Sashe 41
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta gefan su anty halima kuwa bakuna zuwa jikkuna sun mutu murus,kowacce cikin 'yammatan zuciyarta ta tafi,xasu iya cewa tsahon zamansu da burikansu basu taba shiga gida irin wannan ba....duk cikinsu babu wadda bata ji inama inama ace itace zata shigo gidan ba
"Kutumar uba....mutumin nan fa DON ne wallahi da alama"cewar mufida qanwar mijin anty halima sanda take qarewa gidan kallo karo na barkatai,batasan sau nawa ta kalli gidan ba,babu lungu ko saqo na gidan da bata kashe selfie ba....bama ita kadai ba har sauran yammatan
"amma asma cin kai ce....tace mana fuqara'u wal maskin ne shi?....inaga dai bata gano dai dai ba wallahi" inji nusaiba
"Ni gani nake anya wannan baifi hamid kudi ba?,ko a ina ta somashi?" Fatima qanwar mummy ta fada
"Da Allah ku yiwa mutane shiru kun cika mana kunne da surutan banza da wofi......." Anty halima ta fada cikin zafi da qunar rai,lallai ba shakka khaliphan DAURIN BOYE NE,yazo musu ne a duqunqune kenan?,ita a karan kanta tasan cewa babu gami tsakanin khalipha da hamid,hamid eh lallai yana da kudi....saidai duka basu kai yadda suka zata ba,sun zaci yafi haka,fariya da dagawa da son a sani ya qarawa arziqin nasa ado ake masa kallon yafi haka,yayin da khalipha ya iya takunsa,yake dora komai a muhallinsa da mizanin hankali da nutsuwa.
Hannun nusaiba ya kai kan wani daki wanda shi kadai ne basu buda ba bayan na mai gidan,dakin na manne da bedroom din ayshan,binta sukayi duka a baya "gwara mu kashe qwarqwatar idanunmu...kai....wlh ji nake kamar a mafarki....indo?,indon da tazo daga qauye wai itace da wannan gidan?,anya ba qarya mutumin nan yake mana ba raina mana wayo kawai yake don ya burge ya kawomu gidan jama'a?" Inji anty kubra
"Nima tunanin da nake kenan" anty halima ta fada cikin sanyin jiki gami da tausayawa qanwarta,tasan yanzun zata tashi hankalinta matuqar taji cewa gidan ayshan ya kerewa nata.
Daki ne guda wanda aka shiryawa sif ta jikin bango kowanne gefe da tarin hangers na maqale sutturu,sutturu ne sabbi a dinke iya ganinka babu kalar wanda babu
"Innalillahi....oh my god" nusaiba ta fada tana rufe bakinta da hannunta tana fiddo idanunta,abun yayi masifar burgeta da tafiya da ita,ba ita kadai ba kusan duk wadanda suka shigo dakin,saidai hassada data cika zuciyar wasu daga ciki hakan ua gaza tarihi
"Na shiga uku.....indo ina zata kai wadan nan sutturu?....wannan kuwa zata gama saka su harta mutu?" Cewar mero tana dafe qirji,dariya inna laraba ta saki
"Suttura ai itace mutum kuma bata yawa....kuma bai kai mata lefe ba bawan Allah ashe haka ya tsara zaiyi mata" ta fadi cikin murmushi,kayan suka dinga bi daya bayan daya suna tabawa dubawa da fadin kudin wadanda suka san kudinsa,wanda basu sani ba kuwa saidai hasashe kawai da suke,tun suna dubawa suka gaji suka koma kan jakankuna takalma da mayafai,qarshe haqura sukai da qwaqwqwafinsu suka fito daga wajen bayan sun gama daukar hotuna,a falo suka tadda anty halima zaune wanda tunda ta saka kai dakin sai ta fito da sigar amsa waya bata kuma komawa ba,gefanta kubra ce zaune itama cikin sanyin jiki,bala'i ta hausu da shi kan uban meye suka a wajen,kamar basu taba ganin kaya ba?.
"Halima ina zaton saimu koma haka harda motar kaya ko?,tunda naga gidan babu abinda yake buqata ko cokali kuwa"cewar inna laraba,wani banzan kallo ta juyo ta watsawa matar data darawa ma mahaifiyarta a shekaru
"Ke kinga inna laraba,na gama fuskantar take takenki fa...tunda muka shigo gidan nan kike rawar qafa kina neman gindin zama....shine zaki gayawa mutane magana a fakaice,butulu shekararki nawa kina cin arziqinmu daga ke har indon?,ina cewa badon muba da tuni ana qauye ana fama da kirci da faso?,to mu duk girman arziqi bai rudarmu don mun saba gani ba yau farau ba" maganar ta yiwa inna laraba ciwo qwarai,a ganinta ko babu komai haliman ta girmamata ko don furfurarta,cikin murmushi da danne bacin rai tace mata
"Ki adana fushinki don bani nayi ba Allah ne ya nuna ikonsa a kai....duk wani abu da kuka hana aysha sai gashi yau Allah ya bata ninkinsa....duk abinda kuke zaton bata cancanceshi ba sai gashi yau Allah ya bata sama da shi,kun hanata mota qarama qwaya daya sai gashi Allah ya bata manya biyu,kun bata daki mafi qanqanta a gidan sai gashi Allah ya bata masarauta guda....kun siya mata kayan daki a qasar nan maimakon qasar waje kuma saiti daya sai gashi Allah ya bata wasu fiye da daya fin biyu ma,ya qawata mata gidan aurenta da jin qansa da rahamarsa....kinga kenan ba yina bane yin Allah ne...idan kunga dama ku aje abinda ke ranku ku rungumi yarinyar da bata taba taka muku ba bare ta zubar muku,ba sawa ba futarwa sai ku da kuke amfana ma da ita,baky dubi maraicinta ba,baku dubi rauninta ba kuke gallaza mata da gasata a ruwan sanyi ba tare da duk wani mara dogon nazari da tsinkaye ya fuskanci hakan ba,kun manta cewa Allah ke daukaka bawa a duk sanda yaso,kun manta cewa talaka da mai kudi duka Allah ne ya haliccesu badon yafison wani ba sai wanda yafi biyayya a gareshi,kun manta cewa dan kauye mutum ne mai daraja shima kamar kowa....qauye muhalli ne mai daraja tun a zamanin annabawa?,tunda ko annabinmu an bada shi raino a can,ya rayu da su bai kuma taba qyamatarsu ba,halima wannan ishara ce a gareku,ruwanku ku gayara ruwanku ku dora daga inda kuka tsaya,aysha dai tayi gaba amma zaku iya biyota a baya"miqewa anty halima tayi ta soma zuba ruwan bala'i,duk wani bacin rai dake ranta take furtashi a sannan,su anty kubra ke riqeta amma bata ji bata gani,murmushi inna laraba tayi
"Iyaka a dakatar dani bakin aiki ko?....ki sama ranki to daga nan zan wuce cikin nawa ahalin,karki manta yarona da qafarsa yazo zai tafi da ni mahaifiyarku ta dakatar da shi,ta roqeshi ya barni saboda sabo,ina fata baki manta ba?,abu daya zan gaya miki kafin na wuce shine...kibi ko ince kubi duniya a sannu,a yanzu ishara daya tazo muku...idan baku sauya ba sauran isharorin na nan tafe,bikin indo kuwa har qauyen takai in sha Allahu,na barku lafiya" ta fada tana juyawa nan ta fice ta barsu,anty halima naci gaba da kumfar baki.
*mrs muhammad ce*👑*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN BAKI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING_*
*_LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*_,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*KO KUMA*
(07067124863)
*DB*
25
Bin kowannensu da kallo kawai asma'u take sanda suke zayyanawa mummy yadda suka samu gidan ayshan,jin abun take kamar almara,ji take kaman mafarki,tsaye kawai take ta kasa tabuka komai kamar wadda aka zarewa duk wata laka ta jikinta
"Qarya ne....qarya kuke waini zaku zolaya,ta ina yaron oga zai samu irin wannan gidan?,ni zaku tsokana bayan nafi kowa sanin wayeshi,mtseww" Ta fada tana banka musu harara,nusaiba ce tayi caraf ta ciro wayarta ta soma gwadawa asma'un selfie din da suka sha cikin gidan
"Kanbu" asma'u ta lailayo ashar din kai tsaye cike da baqinciki takaici cakude da hassada,zama tayi da sauri gefan gado kusa da nusaiba
"Who is khalipha?" Ta fada tana tambayar kanta,tabbas babu shakka akwai wani daurin boye dangane da al'amarin,tabbas wannan khaliphan ba shine wanda ta sani ba,akwai wani khaliphan boye a bayan khaliphan data sani,ta yaya zata yadda,ta yaya zata amince aysha ta auri wannan khaliphan?bayan duka yaqin da tayi a baya kan hana faruwar hakan,abinda ya dinga kai komo kenan a zuciyarta,cikin fushi da hanzari ba tare data cewa kowa komai ba ta fice daga dakin,tana jin kamar iska ke tafe da ita ba qafafunta ba.
"Aisha....kinga baiwar da Allah yayi miki kuwa?,kinga gidanki aisha?,dama mai kudi zaki aura?" Mero ke fadin haka cikin tsantsar farinciki tana riqe da hannun aishan,sosai takejin dadi kamar ita zata zauna cikin gidan.
Sam bata kawo komai ba tayi murmushi
"Mai rufin asiri dai mero,shima talaka ne kamarmu" idanu mero ta zaro tana dubanta
"Talaka?,alqur'an kada bakinki ya sake fadin cewa shima kamarmu yake,kinsan yadda sama ta yiwa qasa nisa?,to kwatankwacin haka tazarar mu da shi take,kinga gidanki kuwa indo?....bari kigaa a wayata duk da bai dauku da kyau ba" mero ta fada tana ciro 'yar qaramar torching dinta da mijinta ta saya mata wancan wata bayan ya saida amfanin gonarsa ya samu riba mai yawa.
Dariya take kawai a sanda ta karbi wayar don tana zaton zuzuta abu ne kawai irin na meron,a ido gidan ya qayatar da ita sanda take kallon hotunan,saidai sam bata kawo kanta a ciki ba
"A ina kika samo wadan nan hotunan mero?" Aysha ta tambayeta
"Hotunan gidanki ne da muka je yanzu indo...indo ki godewa Allah,Allah ya miki ni'ima da baiwa wallahi,ba shakka Allah ya fanshe miki wahalarki ta shekara da shekaru,yanzu haka kaf kayan jeranki mun dawo dasu saboda babu wajen da zamu zuba su,hasalima wadanda muka tarar jere a gidan sai namu ya tashi kaman a bola muka tsintosu" dariya sosai aysha ta saki,labarin sai ya nishadantar da ita,don har ga Allah bata yarda da gaske mero take ba,ta daukeshi kawai a shaci fadi ko nishadi takeson sanyata saboda taga alamun damuwa tattare da ita tun dazun kafin su fita,ita kuma ba wannan ne a ranta ba,ummanta take son gani,labarin ummanta takeson ji,kulawa take buqata ta gani daga wajen umminta komai qanqantarta.
"Kutumar uba....mutumin nan fa DON ne wallahi da alama"cewar mufida qanwar mijin anty halima sanda take qarewa gidan kallo karo na barkatai,batasan sau nawa ta kalli gidan ba,babu lungu ko saqo na gidan da bata kashe selfie ba....bama ita kadai ba har sauran yammatan
"amma asma cin kai ce....tace mana fuqara'u wal maskin ne shi?....inaga dai bata gano dai dai ba wallahi" inji nusaiba
"Ni gani nake anya wannan baifi hamid kudi ba?,ko a ina ta somashi?" Fatima qanwar mummy ta fada
"Da Allah ku yiwa mutane shiru kun cika mana kunne da surutan banza da wofi......." Anty halima ta fada cikin zafi da qunar rai,lallai ba shakka khaliphan DAURIN BOYE NE,yazo musu ne a duqunqune kenan?,ita a karan kanta tasan cewa babu gami tsakanin khalipha da hamid,hamid eh lallai yana da kudi....saidai duka basu kai yadda suka zata ba,sun zaci yafi haka,fariya da dagawa da son a sani ya qarawa arziqin nasa ado ake masa kallon yafi haka,yayin da khalipha ya iya takunsa,yake dora komai a muhallinsa da mizanin hankali da nutsuwa.
Hannun nusaiba ya kai kan wani daki wanda shi kadai ne basu buda ba bayan na mai gidan,dakin na manne da bedroom din ayshan,binta sukayi duka a baya "gwara mu kashe qwarqwatar idanunmu...kai....wlh ji nake kamar a mafarki....indo?,indon da tazo daga qauye wai itace da wannan gidan?,anya ba qarya mutumin nan yake mana ba raina mana wayo kawai yake don ya burge ya kawomu gidan jama'a?" Inji anty kubra
"Nima tunanin da nake kenan" anty halima ta fada cikin sanyin jiki gami da tausayawa qanwarta,tasan yanzun zata tashi hankalinta matuqar taji cewa gidan ayshan ya kerewa nata.
Daki ne guda wanda aka shiryawa sif ta jikin bango kowanne gefe da tarin hangers na maqale sutturu,sutturu ne sabbi a dinke iya ganinka babu kalar wanda babu
"Innalillahi....oh my god" nusaiba ta fada tana rufe bakinta da hannunta tana fiddo idanunta,abun yayi masifar burgeta da tafiya da ita,ba ita kadai ba kusan duk wadanda suka shigo dakin,saidai hassada data cika zuciyar wasu daga ciki hakan ua gaza tarihi
"Na shiga uku.....indo ina zata kai wadan nan sutturu?....wannan kuwa zata gama saka su harta mutu?" Cewar mero tana dafe qirji,dariya inna laraba ta saki
"Suttura ai itace mutum kuma bata yawa....kuma bai kai mata lefe ba bawan Allah ashe haka ya tsara zaiyi mata" ta fadi cikin murmushi,kayan suka dinga bi daya bayan daya suna tabawa dubawa da fadin kudin wadanda suka san kudinsa,wanda basu sani ba kuwa saidai hasashe kawai da suke,tun suna dubawa suka gaji suka koma kan jakankuna takalma da mayafai,qarshe haqura sukai da qwaqwqwafinsu suka fito daga wajen bayan sun gama daukar hotuna,a falo suka tadda anty halima zaune wanda tunda ta saka kai dakin sai ta fito da sigar amsa waya bata kuma komawa ba,gefanta kubra ce zaune itama cikin sanyin jiki,bala'i ta hausu da shi kan uban meye suka a wajen,kamar basu taba ganin kaya ba?.
"Halima ina zaton saimu koma haka harda motar kaya ko?,tunda naga gidan babu abinda yake buqata ko cokali kuwa"cewar inna laraba,wani banzan kallo ta juyo ta watsawa matar data darawa ma mahaifiyarta a shekaru
"Ke kinga inna laraba,na gama fuskantar take takenki fa...tunda muka shigo gidan nan kike rawar qafa kina neman gindin zama....shine zaki gayawa mutane magana a fakaice,butulu shekararki nawa kina cin arziqinmu daga ke har indon?,ina cewa badon muba da tuni ana qauye ana fama da kirci da faso?,to mu duk girman arziqi bai rudarmu don mun saba gani ba yau farau ba" maganar ta yiwa inna laraba ciwo qwarai,a ganinta ko babu komai haliman ta girmamata ko don furfurarta,cikin murmushi da danne bacin rai tace mata
"Ki adana fushinki don bani nayi ba Allah ne ya nuna ikonsa a kai....duk wani abu da kuka hana aysha sai gashi yau Allah ya bata ninkinsa....duk abinda kuke zaton bata cancanceshi ba sai gashi yau Allah ya bata sama da shi,kun hanata mota qarama qwaya daya sai gashi Allah ya bata manya biyu,kun bata daki mafi qanqanta a gidan sai gashi Allah ya bata masarauta guda....kun siya mata kayan daki a qasar nan maimakon qasar waje kuma saiti daya sai gashi Allah ya bata wasu fiye da daya fin biyu ma,ya qawata mata gidan aurenta da jin qansa da rahamarsa....kinga kenan ba yina bane yin Allah ne...idan kunga dama ku aje abinda ke ranku ku rungumi yarinyar da bata taba taka muku ba bare ta zubar muku,ba sawa ba futarwa sai ku da kuke amfana ma da ita,baky dubi maraicinta ba,baku dubi rauninta ba kuke gallaza mata da gasata a ruwan sanyi ba tare da duk wani mara dogon nazari da tsinkaye ya fuskanci hakan ba,kun manta cewa Allah ke daukaka bawa a duk sanda yaso,kun manta cewa talaka da mai kudi duka Allah ne ya haliccesu badon yafison wani ba sai wanda yafi biyayya a gareshi,kun manta cewa dan kauye mutum ne mai daraja shima kamar kowa....qauye muhalli ne mai daraja tun a zamanin annabawa?,tunda ko annabinmu an bada shi raino a can,ya rayu da su bai kuma taba qyamatarsu ba,halima wannan ishara ce a gareku,ruwanku ku gayara ruwanku ku dora daga inda kuka tsaya,aysha dai tayi gaba amma zaku iya biyota a baya"miqewa anty halima tayi ta soma zuba ruwan bala'i,duk wani bacin rai dake ranta take furtashi a sannan,su anty kubra ke riqeta amma bata ji bata gani,murmushi inna laraba tayi
"Iyaka a dakatar dani bakin aiki ko?....ki sama ranki to daga nan zan wuce cikin nawa ahalin,karki manta yarona da qafarsa yazo zai tafi da ni mahaifiyarku ta dakatar da shi,ta roqeshi ya barni saboda sabo,ina fata baki manta ba?,abu daya zan gaya miki kafin na wuce shine...kibi ko ince kubi duniya a sannu,a yanzu ishara daya tazo muku...idan baku sauya ba sauran isharorin na nan tafe,bikin indo kuwa har qauyen takai in sha Allahu,na barku lafiya" ta fada tana juyawa nan ta fice ta barsu,anty halima naci gaba da kumfar baki.
*mrs muhammad ce*👑*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN BAKI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING_*
*_LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*_,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*KO KUMA*
(07067124863)
*DB*
25
Bin kowannensu da kallo kawai asma'u take sanda suke zayyanawa mummy yadda suka samu gidan ayshan,jin abun take kamar almara,ji take kaman mafarki,tsaye kawai take ta kasa tabuka komai kamar wadda aka zarewa duk wata laka ta jikinta
"Qarya ne....qarya kuke waini zaku zolaya,ta ina yaron oga zai samu irin wannan gidan?,ni zaku tsokana bayan nafi kowa sanin wayeshi,mtseww" Ta fada tana banka musu harara,nusaiba ce tayi caraf ta ciro wayarta ta soma gwadawa asma'un selfie din da suka sha cikin gidan
"Kanbu" asma'u ta lailayo ashar din kai tsaye cike da baqinciki takaici cakude da hassada,zama tayi da sauri gefan gado kusa da nusaiba
"Who is khalipha?" Ta fada tana tambayar kanta,tabbas babu shakka akwai wani daurin boye dangane da al'amarin,tabbas wannan khaliphan ba shine wanda ta sani ba,akwai wani khaliphan boye a bayan khaliphan data sani,ta yaya zata yadda,ta yaya zata amince aysha ta auri wannan khaliphan?bayan duka yaqin da tayi a baya kan hana faruwar hakan,abinda ya dinga kai komo kenan a zuciyarta,cikin fushi da hanzari ba tare data cewa kowa komai ba ta fice daga dakin,tana jin kamar iska ke tafe da ita ba qafafunta ba.
"Aisha....kinga baiwar da Allah yayi miki kuwa?,kinga gidanki aisha?,dama mai kudi zaki aura?" Mero ke fadin haka cikin tsantsar farinciki tana riqe da hannun aishan,sosai takejin dadi kamar ita zata zauna cikin gidan.
Sam bata kawo komai ba tayi murmushi
"Mai rufin asiri dai mero,shima talaka ne kamarmu" idanu mero ta zaro tana dubanta
"Talaka?,alqur'an kada bakinki ya sake fadin cewa shima kamarmu yake,kinsan yadda sama ta yiwa qasa nisa?,to kwatankwacin haka tazarar mu da shi take,kinga gidanki kuwa indo?....bari kigaa a wayata duk da bai dauku da kyau ba" mero ta fada tana ciro 'yar qaramar torching dinta da mijinta ta saya mata wancan wata bayan ya saida amfanin gonarsa ya samu riba mai yawa.
Dariya take kawai a sanda ta karbi wayar don tana zaton zuzuta abu ne kawai irin na meron,a ido gidan ya qayatar da ita sanda take kallon hotunan,saidai sam bata kawo kanta a ciki ba
"A ina kika samo wadan nan hotunan mero?" Aysha ta tambayeta
"Hotunan gidanki ne da muka je yanzu indo...indo ki godewa Allah,Allah ya miki ni'ima da baiwa wallahi,ba shakka Allah ya fanshe miki wahalarki ta shekara da shekaru,yanzu haka kaf kayan jeranki mun dawo dasu saboda babu wajen da zamu zuba su,hasalima wadanda muka tarar jere a gidan sai namu ya tashi kaman a bola muka tsintosu" dariya sosai aysha ta saki,labarin sai ya nishadantar da ita,don har ga Allah bata yarda da gaske mero take ba,ta daukeshi kawai a shaci fadi ko nishadi takeson sanyata saboda taga alamun damuwa tattare da ita tun dazun kafin su fita,ita kuma ba wannan ne a ranta ba,ummanta take son gani,labarin ummanta takeson ji,kulawa take buqata ta gani daga wajen umminta komai qanqantarta.