Sashe 5
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yana fita duka suka taso inda yake,da hannu ya tsaidasu kafin ya daga kai ya dubesu
"Mota daya ta isheni da driver,zaku jira mahmoud tare zaku tafi,zan taho daga baya" kai auka jinjina suna janyewa,yayin daya bude motar da kanshi ya shige gidan baya,drivan motar ya shiga ya tasheta suka bar harabar makeken gidan.
Layuka biyu suka rage kafin ya qarasa layin gidan nasu ya bashi umarnin ya saukeshi ya kuma jirashi a nan,ba musu ya tsaya kaman yadda ya umarceshi,ya bude ya fice.
Sannu a hankali yake takawa,shi kansa yana jin dadin takawar da yake,saboda ko banza ya motsa gabbansa,ba kamar baya ba da motar ita ta zame masa qafafunsa,sauqin abun daya bai da lalaci,duk safiyar duniya sai ya shiga dakin dake bangarensa,wanda ke cike sa nau'in qarafuna da na'urori na motsa jiki da qara lafiya.
Plashing yayi bugu biyu ya katse,shi kansa sai da dariya ta subuce masa
"Shame on you khalipha,wai yau kaine da yin plashing,Allahu yahdik" ya furta a zuciyarsa yana sakin murmushi gami da ranqwashin tsakiyar kansa,fitowarta ita yasa ya maida hankalinsa ga qofar gidan,tayi kwalliya sosai cikin atamfarta
"Sannu da zuwa" ta furta tana wuwwulga ido kaman mai neman wani abu,amma sai ta basar saboda jin kanta da take a mace mai aji
"Yauwa barka da fitowa"
"Ina kuma abun hawan yau?" Ta tambaya kai tsaye tana dubanshi,wani abu mai kama da mamaki yaso mamayarsa amma sai yayi hanzari kau da shi yace
"Kinsan qarfen nasara bashi da tabbas,yau yaqi tashi kawai sai na yanke na taho a na haya"
"Kan bala'i,ana wata ga wata" ta furta qasa qasa,sarai ya jita amma sai yace
"Na'am,me kika ce?"
"Babu komai,shigo daga ciki" ta fada ranta a alamun bace,bai musa ba yabi bayanta har setting room din gidan,duk da cewa ba baqonsa bane gidan da zuwanshi kusan na uku kenan,kallon farko zuwa na biyu zaka yankewa maxauna gidan ajin rayuwar da suke ciki,ba alamun suna cikin talauci,dukkan wata alama ta rufin asiri akwaita a gidan,kaman yadda ya tsammaci akwai tarbiyya gwargwado gidansu khadijan.
Nan ta masa sauki ta gabatar masa da abun motsa baki kamar kullum,saidai abinda ya fuskanta abinda aka kawo masa jiya idan ya sake zuwa yawansu da tsadarsu kan ragu,idan cake da doghnout da lemo yaci to zuwa na gaba doughnout da lemo kawai zai samu,yasan bai taba baiwa khadijan komai ba,haka itama bata taba roqarsa ba,saidai amma ya lura duk sanda sukayi sallama zai tafi ba tare da ya miqo komai ba yakanga bacin rai qarara a fuskarta,har idan ya koma gida ya kirata da zummar gaya mata ya iso bata dagawa,saidai duk ya share wannan bai sanyashi a babin komai ba.
Tun kafin aci talata da laraba a hirar tasu ta gyara zamanta tare da sake lanqwashe murya
"Ammm....dama muhammad akwai maganar da nakeso muyi"
"Ina saurarenki" ya fada yana harde qafafunshi waje guda tare da zuba mata idanunsa,haka nan taji ya mata kwarjini,abinda take yawan tunani kenan,me yasa yake yawan cika mata ido,wanda wannan dalilin yasa tun zuwansa na farko dana biyu data fuskanci ba kalar wanda take lalube bane ta kasa masa bayani,janye qwayar idanunta tayi cikin dakiya tace
"Dama.....biki zamuyi na wata qawata,so an fidda anko nakeso ka yimin" janye yatsansa dake saman lebansa yayi ya dan motsa jikinsa kadan sannan yace
"Kaman nawa ne kudin how much?" Sai da tayi rolling qwayar idanunta sannan tace
"Dubu talatinma is enought,idan son samu ne kuma 40k" murmushi ya qwace masa saidai iya shi da zuciyarsa,ba kudin data tambaya bane suka bashi mamaki don ba matsalarsa bane,don a yanzun haka akwai ninkinsu a wajensa,wanda ya fito da su ne yau dan ya mata kyauta matuqar ta sake tsallake yau din bata nemi komai daga wajensa ba,mamakinsa shine yadda yarinya budurwa da bata rasa ci sha da sutura daga gidansu ba take iya duban qwayar idon namiji ajnabinta ta roqeshi kudin da zata dinka suturawa jikinta haka kanta tsaye ba kunya,tamkar ta bashi ajiya ne,kai yake kadawa a hankai zuciyarsa na gaya masa bata gama cin jarabawa ba ba shakka
"Ya naji kayi shiru ne?" Ta tambayeshi tana dan bata rai gami da fiddo ido waje
"A'ah babu komai,kawai....gani nayi kudin basuyi yawa ba?" Tsaf ta dinke girar sama da qasa
"Just 30 to 40k dinne sukai yawa?,ko iyawa ne ba zaka yi ba?,thank god da ba'a gaban qawayena bane da nake cika musu kanka da naji kunya" murmushi ya saki yana miqewa tsaye
"Ba zakiji kunya ba in sha Allahu zan shiga na fita,amma sai kin danmin haquri kadan kinsam abinka da almajiri mai nema"
"Ba damuwa indai zasu samun,amma kar su wuce nan da one week don Allah" ta qarashe maganar a shagwabe,kai kawai ya iya jinjinawa mamaki na kasheshi,haka tayi masa rakiya har qofar gida yau cike da kulawa sannan ta juya ta koma,shi kuma yaci gaba takawa yana juya abinda ya faru tsakaninsa da khadijan har ya isa bakin motar,wanda tuni driver ya bude masa ya shige shi kuma ya maidata ya rufe sannan ya shiga mazauninsa ya tada motar suka bar unguwar.
"Ashe duk kanwar jaa ce?" Ya fada qasa qasa cikin sigar tambayar kansa da kansa bayan ya ciro sabbin kudaden dake aljihunsa ya qare musu kallo ya watsasu cikin wata ma'ajiyar dake motar ya maidata ya kulle yana sauke ajiyar zuciya,kansa ya shafa sau biyu yana kiran sunan Allah sannan ya maida idanunsa ya lumshe yana aje numfashi
*DAURIN BOYE*
*NA*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(home of expert and perfect writers)
0⃣5⃣
A hankali take takowa bayan fitowarta daga kitchen dauke da babban tray data shiryo abincin daddy a kai zuwa inda yake zaune yana faman rubuce rubuce cikin wasu takardu,yayin da gimbiyar tasa hajiya sa'adatu mommy ke zaune gefanshi cikin kwalliya tana aikin duba tashar da zata dace da kallonta.
Duk da yawan ma'aikatan dake gidan hakan sam bai damu ayshatu ba ko ya tsone mata idanu,takan bata lokaci aduk sadda take da dama tayi girkin da zata ciyar da mutanen gidan,musamman daddy mutumin dake da qima a idanunta,mutumin da take masa kallon mahaifi,kai tana iya cewa abinda yayi mata ko mahaifin da yayi silar kawota duniya baiyi mata shi ba,don ba zata iya cewa yau ga dadin da mahaifi yake da shi ba.
Gabansa ta aje tray din cikin nutsuwa a ladabce,ya dan daga kansa ya dubeta fuskarshi washe da fara'a
"Sannu indon baffale" murmushi ta saki saboda kiranta da wani suna daya shude can baya cikin tarihin rayuwarta,sai ta duqad da kanta ta koma can baya ta rabe daura da momy,tana jira ya bata dama ta sanar masa tafiyarta qauye da takeso tayi gobe asabar ta dawo litinin tunda bata da makaranta ranar litinin din.
Asma'u ce ta fito daga dakinta sanye da dogon wando da riga 'yar qarama mai gajeran hannu,sai ta dora top wadda takai har saman gwiwarta,kunnenta sanye da earpiece kaman yadda yake kusan al'adarta kenan ko da yaushe,kanta babu dankwali sai yalwataccen gashinta mai tsaho dake fake cikin ribbom,a shagwabe ta qaraso gaban iyayen nata ta zube a gaban daddyn
"Daddy....tun shekaran jiya ka dawo har yau zuwa fa banga alqawari na ba"
"Hmmm,bake kadai ba,nima shiru nake ji har yau ba'a cemin komai ba,safina ma tayo waya tana jira amma duk daddy ka mana shiru"inji mummy sa'adatu ta fada tana ci gaba da sauya tasha,takaddun ya tattara gefe daya kana daga bisani ya cire gilashin idanunsa yana murmushi
" kowa sai daya min qorafin saqonsa shiru,ayshatu ce har yau banji ta fadi komai ba"murmushi aysha tayi tana sadda kanta qasa,ita awa?,wanne saqo ma ta baiwa daddyn?,iya alfarmar da ya yiwa rayuwarta kadai ta isheta har abada,ta gefan asma'u kuwa fuska ta kwabe tana dan bata rai,ta tsani daddy ya dinga hada yarinyar da su sam,tana ganin bata cancanci jerawa da su ba,yayin da hajiya sa'adatu ta dan tabe baki gami da dauke kai a fakaice,wanda ba kowa bane zai kula da hakan,bai sake cewa komai ba ya kira waya ya bayar da umarni,cikin mintina biyu daya daga cikin amintattun yaran gidan ya shigo jaye da akwati da kuma wata babbar jaka ya dire a falon ya juya ya fice.
Saukowa yayi qasa carfet din ya janyo jakar ya soma kici kicin zugeta hadi da fadin
"Ai gwara na sallameku na huta kada ku cinyeni danye" dukkansu sai da sukayi dariya,kasancewarsa mutum mai barkwanci a wasu lokutan,amma fa idan ya murde sam bashi da dadin sha'ani.
"Mota daya ta isheni da driver,zaku jira mahmoud tare zaku tafi,zan taho daga baya" kai auka jinjina suna janyewa,yayin daya bude motar da kanshi ya shige gidan baya,drivan motar ya shiga ya tasheta suka bar harabar makeken gidan.
Layuka biyu suka rage kafin ya qarasa layin gidan nasu ya bashi umarnin ya saukeshi ya kuma jirashi a nan,ba musu ya tsaya kaman yadda ya umarceshi,ya bude ya fice.
Sannu a hankali yake takawa,shi kansa yana jin dadin takawar da yake,saboda ko banza ya motsa gabbansa,ba kamar baya ba da motar ita ta zame masa qafafunsa,sauqin abun daya bai da lalaci,duk safiyar duniya sai ya shiga dakin dake bangarensa,wanda ke cike sa nau'in qarafuna da na'urori na motsa jiki da qara lafiya.
Plashing yayi bugu biyu ya katse,shi kansa sai da dariya ta subuce masa
"Shame on you khalipha,wai yau kaine da yin plashing,Allahu yahdik" ya furta a zuciyarsa yana sakin murmushi gami da ranqwashin tsakiyar kansa,fitowarta ita yasa ya maida hankalinsa ga qofar gidan,tayi kwalliya sosai cikin atamfarta
"Sannu da zuwa" ta furta tana wuwwulga ido kaman mai neman wani abu,amma sai ta basar saboda jin kanta da take a mace mai aji
"Yauwa barka da fitowa"
"Ina kuma abun hawan yau?" Ta tambaya kai tsaye tana dubanshi,wani abu mai kama da mamaki yaso mamayarsa amma sai yayi hanzari kau da shi yace
"Kinsan qarfen nasara bashi da tabbas,yau yaqi tashi kawai sai na yanke na taho a na haya"
"Kan bala'i,ana wata ga wata" ta furta qasa qasa,sarai ya jita amma sai yace
"Na'am,me kika ce?"
"Babu komai,shigo daga ciki" ta fada ranta a alamun bace,bai musa ba yabi bayanta har setting room din gidan,duk da cewa ba baqonsa bane gidan da zuwanshi kusan na uku kenan,kallon farko zuwa na biyu zaka yankewa maxauna gidan ajin rayuwar da suke ciki,ba alamun suna cikin talauci,dukkan wata alama ta rufin asiri akwaita a gidan,kaman yadda ya tsammaci akwai tarbiyya gwargwado gidansu khadijan.
Nan ta masa sauki ta gabatar masa da abun motsa baki kamar kullum,saidai abinda ya fuskanta abinda aka kawo masa jiya idan ya sake zuwa yawansu da tsadarsu kan ragu,idan cake da doghnout da lemo yaci to zuwa na gaba doughnout da lemo kawai zai samu,yasan bai taba baiwa khadijan komai ba,haka itama bata taba roqarsa ba,saidai amma ya lura duk sanda sukayi sallama zai tafi ba tare da ya miqo komai ba yakanga bacin rai qarara a fuskarta,har idan ya koma gida ya kirata da zummar gaya mata ya iso bata dagawa,saidai duk ya share wannan bai sanyashi a babin komai ba.
Tun kafin aci talata da laraba a hirar tasu ta gyara zamanta tare da sake lanqwashe murya
"Ammm....dama muhammad akwai maganar da nakeso muyi"
"Ina saurarenki" ya fada yana harde qafafunshi waje guda tare da zuba mata idanunsa,haka nan taji ya mata kwarjini,abinda take yawan tunani kenan,me yasa yake yawan cika mata ido,wanda wannan dalilin yasa tun zuwansa na farko dana biyu data fuskanci ba kalar wanda take lalube bane ta kasa masa bayani,janye qwayar idanunta tayi cikin dakiya tace
"Dama.....biki zamuyi na wata qawata,so an fidda anko nakeso ka yimin" janye yatsansa dake saman lebansa yayi ya dan motsa jikinsa kadan sannan yace
"Kaman nawa ne kudin how much?" Sai da tayi rolling qwayar idanunta sannan tace
"Dubu talatinma is enought,idan son samu ne kuma 40k" murmushi ya qwace masa saidai iya shi da zuciyarsa,ba kudin data tambaya bane suka bashi mamaki don ba matsalarsa bane,don a yanzun haka akwai ninkinsu a wajensa,wanda ya fito da su ne yau dan ya mata kyauta matuqar ta sake tsallake yau din bata nemi komai daga wajensa ba,mamakinsa shine yadda yarinya budurwa da bata rasa ci sha da sutura daga gidansu ba take iya duban qwayar idon namiji ajnabinta ta roqeshi kudin da zata dinka suturawa jikinta haka kanta tsaye ba kunya,tamkar ta bashi ajiya ne,kai yake kadawa a hankai zuciyarsa na gaya masa bata gama cin jarabawa ba ba shakka
"Ya naji kayi shiru ne?" Ta tambayeshi tana dan bata rai gami da fiddo ido waje
"A'ah babu komai,kawai....gani nayi kudin basuyi yawa ba?" Tsaf ta dinke girar sama da qasa
"Just 30 to 40k dinne sukai yawa?,ko iyawa ne ba zaka yi ba?,thank god da ba'a gaban qawayena bane da nake cika musu kanka da naji kunya" murmushi ya saki yana miqewa tsaye
"Ba zakiji kunya ba in sha Allahu zan shiga na fita,amma sai kin danmin haquri kadan kinsam abinka da almajiri mai nema"
"Ba damuwa indai zasu samun,amma kar su wuce nan da one week don Allah" ta qarashe maganar a shagwabe,kai kawai ya iya jinjinawa mamaki na kasheshi,haka tayi masa rakiya har qofar gida yau cike da kulawa sannan ta juya ta koma,shi kuma yaci gaba takawa yana juya abinda ya faru tsakaninsa da khadijan har ya isa bakin motar,wanda tuni driver ya bude masa ya shige shi kuma ya maidata ya rufe sannan ya shiga mazauninsa ya tada motar suka bar unguwar.
"Ashe duk kanwar jaa ce?" Ya fada qasa qasa cikin sigar tambayar kansa da kansa bayan ya ciro sabbin kudaden dake aljihunsa ya qare musu kallo ya watsasu cikin wata ma'ajiyar dake motar ya maidata ya kulle yana sauke ajiyar zuciya,kansa ya shafa sau biyu yana kiran sunan Allah sannan ya maida idanunsa ya lumshe yana aje numfashi
*DAURIN BOYE*
*NA*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(home of expert and perfect writers)
0⃣5⃣
A hankali take takowa bayan fitowarta daga kitchen dauke da babban tray data shiryo abincin daddy a kai zuwa inda yake zaune yana faman rubuce rubuce cikin wasu takardu,yayin da gimbiyar tasa hajiya sa'adatu mommy ke zaune gefanshi cikin kwalliya tana aikin duba tashar da zata dace da kallonta.
Duk da yawan ma'aikatan dake gidan hakan sam bai damu ayshatu ba ko ya tsone mata idanu,takan bata lokaci aduk sadda take da dama tayi girkin da zata ciyar da mutanen gidan,musamman daddy mutumin dake da qima a idanunta,mutumin da take masa kallon mahaifi,kai tana iya cewa abinda yayi mata ko mahaifin da yayi silar kawota duniya baiyi mata shi ba,don ba zata iya cewa yau ga dadin da mahaifi yake da shi ba.
Gabansa ta aje tray din cikin nutsuwa a ladabce,ya dan daga kansa ya dubeta fuskarshi washe da fara'a
"Sannu indon baffale" murmushi ta saki saboda kiranta da wani suna daya shude can baya cikin tarihin rayuwarta,sai ta duqad da kanta ta koma can baya ta rabe daura da momy,tana jira ya bata dama ta sanar masa tafiyarta qauye da takeso tayi gobe asabar ta dawo litinin tunda bata da makaranta ranar litinin din.
Asma'u ce ta fito daga dakinta sanye da dogon wando da riga 'yar qarama mai gajeran hannu,sai ta dora top wadda takai har saman gwiwarta,kunnenta sanye da earpiece kaman yadda yake kusan al'adarta kenan ko da yaushe,kanta babu dankwali sai yalwataccen gashinta mai tsaho dake fake cikin ribbom,a shagwabe ta qaraso gaban iyayen nata ta zube a gaban daddyn
"Daddy....tun shekaran jiya ka dawo har yau zuwa fa banga alqawari na ba"
"Hmmm,bake kadai ba,nima shiru nake ji har yau ba'a cemin komai ba,safina ma tayo waya tana jira amma duk daddy ka mana shiru"inji mummy sa'adatu ta fada tana ci gaba da sauya tasha,takaddun ya tattara gefe daya kana daga bisani ya cire gilashin idanunsa yana murmushi
" kowa sai daya min qorafin saqonsa shiru,ayshatu ce har yau banji ta fadi komai ba"murmushi aysha tayi tana sadda kanta qasa,ita awa?,wanne saqo ma ta baiwa daddyn?,iya alfarmar da ya yiwa rayuwarta kadai ta isheta har abada,ta gefan asma'u kuwa fuska ta kwabe tana dan bata rai,ta tsani daddy ya dinga hada yarinyar da su sam,tana ganin bata cancanci jerawa da su ba,yayin da hajiya sa'adatu ta dan tabe baki gami da dauke kai a fakaice,wanda ba kowa bane zai kula da hakan,bai sake cewa komai ba ya kira waya ya bayar da umarni,cikin mintina biyu daya daga cikin amintattun yaran gidan ya shigo jaye da akwati da kuma wata babbar jaka ya dire a falon ya juya ya fice.
Saukowa yayi qasa carfet din ya janyo jakar ya soma kici kicin zugeta hadi da fadin
"Ai gwara na sallameku na huta kada ku cinyeni danye" dukkansu sai da sukayi dariya,kasancewarsa mutum mai barkwanci a wasu lokutan,amma fa idan ya murde sam bashi da dadin sha'ani.