a yanzu.
"Nasan ban cancanci ki yafemin ba indo,amma na gamaki da Allah duk sanda kike jin kin huce na cancanci yafiya toki yafemin" ta fada tana fashewa da kuka,kai aysha ta kada kawai,itakam me zata cewa Allah banda godiya,komai aduniya da zai samu bawa koya sameshi yana damfare da yanayin rayuwarshi na baya,ba don qalubalen data fuskanta ba da babu lallai daddy ya daukota ya kawota nan,da bai kawota din ba da babu lallai asma'u ta hadata da khalipha,duk da yakedai duk inda bawa yake rabonsa baya kubuce masa
"Na yafemiki,Allah ya yafe mana gaba daya" kusan wannan shi ya kawo daidaito tsakanin gabar inna yelwa da ummi naja'atu.
Qarfe hudu da minti ashirin na yammaci yasa aka kira mishi ayshan,can wani waje da babu kowa cikin gidan suka zauna saman darduma,ya tsareta da idanunshi bayan ya aje abinci a tsakiyarsu,saita zuba mishi ido itama sonshi da qaunarshi na sake karyar mata da zuciya,hawaye ya cika idanunta,haka kawai take jin wani abu ya cunkushe mata wuya wanda shike hanata cin abinci
"Oya,bude bakin" ya fada bayan ya debo abincin a cokali yakai bakinta,sai kawai ta sake masa kuka mara sauti sai sheshsheqa
"Ya salam" ya fada yana aje cokalin cikin damuwa,ya rasa me yasa har yau zuciyarta taqi saki,a yanzun kuka baiyi mata wani wuya,yanzu yanzu ne zata saki abinta,bai manta ba jiya suna kici kicin tahowa zai kawota,zata sanya wata riga taqi shigarta tayi mata kadan,sai zuwa yayi ya sameta a zaune dirshan tana sharbar kuka abinta,daga lallashi nan ma cibi ya zama qari,hannunshi ya miqa mata batayi wata wata ba ta taho,cikin jikinsa ya sanyata tana shafar bayanta a hankali
"Uwaisha ba zaki sanya haquri cikin zuciyarki ba ehmm?,bakisan yadda zuciyata ke quna ba a duk sa'in dana ganki cikin damuwa?,so kike wani abu nima ya sameni?" Saita fashe da kuka tana girgiza kai tana fadin a'ah
"Ya Allahu.....kin zama makokiya gaba daya?" Ya fada yana share mata hawayen dake sauko mata
"Na daina...." Ta fada cikin muryar kuka,murmushi kawai ya saki yana ci gaba da riqeta cikin jikinsa,bai barta ba sai daya tabbatar taci abinci ta kuma sake sannan ya qyaleta.
Kwana goma da rasuwar da wani dare tana zaune gaban anni suna hira,tun dazu khalipha ke kaiwa da kawowa tsakanin sashen annin zuwa nasu,ya gaji yakai maqura yau haqurinshi ya qare,so yake ya dauki matarshi kawai su wuce gidansu amma ayshan tayi qememe kamar ma bata gane me yake nufi,sake miqewa yayi ya nufi sashen cikin qwarin agwiwa.
"Ya khalipha?,me yake faruwa?,me ake haka a gidan?" Ta tambayeshi cike da tsoron amsar da zata fito daga bakinsa
"Kinga saukarmu kenan nace bari na kawoki kiga jikinsa don hankalinki yafi kwanciya,wataqila maqota ke wani sha'anin koma daurin aure ake ne,amma kinsan me za'ayi?,shiga ciki ina nan ina jiranki idan kun gaisa saiki fito mu tafi"
"To" tace tana fitowa bayan ya bude mata murfin motar da kanshi,haka kawai ta dinga jin kamar zata fadi qafafunta sunyi laushi kamar ba'a jikinta ba haka ta dinga takawa har cikin gidan.
Anni ta soma cin karo da ita,mamaki dukka saiya kamata,meya kawo anni gidan to me akeyi?,ko dama ta sansu?
"Allah ya jiqan alhj,ba shakka anyi babban rashin da aka jima ba'ayi irinsa ba" kunnenta ya dauko mata muryar wani daga can wata rumfa dake bayanta da yazo gaisuwa,bata gama wannan ba ta dinga jiyo ihun asma'u tana kiran sunan daddy,da hanzari ta taka don shiga tabi ba'asin meke faruwa sai taji gangar jikinta ta kasa daukarta,ji tayi tana sulalewa zuwa qasa,daga haka bata sake sanin abinda ke faruwa ba.
Sanda ta farka dakin ta dinga bi da kallo sai daga bisani ta gane a asibiti take,a hankali abinda ya faru ya dawo mata kanta,saita fashe da kuka tana fadin
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" a hankali wanda hakan shi ya fargar da khalipha dake saman abun sallah cewar ta farka,gaba daya hankalinshi a tashe yake cikin hanzari ya isa gabanta anni dake zaune can kan kujera ta taso itama,ta dakatar da khalipha dake shirin dagata ta zauna,saiya fasa ya tsaya saitin kanta yana shafa sumar kanta a hankali yana tayata fadin innalillahin,har tsahon wani lokaci bai hanata kuka ba hakanan basu fasa maimaita innalillahin ba tare dashi,daga bisani ne ta saki ajiyar zuciya tana cewa
"Da gaske ya khalipha daddy ya mutu?,dama sallama jiya mukayi dashi kenan a waya?" Ganin shima ba wani a nutse yake can ba saboda yanayin da ayshan ke ciki ya sanya anni matsowa
"Allahn daya haliccemu shi ya fimu sonshi,ya kuma fimu sanin dalilin daya sanya ya dauke abinshi,kada mu yiwa Allah daya bamu shi butulci"
Kai kawai take gyadawa tana ci gaba da ambaton sunan Allah,wanda shi ya dafa mata ta samu nutsuwa,sai da anni ta tabbatar ta nutsu sannan ta taimaka mata ta tashi ta zauna,khalipha ya sanya daya daga cikin yaranshi suka yiwa likitar magana,macace likitan dalili kenan ma daya sanya khaliphan ya kawota wannan asibitin,ta tabbatar mishi komai ya koma normal,saidai ta kiyaye damuwa da bacin rai ta rubuta sallama.
Gidan anni suka wuce kai tsaye tayi wanka,saidai har a sannan hankalinta bai jikinta,ta matsa sai an kaita can gidan makokin,haka khalipha ya dauketa ya kaita.
Karon farko data sake sallamawa Allah lamuranta ta tabbatar lallai mutum koshi waye ba'a bakin komai yake ba,kwana daya tak mummy da asma'u sunfi kowa fita hayyacinsu,tausayin kanta da tausayinsu ya kamata,kuka ta dinga sosai ta manta da duk wani sharadi na likita,anty safiyyace kawai mai qarfin halin lallashinsu,ranar mummy ce ke cewa aysha ta yafe mata,saboda gabanta ita da asma'u daddy ya rasu,sun tsorata matuqa da yadda mutuwa take,fitar rai ba wasa bane,kowanne dan adam lallai saiya taba yaji a jikinsa,saidai fata Allah yasa mu dace.
A nan khalipha yake barinta,kullum sai dare yake zuwa ya dauketa su koma gida,har a sannan aysha bata daina kukan rasuwar daddy ba,saidai tanayi a boye yadda khalipha bazai gani ba hankalinsa ya tashi,don dukkan wani qoqari nasa yana yi don ganin ta sake,saidai ita kanta batasan ma meke damunta ba,hatta da taste din bakinta ya sauya tun daga randa akayi mutuwar.
Ranar sadakar uku su inna yelwa suka zo,tunda sukazo aysha ta lura da ta sauya gaba daya,sai da ana hira takejin bata da cikakkiyar lafiya kwana biyu,yau da lafiya gobe babu,ba'ayi azahar ba umminta ta iso itama ita dasu basma,don ita kanta mutuwar ta daketa,taso qwarai ace Allah ya hada ganawarsu da mutumin daya ceci rayuwar 'yarta,taso sosai tayi masa godiya koda sau daya ne a rayuwarta amma Allah bai nufa ba.
Shuru dakin da suke zaune ya dauka gaba daya,baka jiyo komai sai muryar wata baiwar Allah dake harabar gidan tana wa'azi kan mutuwa,tun daga sanda mala'ikan mutuwa dubi bawa,zarar rai,wankan gawa kwanciyar kabari da yadda mala'iku kebi suna jin yadda jama'a ke fadar halayyar mamaci,da yadda hakan yake tasiri a kansa da sauransu,sosai jikin inna yelwa ya sake laqwas,tunda tazo gidan bata ji mutum daya daya fadi mummunan hali akan daddy ba,yau ga inna yelwa ga ummi,abinda ya dauki tsahon shekaru rabon daya faru,sai inna yelwa ta kasa sakewa gaba daya,sai satar kallon ummi take,ba dadewa fa fashe da kuka,ita kadai tasan me take ji a lokacin,ba abinda take tunawa sai abinda ta aiwatar a rayuwarta a baya,yanzu idan mala'ikan daukar rai ya cimmata fa?,tabbas tasan kadanne masu fadin alkhairi a kanta,idon kowa sai yayi kanta,Allah yasa dukka 'yan takai ne da wadanda suka jibanci aysha,anzo mata sosai saboda yanzun kowa neman fada yake da ita
"Don girman Allah ki yafemin naja'atu,wallahi na cuci kaina na cuci rayuwarki keda diyarki" abinda inna yelwa ta dinga fada kenan tana zabga kuka da majina,tsit dakin yayi,yayin da ummi tayi shuru tana hadiyar wani abu mai tauri,zuciyarta quna kawai take tana yunqurin danneta da cika alqawarin data dauka a gaban dakin Allah.
Inna yelwa ta jima gaban ummi tana kuka gami da gaya mata ita ta rabata da baffale,ita ta shiga tsakaninsu,lumshe idanu ummi kawai tayi,zuciyarta nason tuna mata irin abubuwan da inna yelwan tayi mataba rayuwa,yayin da daya sashen na zuciyarta ke tunasar da ita ni'ima baiwa da kuma musanyan alkhairi da Allah yayi mata ayanzu
"Na yafe miki" kalmar data baiwa inna yelwan mamaki,don bata taba tsammatar haka daga wajen ummin da sauqi ba,hakan ya sake karya mata zuciya,nadama ta shigeta sosai,tana son kallon aysha dake zaune waje daya tana jan carbi tace ta yafe mata amma tana jin kunyarta da nauyinta,tana jin idan tace ta yafe matan tamkar ta zama mai son kai ne,amma ita kadai tasan yadda akwanakin take yawan mafarkin baffale,yana kuka yana ta cuci su aysha,ta gaggauta hada tsakaninsu,ta gaggauta neman afiya da yafiyarsu,ta raba uwa da 'ya,saidai kuma cikin kyakkyawan yanayi take ganinshi,saidai kukan kawai da yake mata,babu randa zata kwanta bacci ta tashi batayi mafarkinsa ba,abun ya takurata qwarai,kusan shi ya haifar mata da lalurar da take fama da ita a yanzu.
"Nasan ban cancanci ki yafemin ba indo,amma na gamaki da Allah duk sanda kike jin kin huce na cancanci yafiya toki yafemin" ta fada tana fashewa da kuka,kai aysha ta kada kawai,itakam me zata cewa Allah banda godiya,komai aduniya da zai samu bawa koya sameshi yana damfare da yanayin rayuwarshi na baya,ba don qalubalen data fuskanta ba da babu lallai daddy ya daukota ya kawota nan,da bai kawota din ba da babu lallai asma'u ta hadata da khalipha,duk da yakedai duk inda bawa yake rabonsa baya kubuce masa
"Na yafemiki,Allah ya yafe mana gaba daya" kusan wannan shi ya kawo daidaito tsakanin gabar inna yelwa da ummi naja'atu.
Qarfe hudu da minti ashirin na yammaci yasa aka kira mishi ayshan,can wani waje da babu kowa cikin gidan suka zauna saman darduma,ya tsareta da idanunshi bayan ya aje abinci a tsakiyarsu,saita zuba mishi ido itama sonshi da qaunarshi na sake karyar mata da zuciya,hawaye ya cika idanunta,haka kawai take jin wani abu ya cunkushe mata wuya wanda shike hanata cin abinci
"Oya,bude bakin" ya fada bayan ya debo abincin a cokali yakai bakinta,sai kawai ta sake masa kuka mara sauti sai sheshsheqa
"Ya salam" ya fada yana aje cokalin cikin damuwa,ya rasa me yasa har yau zuciyarta taqi saki,a yanzun kuka baiyi mata wani wuya,yanzu yanzu ne zata saki abinta,bai manta ba jiya suna kici kicin tahowa zai kawota,zata sanya wata riga taqi shigarta tayi mata kadan,sai zuwa yayi ya sameta a zaune dirshan tana sharbar kuka abinta,daga lallashi nan ma cibi ya zama qari,hannunshi ya miqa mata batayi wata wata ba ta taho,cikin jikinsa ya sanyata tana shafar bayanta a hankali
"Uwaisha ba zaki sanya haquri cikin zuciyarki ba ehmm?,bakisan yadda zuciyata ke quna ba a duk sa'in dana ganki cikin damuwa?,so kike wani abu nima ya sameni?" Saita fashe da kuka tana girgiza kai tana fadin a'ah
"Ya Allahu.....kin zama makokiya gaba daya?" Ya fada yana share mata hawayen dake sauko mata
"Na daina...." Ta fada cikin muryar kuka,murmushi kawai ya saki yana ci gaba da riqeta cikin jikinsa,bai barta ba sai daya tabbatar taci abinci ta kuma sake sannan ya qyaleta.
Kwana goma da rasuwar da wani dare tana zaune gaban anni suna hira,tun dazu khalipha ke kaiwa da kawowa tsakanin sashen annin zuwa nasu,ya gaji yakai maqura yau haqurinshi ya qare,so yake ya dauki matarshi kawai su wuce gidansu amma ayshan tayi qememe kamar ma bata gane me yake nufi,sake miqewa yayi ya nufi sashen cikin qwarin agwiwa.