← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 114

Sashe 72

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kafin nayi serving number din ne ta gudu" sake gyara zama yayi sosai,haka nan yake son hirar tasu tayi tsayi,duk da cewa ya sani shine mai.laifin da bai taba nemanta ba
"Amma me yasa baki amsa ba wajen anni?"
"Hakan na nufin zata fahimci baka kirana kenan" ta sake bashi amsa a taqaice a sanyaye,murmushi yayi yana gyada kai,sai yanzu ya gane dalilin da yasa anni bata taba masa fada ba kan bai taba kiran nata ba,tafin hannayensa ya game waje daya,bashi da sauran abin cewa,gashi kuma baison zaman nasu ya qare da wuri haka,sai ya sake bude takardun daya hada matan ya soma zarosu yana mata tambayoyi kan course din da takeyi,batayi qasa a gwiwa ba ta soma bashi amsa daki daki,saidai abu daya ne da bata so shine ya daga kai ya zuba mata idanunshi,faduwar gaba da daburcewa suke sakata,har ta qare maganarta idanunshi a kanta yana gyada kai
"Ma sha Allah" ya fada sanda ya fuskanci ta gama
"Allah ya taimaka"ya fadi yana miqewa,a gajiye yake sosai don fitarsa dazu ba qaramin yawo sukayi ba
"Ameen,na gode,Allah ya saka da alkhairi ya jiqan magabata"
"Ameen" ya amsa cikin jin dadi ya wuce cikin dakin.

Koda ya fito tuni ta miqe saman doguwar kujera,da alama nufinta nan zata kwana,ita kanta tasan qarfin hali ne kawai takeson nunawa,amma tsoron da takeji Allah kadai ya sani,saboda shi kanshi falon yayi mata girma,batason ne a matsayinsa na baqo kuma muhallinsa ne ace ya kwana a nan
"Ki koma inda kika saba kwanciya ki kwana" kafada ta maqale
"Ka barshi zan kwana anan" bai sake ce mata komai ba ya juya ciki.

Duk yadda jikinsa da idanuwansa suka buqatu da barci amma hakan taqi samuwa,yayi juyi saman gadon yafi sau shurin masaki,tunda ya kwanta take masa yawo cikin idanuwanshi,komai yake dawo masa fes game da ita,yanayin daya ganta dazu zuwa yanzu daya shigo ya sameta tana bacci,tsaki yaja ya miqe ya zauna dirshan saman gadon sanda wayarshi ta soma ruri,

Tunda ya kalli number dake yawo yasan lili ce take kiranshi,hatsabibiyar matashiyar budurwar data takura rayuwarshi da sunan tana sonshi,saidai bayan soyayya da take masa tana da burin suyi soyayya irin ta watsewa wadda ita a wajensu ba wani abun aibu bane,tsaki ya kuma ja yana tuna sanda ta keta parlour dinshi a can ta taddashi har cikin dakin gadonshi,tun daga ranar bai sake yadda yabar gidan a bude ba,kashe wayar yayi baki daya bayan yayi rejecting call dinta,sake juyawa yayi ya kwanta rigingine yana addu'ar Allah yasa bacci ya daukeshi,saidai hakan bata samu ba,dole ya sauko daga gadon wani abu na kaikawo a ranshi,toilet ya shiga da niyyar daura alwala ko Allah zaisa ta sanadin haka baccin yazo.

Gefan gadonshi ya dawo ya zauna yana tsane ruwan alwalar,bayan ya gama ya sauke hannun rigarshin,haka kawai ya kasa sake komawa gadonshi,sai ya zura slippers dinsa ya tako a hankali zuwa bakin qofa ya budeta a hankali.

Idanunshi ya shuga wuwwulgawa cikin falon,can ya hangota lokon kujera a takure waje daya kanta na saman gwiwoyinta,qofar ya saki ya taka zuwa cikin falon
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ta fada a zabure tana miqewa sanda taji motsin tsaiwarsa,ta tsorata sosai da sauri ya riqeta yana mamakin tsoro irin nata,ganin taqi nutsuwa waje daya ya sanyashi riqe dukka hannayenta yana fadin
"Calm down nine,khalipha ne" ya qarashe fada da dan qarfi don ya dawo da hankalinta kanshi,ajiyar zuciya ta saki don ta soma bacci ne taji wannan motsin,uwa uba dama a tsorace baccin ya dauketa,bai saki hannunta ba har zuwa dakin sannan ya zame hannayensa,da hannu daya yayi mata nuni na tahau ta kwanta,saita kalleshi sannan ta dubi gadon,ta taka a hankali zuciyarta na bugawa saboda tsoron data ji dazu.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

A nutse ta tura qofar dakin anni bakinta dauke sa sallama don su gaisa,saboda bata samu zama breakfast tare da su ba ta tsaya gyaran sashen nasu,tadai kammala abun karin da tasan zai ishi kowa a gidan ta gyara dining din ta bar sashen,da fara'a saman fuskar anni take sa sallamar tata
"Maraba da takwara" murmushi aysha ta saki har wushiryarta na fitowa,tana yaba yadda annin ke mata,tana jin cewa inama inama ace ita tahaifeta,inama ace itace mahaifiyarta,kanta a qasa saboda ta fuskanci suna wata magana mai muhimmanci ne ita da khalipha wanda ya nutse cikin kujerar dake falon annin yana satar kallonta can cikin zuciyarsa yana mamakin sauyarwarta,waishin dama matan cikin hijabi akwai wani sirri na musamman da suke boyo ne ko kuwa wani abu ne ya sauyata?,iyaka saninshi da ita ba haka take ba,kunnuwanshi na sauraren muryarta da suke magana da anni,ita dinma yana jin kaman ba tata ba,kodai watannin daya diba ne yasa yake ganin komai ya sauya?,har suka gama gaisawa da annin da 'yan maganganunsu baice komai ba,furucin anni na qarshe ne ya dawo dashi
"Karki zauna haka na sanki sarai ki nemi abu kici" kanta ta kada sannan taci gaba da takawa don ficewa daga dakin,sai taji tana son ta harde,ba shakka akwai wani dake kallonta,wani nauyi take ji kamar yau ta saba shigowa falon annin
"Khalipha" anni ta kira sunanshi ganin hankalinsa nai tare da ita,cikin dakewa irin ta gigaggun maza ya soma shafa kanshi kafin ya maida idanunshi a kan annin,cike da basarwa yace
"Anni yarinyar nan tana karatun nan kuwa?" Dariya ke cin anni a qasan ranta,amma a zahiri saita dake gami da bata rai
"Me ka gani?" Kai ya girgiza da sauri,don idan ta tirkeshin kan me ya gani dinma baisan me zaya ce mata ba
"Babu komai"
"Aisai ka fadi abinda ka gani" ta sake fadi tana yin kicin kicin da fuska
"Ba komai anni....na lura bakison laifinta"
"Dole kace haka khalipha saboda kaga na qyaleka kan naka laifin ban tuhumeka ba,duk yadda taso ta boyen nasan abinda ke wakana"haquri sosai ya shiga baiwa annin tare da yi mata bayanin abinda ya kawo tsaikon dawowarshi
"ita zaka je kama wannan bayanin bani ba"ta fada tana miqewa,sai ya miqe tare sa annin yana dariya qasa qasa
"Anni yanzu gwamnatina ta rushe kenan?...."dariya yaso bata,sai taqi cewa komai ta amsa shi a taqaice
"Oho to wa yasani?" Murmushi yayi yana biye da ita duk takunta daya sai daya ga shigarta dakin gadonta sannan yaja mata qofar ya fito.

Tana tsaye cikin kitchen din ta hada corn flakes da madara cikin wani qaramin bowl da alama shi take nufin sha,gefe daya ta dora kankana a kan plate tana yankata qananu qananu itama tana zubata a wani bowl din a haka ya sameta.

Bata ji shigowarshi ba sai inuwarsa data gani a gafenta,jan mayafinta tayi dake niyyar sabulewa daga kanta saboda santsin gashinta,gashin nata ya kalla sannan yaci gaba da kallonta ta gefan fuska,duk saita ta kura,batasan wanne jarabar kallo bane haka wanda da can data sanshi bata sanshi da kallo ba,kafin a daura aurensu idan yazo mata tsahon minti talatin din nan yafi ta'allaqa idanunshi kan wayarshi,a nashi gefan kuwa wani abu daya faru bayan barinsa gida shi ya dinga dawo mishi a kai,nazarin ayshan yake gami da dorata a mizanin da zuciyarshi ta shawarceshi a kai,saidai baiga wata qofa dake nuna tana ra'ayinsa ba bare sukai ga bigiren da zuciyarsa ke hasashen masa,ta yaya zai koya mata sonshi?,ta yaya zabi da ita ta karbeshi ta fuskar da yakeso?,ya tabbatar da cewa irin aysha tun a wancan lokacin dai daikune cikin jinsin 'yammata,faruwar lamarin ya sake tabbatar masa da wannan.

Hannunshi yasa ya dauki cokalin dake cikin madarar yana juya cornflaske din bayan ya dauke idonsa daga kanta wanda take ta faman gutsira kankanar kaman ba zata gama ba
"Wannan shi zakici a matsayin breakfast?" Kai ta gyada ba tare data dubeshi ba,baice mata komai ba saiya dibi cokali daya yakai bakinsa yana taunawa,shi a rayuwarshi har mantawa yake da abin nan,ya manta rabonshi daya cishi,kadan kadan ya dinga diba yana ci sai gashi yana shirin tashi dashi,batasan sanda ta saki baki tana kallonshi ba gaba daya wanda dama shi haka yakeso,aje cokalin yayi sannan ya soka yatsunsa cikin na juna,cikin cool voice dinshi wanda ba hayaniya sam a ciki ya furta
"Am sorry"
"Bayan ka cinyemin abuna?,da kanaso saika fadamin na hada maka wani" murmushi ya saki sai kuma taji kunya da nauyi,kaman gidanmu?,kaman bashi ke aje komai ba?,qasa ta danyi da kanta,kamar ya fuskanci haka saiya jawo locker da suke aje kayayyakin ya dauki wani cup din ya zuba ruwan dumi ya hada mata wani
"Gashinan na biyaki,ke naki ma da ruwan sanyi kika hafa babu dadi,ni kuwa dana dumi nayi miki"
"Na gode" ta fada tana boye murmushin jin kunyar da take
"Kiyi haquri naje na zauna ba tare dana nemeki ba,ni kuma nayi hakanne don na baki damar yin masters dinki cikin nutsuwa,duba da yadda kike qaunar karatunki"
"Babu komai",dukkansu shuru sukayi saboda jiyo tashin wata murya kamar ta rahama na doso kitchen din.

Katsam babu tsammani taji gaba daya taji ya rungumota ta baya hannuwanshi saman cikinta,faduwar gaba da kaduwa suka sameta lokaci daya
"Karki motsa" ya rada mata akunneta wanda sautin da dumin fitar furucin ya ratsa har bargonta
"Khalipha me kakeyi a kitchen?,kaman wanda baida mata" muryar rahama dake cike da iyayi da kwainane ta cika kitchen din,juyowa yayi gaba daya har yanzu aysha na cikin jikinsa
"Tare da matar muke,kinsan se ana mata dure bata son cin abinci,ban sani ba ko baby na ke wahalar da ita" wani abu taji ya daki tsakiyar kanta,maganarsa da yadda ta ganshi manne a jikinta,duk da qoqarin basarwar da take amma hakan.sai daya bayyana saman fuskarta ya sauya duk wata walwalwa data shigo da ita
"Ohkey....ohkey" ta fada cikin murmushin yaqe tana bude frdge ta dauki ruwa ta fice ba tare data sake cewa komai ba.
Chapter 72 · 0% Book details