← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 114

Sashe 47

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana zaune waje daya kawai tunda ta gama nata shirin tana binsu da ido wayarta ta dauki qara,ta duba batasan number ba sai ta daga ta kara a kunneta tayi shuru ba tare data ce komai ba taji waye
"Assalamu alaikum warahmatullah" ta jiyo muryar wata mace dattijuwa,cikin mamaki ta amsa sallamar tana son taji wace
"Ina fata aishatu ce" a ladabce ta amsa saboda yadda muryar ke nuna shekarun mai maganar
"To ma sha Allah....me ya faru na saka khalipha ya turo muku driver ya kaiku,sai naji yana waya da driver yana gaya masa ya dawo kawai?" A take ta gane wace,anni ce duk da cewa baifi sai biyu ta taba jin sunanta daga bakinsa ba,diriricewa tayi gami da tsorata kamar wadda ta yiwa sarko qarya har hakan ya bayyana saman fuskarta,aliya dake gefe wadda ke jin duk abinda ke faruwa saita amshi wayar,gaisawa sukayi sannan tace
"Qawar aysha ce,bamu gane waye ya turoshi ba sai daga bisani....amma yanzun haka ma gab muke da gama shiryawa mu wuce"
"To madalla...na zaci daga khalipha ne...Allah ya tsare hanya...a gaida mutanen gidan"
"Amin zasu ji,mun gode" daga haka ta katse wayar itama aliyan ta sauke tana murmushi qasa qasa,hannu ta saka ta daki bayan ayshan
"Saikin biyani ladan yin lauya....haka zakije ki dinga musu wannan sanyin naki da tsoro?...uwar mijinki ce fa ta kira" idanu aysha ta zaro tana duban aliya
"Ke...uwar mijin wa?...mamana zaki ce,a matsayin yayana yake ni da shi babu zancan miji da mata" idanu aliya ta saka tana kallon ayshan,sai kuma tayi turus ayshan tana duban dakin,Allah yasa su biyu ne su gwaggo sun soma fita da kayansu ana kaiwa mota
"Kaman yaya ban gane ba,yimin bayani...."
"Share kawai" ta fada tana miqewa gami da saba jakarta a kafada,itama aliyan tashi tayi tana rataya tata
"Wallahi baki isa ba yarinya kinyi kadan,tunda kika fara fada dole ki fada duka" murmushi tayi tayi gaba...itama tasan hakanne,ba wani boye boye tsakaninsu,idan ta boye dinma tana da wanda zata gayawa ne daya fita.

A parlour aliya ta toge aysha ta haura sama yiwa mummy sallama
"Mummy zamu wuce...sai mun dawo"a watse ta amsa tana sabgar gabanta,bata damu ba ta miqe ta fito,nan suka ci karo da anty safiyya,da fara'a take dubanta
"yanzu shikenan haka zaki tafi ba dan rakiya?"
"Ba komai anty muna tare da aliya da mero,ga gwaggo asabe ga baaba karima"
"Shikenan....sai ranar lahadin kenan"
"Eh in sha Allahu" ta fada tana duqar da kanta qasa kadan alamar kunya
"To Allah ya nuna mana,don Allah ki gaidasu ,abinne ya hade mana lokaci guda"
"Zasuji anty" har ta juya anty safiyyan tace
"Ammm...aysha zo aliya ta kawo min qararki" waiwayowa tayi ta dawo rana taraddin me ya faru,a tausashe take mata magana
"Bana son inji wata baraka tsakaninki da khalipha,tunda ba wani mugun hali nashi ya boye miki ba sai yanzu ya bayyana,abinda ya farun me yiwuwa haka tsarinshi yake,yaso daukar asma'u amma Allah ya duba ba kalarshi bace bata dace da shi ba sai ya hada tsakaninku,kinsan komai basai na miki bita ba,kuma koda baki fada ba da bakinki kin sani cewa Allah ne ya qwata ya baki,ya lullube asirin komao bada wayon khalipha ko plan dinsa ba,wannan shirin Allah ne,so don Allah aysha banson jin komai"
"In sha Allahu anty...na gode"
"Yauwa Allah ya tsare hanya"
"Amin anty" daga haka suka rabu ita ta sauko qasa ita kuma ta wuce dakin mummy.

Lafiyayyar mota ce data amsa sunanta,hakan ya sanya sukai tafiya mai dadi wanda har mero ta dinga santin ashe hanyar garinsu bata wani rube sosai ba rashin kyawawan motoci yasa suke shan wahala.

Qarfe biyu da mintina takwas suka isa qofar gidan nasu,a hankali aysha take qarewa gidan nasu kallo tana mamakin jama'ar data gani anata shige da fice a gidan,sai tayi tsammamin wani abu ke faruwa don ko kusa ko alama bata kawo cewa bikin aurenta yasa mutane taruwa ba har sai data fito daga motar taga jama'a sun soma yanyameta tare da yi mata maraba lale gami da kiranta da amarya,da mamaki kawai dubansu kamar wasu masu shirin wasan kwaikwayo,kafin kace meye kayanta da aka fito dasu daga booth har an samu masu sunguma sukai cikin gida da shi sannan ita kuma da sauran mutanen da suka tsaya gaban motar suka dunguma zuwa cikin gidan.

Sosai tunani da qwaqwalwarta suka daure da sauyin data taras cikin gidan nasu koma tace a unguwar baki daya,kowa indo yakewa marhaba,kowa indo yake tare,kowa indo yakeson nunawa kulawa,kowa.indo yake so ya raba,kowa ita yakeso ya yiwa magana,shin me ya haifar da wannan gagarumin sauyi haka dare daya?,me yake faruwa ne koko daya daga cikin ire iren mafarkan data saba yi ne tau take yinsu ido biyu,ba aysha kawai ba ba mero da gwaggo asabe da suka san meke faruwa ba hatta da aliya wadda labarin aysha ne kawai ya isketa sai data yi mamakin sauyin data gani.

Mamaki bai sake kamata ba sai sanda inna yelwa ta miqe da kanta ta tareta,ta tareta cikin yanayin da tunda ta budi idanu tasan duniya da abinda ke cikinta bata taba ganinsa ba,cikin kulawa da fara'ar da bata taba ganin makamanciyarta ba daga gareta,da idanu take bin rumfar inna yelwa da ido tunani yana zagaye ilahirin qwaqwalwarta,yadda aka gyara rumfar fes kai baka ce ita bace,aka sabunta ta aka sauya mata kamanni,ta sha leda...ta sha fenti da labulaye harma da kujeru
"Wai meke faruwa?" Ayshan ta tambayi kanta da kanta tana duban aliya kamar ita zata bata amsa,kafada aliya ta daga sannan tace
"Ina zan sani sashen....wannan abun akwai ayar tambaya a kai" tana kaiwa aya wayar aysha dake hannun aliya ta kada qaraurawa alamun shigowar saqo,dubawa tayi don ba komai irin haka a tsakaninsu sun saba
"Karki wani damu da sauyin da zaki gani,anni tayi duk wani abu daya dace saboda ki samu walwala ki sake" aliya ta karanto saqon a fili don mai wayar taji abinda ya qunsa,shuru tayi tana tunani
"Me tayi daya dace?,me ya sauya mutanen nan haka?" Ta sake aikawa da qwaqwalwarta da wannan tambayar,bata kai ga samun amsarta ba matan kawun ta suka soma shigowa,kowacce baki har kunne aka sake sabuwar gaisuwa a gurguje kar inna yelwa ta shigo ta riskesu don ta gargadi kowaccensu da karta shigo bare ta damesu,abun mamaki shine godiyar da suketa sheqa mata kafin kowacce ta miqe ta fice
"Aliya don Allah ki fahimtar da ni abinda ke faruwa mana" ta kama hannun aliya tana fada cikin rudu,don ita har ga Allah tsoro.ma abin yake bata,ko wani abun suke qullawa?,ko wani shiri ne sukayi na daban wanda batasan da shi ba,domin bata tunani akwai abinda zai sauya wadan nan mutanen lokaci guda kai kace umarni ne daga sama
"Babu komai sai alkhairi aysha...karki damu...saqon daya shigo daga khalipha yake,kuma na tabbatar su su khaliphan bazasuyi abinda zasu cutar da ke ba" maganar ita ta kwantar da hankalinta,saidai idanu data sanya tana lura da motsin komai da yadda komai yake gudana,tana iya jiyo shewar cincirindon matan qauyen dake tsakar gidan gidan nasu,sanda aliya ta miqe zata alwala ta daga labule a nan taga manyan tukwanen dake girke a tsakar gidan suna cin wuta,da aliyan ta dawo dubanta tayi
"Na kusa gane abinda anni tayi,anya ba siye mutanen sukai ba?anya ba kudi ne suka sauya komai ba?,aysha shanu biyu aka shigo da su a yanke,ga tarin abinci kala kala a wancan rumbun dake kusa da makewayinku,sannan kowanne cikin gidan nan cikin walwala yake da burin zuwan gobe ranar daurin aure" daga idanu tayi ta kalli aliya sanda take maida pad din data ciri daya zata sauya cikin jakarta
"Hakan ma zata iya faruwa aliya,kin manta ni ba komai bace...zasu iya sadaukar dani saboda abinda baikai wannan bama...." Ta fada tana sauke idanunta qasa qwalla nason qwace mata,dafata aliya tayi sannan tace
"Idan kika lura a yanzu kin zama mai daraja aysha,baki lura da yadda suke kaffa kaffa dake da dukkan lamuranki ba?...dubi kwanukan abinci kin taba gani an jere miki su haka a gabanki daga sashe sashe?,ko wannan ya isa ya gaya miki daraja su anni suka siya miki...kuma ina miki fatan kici gaba da kasance mai daraja ta sanadiyyarsu".

Sai da suka zo kwanciya bayan inna yelwa ta saka musu maganin sauro an yada musu dandamemiyar katifa da bargo sannan dukkansu suka dago manufar sauyi da suka samu
"Indo ina kika samu miji mai arziqi haka?....ashe dai zamu dandana arziqinki....bama 'yan gidan nan ba har maqota...kinsan kaf gidan nan babu wanda yanzu bashi da jari mai tsoka?...sannan kaf dinmu mu da maqota ba wanda bai samu sabon dinki ba da zai saka a gobe?bayan manyan buhunhunan shinkafa da aka bi aka raba musu,sannan rumbunan gidan nan uku kowanne cike yake da cima ta 'yan birni,guda daya yace ayi hidimar biki da shi...saura namu ne muci mu qara idan sun qare za'a dado wasu....ke kanki yasa mun fadi yadda muke bukukuwanmu na al'ada ya biya komai gobe kwana za'ayi ana cashewa,ke ni fa da nake kakarki har kudin liqi sai da aka zubemin in gaya miki,kudina sabbi fil a miqe...." Kanta kawai ta juya daya barin,babu abinda ya burgeta a zubar da inna yelwa keyi,sun sake saida mata dan guntun mutuncin da yayi mata saura,bata sake cewa komai ba tana jin inna yelwar da aliya na sake bugun cikinta tana jin yadda abubuwa suka kasance,mota guda ashe aka yi musu ta saqonsu.

Tashi inna yelwar tayi ta janyo wata babbar akwati ruwan makuba(marroon mai adon dark blue)tana sumbatu
"Ga uban kayan da yace a aje miki indo ko zaki buqata,idan kinzo a baki,kaf karkarar nan da maqotanta ba wadda ta samu adaka irin taki cike da suturu haka,na biye ne saboda masu dauji dai dai nace sai kinzo na danqa miki abarki" kusan aliya ce kawai ta bude tagani,kaya ne aqalla kala goma sha biyu dinkakku,wanda amsa sunansu,takalma jaka mayafai zuwa sarqa da dan kunnaye kowanne kaya da kalar daya dace dashi,kayan kwalliya da duk wani nau'in abu da zata buqata akwai a ciki,jinjina kai aliya take tana qissima tsadar iya wadan nan kayan,sannan a ido kawai kyansu dole ya burge mutum,ba yadda batayibda aysha ta tashi ta gani amma taqi koda motsawa haka ta gaji ta haqura ta qyaleta.
Chapter 47 · 0% Book details