Sashe 50
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta bangaren aysha kuwa tana yin komai ne bisa umarnin aliya,tun dazun da daddy yazo ya musu nasiharsa da bankwana na qarshe take jin kamar idan ta fita daga gidan ba zata dawo ba,kaman tace ta fasa auren...kamar tace ta fasa tafiya,suyita zamansu dasu asma'un tana daurewa halayyarsu,tabbas sabo mugun abu ne,sabo turken wawa ne,batasan da wanne baki zata yiwa daddyn godiya ba,batasan cikin addu'o'i wacce addu'a ya cancanta tayi masa ba,saidai kowa tayita roqa masa gafara da rahamar ubangiji har qarshen rayuwarta,tana zaune saman doguwar kujera a gaban mudubi aliya na shiryata,sunyi fada yafi sau nawa,duk abinda ta saka mata sai ta cire,duk abinda ta goga mata saita goge,saida aliyan ta nuna fushinta sannan ta tsaya ta mata madaidaiciyar kwalliya wadda ba qaramin kyau tayi wa ayshan ba,kamar ka sace ta ka gudu,kwalliya mai sanyi babu hayaniya ba cin waje,tana tsaka da fesheta da turare wayar aliya ta dauki ruri,da hannu daya ta daga saboda dayan ya baci da hoda ta kara akunneta
"Okey...okey to shikenan" ta ambata,wayar ta datse tana fidda murmushi idonta akan aysha
"Ko iya haka aka tsaya khalipha ya faranta min....na gode masa qwarai" saita dubi 'yan uwan ayshan dake dakin tace
"Duk motar da kuka gani baqa mai dauke da wani tambari a jikinta motocin daukar indo ne...ku shiga duk wadda kuka ga dama,ko kowacce mutum mutum daya zata dauka motocin sun mana yawa....duk wanda ya muku magana koya gaya muku maganar banza ku mayar masa" dariya suka sanya aysha na binsu da kallo,tun jiya aliya ta zige su baki daya,sun kuma hau,kowa yasan yanayin yadda wasu yaran karkarar suke bare yanzu da aliya ta sake tunzurasu,murya qasa qasa don sam bata son magana tace
"Aliya....kin zama babbar kwabo...ke kike sake tunzurasu" idanu aliya ta fito da shi tana tsayawa daga rolling mayafinta da take tana duban aysha
"Kin manta abinda hausawa suka ce?...rana dubu ta barawo rana daya tak tamai kaya...shekara nawa ana abu daya...so ba ruwanki malama ki barmu yau mu huce takaici" bakinta kawai taja ta tsuke,tasan tunda ta niyyata sai sun adar,tana kallon aliyan ta fice daga dakin.
A corridor ta samu mamanta wadda daga dakin mummy take tayi mata Allah ya sanya alkhairi,aliya na ganinta ta mele baki
"Kai mama...sai da kika mata Allah ya sanya alkhairi bayan baso take ba na 'yarta kawai takeso" daquwa maman ta watsa mata
"Gidanku ja'ira...koma meye ba daga yau ya qare ba?,Allah ya qaddarawa kowa qaddararsa?"
"Shikenan mama....ga masu daukan ayshan can sunzo bari na yiwa su gwaggonta magana....."
"To shikenan...bari na shiga mu gaisa".
Wayarta ta daga ta kira mahmoud wanda suka jone a matsayinsa na babban abokin ango ita kuma babbar aminiyar amarya,bakin daya daga cikin motocin ta qarasa tana qarewa motocin kallo a fakaice,ita kanta abun ya qayatar da ita,yawansu da kyan motocin da yadda suke daukar ido,magana sukayi da shi ta gaya masa duk matar data shiga motarsu gidan aysha za'a wuce kawai sannan ta dawo ciki,tun daga farfajiya zuwa falon godan take jin ana zancan motocin da suka zo daukar asma'u,kowa na zuzutasu hadi da yabawa,dariya take sosai cikin ranta tana qissima yadda dramer zata kaya,lallai yau akwai film guda a sanda asma'u ta fahimci meke faruwa,yau zata gane a rayuwa kafi wani ne wani ya fika,kuma dole kai qasan wani kake komai kyanka,iliminka dukiyarka ko nasabarka.
Sanda ta shiga dakin bata taddasu aysha ba,su gwaggo sun miqa ta wajen mummy da nufin suyi sallama,kalaman da aysha tayi ga mummy ba ita kadai ba har wanda ke wajen ya tabasu,wannan karon duk da yadda mummyn kejin zafin aysha...jin zafi mara dalili ta daure tayi mata fatan alkhairi,kuka take sosai cikin mayafinta,kukan rashin uwa,uwar da zata tallafeta ta rungumeta,kukan rashin uwar da zata gaya mata dokoki da hanyoyin zaman gidan auren,uwar da zata nuna alhinin na haqiqa saboda sun raba muhalli...uwar da zata roqa mata salama da samun tabbatuwa da zaman lafiya a sabon muhallin da zata soma rayuwa,yau jinta take cikin matsanancin quncin da zata iya cewa tamkar ninka mata shi akayi,a haka take takawa tana ficewa daga gidan,kuka na sarqe numfashinta kamar zata shide.
Kowa ya san yadda mata keda kwadayi da rububin zuwa gidan amarya,hakan ce kuwa ta kasance sanda aka soma bude motocin daukar aysha,dangi da 'yan uwan da kaso tara cikin goma na asma'u ne suka soma duruwa ciki,suna tsammamin motocin rakiyarta ne,don da yawa daga cikinsu suna da kabarin irin mijin da ayshan zata aura,basu da labarin yadda lamari ya sauya lokaci daya,so babu wanda ya kawo cewa mijin nata zai iya aiko da wadannan motocin bare suyi tunanin nata ne,a haka labari ya bazama cikin gida masu son zuwa kai amarya wadanda basu da ababen hawa suka soma fitowa.
Farida ce ta shiga dakin da asma'u da qawayenta suke ta sanar musu an soma tafiya fa,a sannan wata yayar mummy ta shiga ta kai asma'un wajen mummy don suyi sallama,ba wata sallama bace ko wasu kalamai illa kuka da suka dinga yi,saida aka riqe asma'u wanda kusan rabi pretending ne,don dai kawai kar aga rashin kunyarta,bata tunanin don zata koma zama da masoyi kuma ya zame mata abun kuka,a haka aka lullube asma'u aka dannata cikin daya daga cikin motocin daukar amarya da zasu gidan aysha ba tare da sun sani ba.
*_Ya Allah,ya ubangiji ka rabamu da sharrin mutum da aljan_🙏🏽🙏🏽*
*mrs muhammad ce*👑
*mrs muhammad ce*👑🏡🏡🏡💋💋💋💋💋💋
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: *_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300
*KO WANNAN NUMBER*
07067124863
*DB*
29
Ita kadai da qawayenta ne suka shiga motar,saboda a cewarta idan aka hadata da tsofaffi zasu hanasu sakewa,suna shiga ta yaye lullubin kanta tana kallon cikin motar,ita mayyar mota take ta burgeta,tayi mata kyau sosai komai yaji,tana ji a ranta ita ko irinta zata sa mahmoud ya siya mata,nan suka rare cikin motar abinsu kamar ba amarya ba,ta yiwa driver magana ya saka musu waqa,saida suka zaba daya daga cikin waqoqin mutanen kudu
"Asmaa....haka friends din hamid suka hadu?....ke kinga wani guy dana gani a cikinsu kowa....ke inaga rabo ke kira na nazo bikinki" cewar husna duk girman kanta da fadin ranta,dariya suka sheqe da ita gaba da
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: qawayenta mutum uku,baya son qorafi baya son kuma ya qarajin wani abu ya biyo baya,tasan daddyn har yau na ciki da ita kan maganar aysha,tilas ta haqura,aka dauki yayarta daya yayar daddy daya,qawayenta biyu,qawayen asma'un biyu,abun mamakin shine sanda suka fita da amaryar akwai motoci kusan guda takwas,saidai biyu ne kawai nasu saura dangin hamid ne mata,wanda a qa'ida su zasu shiga su fito da amarya amma suka qame cikin mota ba wadda ta tako waje har aka saka asma'un cikin motar aka soma tafiya.
Qarfe tara na dare ayarin motocinsu khalipha da abokanshi suka shigo gidan,daga inda take zaune tana iya jiyo qararsu da maganganu sama sama,duka duka ba'a fi mintuna goma sha biyar ba taji motocin sun sama ficewa daga gidan,cikar mintuna ashirin taji dif alamun babu kowa a harabar gidan.
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: tsantsar bacin ran dake fuskarta na nunawa,duk da qoqarin danneshi da take
"Motoci biyu?...motoci biyu kuma?" Mummy ta tambaya tana yatsine fuska
"Ki aika a gano miki" anty safiyya ta fada tana cire mayafinta ta wuce bandaki,don ita bata jin zata ma iya zuwa.
Kai tsaye dakin asma'u mummy ta wuce tana tambayarta zancan motoci biyu da aka ce,ta tabbatar mata haka ne,nan mummy ta hau masifa tana fadin idan ma qyashin bada motocin suke su zasu bada wadanda zasu isa
"Mummy.....kiyi haquri kawai don yace baya buqatar mota sama da biyu",wannan batun shi ya tunzura mumnyn,tana ganin kawai hamid ya shirya wulaqanta su ne,ta taya har aisha zata fisu yawan 'yan rakiya da ababen hawa?,ganin yadda mummyn ta hau sosai taqi sauka daga qudurinta na qara motoci,sannan ita ta sani idan haka ta kasance komai zai iya faruwa,saboda haka tayi hanzarin kiran daddy ta gaya masa komai,kashe wayar yayi ba tare daya ce komai ba ya nemi mummyn da kanshi ya bata umarnin ta bada yarinya a tafi kaita,a hadata da manya mutum uku
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: ,bata iya bata amsa ba sai hannunta data kama suka shige motar anty haliman suka tada ta,tilas saura suka sake hawa motocin da aka kawosu akayi jigilar maidasu.
Tun cikin mota ta dinga jin ta muzanta,duk da cewa ba wadda ta sake ce mata komai amma saitaji a karan kanta ta tsargu da kanta,ba abinda ke mata yawo cikin idanu da kwanya irin gidan aysha,ita kanta ta tabbatar da cewa khalipha ya yayiwa hamid fintikau ya tsere masa,tako ina WUTSIYAR RAQUMI tayi nesa da qasa(daya daga cikin littafan zafafa biyar na billyn abdul),yau BURI DAYA (zafafa biyar mamuhghee)da take da shi ya cika,saidai ta raina cikar burin nata,ashe abinda take hangowa akwai sama da haka?ta yaya akai haka ta faru?,inama ace zata samu SAUYIN QADDARA(zafafa biyar na hafsat rano). Sai takwas na dare sannan ya kirata ya sanar mata zuwan motocin,anty safiyya ce ta fita sai gata ta dawo ta dubi mummy
"Sai a zabi wadanda zasu je kaita"
"Kamar yaya....kowa zaije kamar yadda aka je na indo"
"Da motoci biyun?" Anty safiyya ta fada
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: Duk yawan motocin tsaf harabar gidan ta lanqwame su,a jere daya bayan bayan daya suka jeru sannan jama'ar ciki suka fara fitowa,kowa ka kalla ido a waje yake duban gidan,kowa tanka kyau da tsarin gidan yake,tun daga harabar gidan zuwa cikin gidan,a sannan asma'u na cikin mayafi farinciki kaman ta taka rawa,tana tsammamin ana magana ne kan gidanta,sai a sannan ta soma zagin su nusaiba cikin ranta,wato qarya suke mata da suka wassafa yadda gidan aysha yafi nata kyau kenan?,so suke su haukatata kenan saboda sunsan yadda ta tsani tayi qasa a rayuwa.
"Okey...okey to shikenan" ta ambata,wayar ta datse tana fidda murmushi idonta akan aysha
"Ko iya haka aka tsaya khalipha ya faranta min....na gode masa qwarai" saita dubi 'yan uwan ayshan dake dakin tace
"Duk motar da kuka gani baqa mai dauke da wani tambari a jikinta motocin daukar indo ne...ku shiga duk wadda kuka ga dama,ko kowacce mutum mutum daya zata dauka motocin sun mana yawa....duk wanda ya muku magana koya gaya muku maganar banza ku mayar masa" dariya suka sanya aysha na binsu da kallo,tun jiya aliya ta zige su baki daya,sun kuma hau,kowa yasan yanayin yadda wasu yaran karkarar suke bare yanzu da aliya ta sake tunzurasu,murya qasa qasa don sam bata son magana tace
"Aliya....kin zama babbar kwabo...ke kike sake tunzurasu" idanu aliya ta fito da shi tana tsayawa daga rolling mayafinta da take tana duban aysha
"Kin manta abinda hausawa suka ce?...rana dubu ta barawo rana daya tak tamai kaya...shekara nawa ana abu daya...so ba ruwanki malama ki barmu yau mu huce takaici" bakinta kawai taja ta tsuke,tasan tunda ta niyyata sai sun adar,tana kallon aliyan ta fice daga dakin.
A corridor ta samu mamanta wadda daga dakin mummy take tayi mata Allah ya sanya alkhairi,aliya na ganinta ta mele baki
"Kai mama...sai da kika mata Allah ya sanya alkhairi bayan baso take ba na 'yarta kawai takeso" daquwa maman ta watsa mata
"Gidanku ja'ira...koma meye ba daga yau ya qare ba?,Allah ya qaddarawa kowa qaddararsa?"
"Shikenan mama....ga masu daukan ayshan can sunzo bari na yiwa su gwaggonta magana....."
"To shikenan...bari na shiga mu gaisa".
Wayarta ta daga ta kira mahmoud wanda suka jone a matsayinsa na babban abokin ango ita kuma babbar aminiyar amarya,bakin daya daga cikin motocin ta qarasa tana qarewa motocin kallo a fakaice,ita kanta abun ya qayatar da ita,yawansu da kyan motocin da yadda suke daukar ido,magana sukayi da shi ta gaya masa duk matar data shiga motarsu gidan aysha za'a wuce kawai sannan ta dawo ciki,tun daga farfajiya zuwa falon godan take jin ana zancan motocin da suka zo daukar asma'u,kowa na zuzutasu hadi da yabawa,dariya take sosai cikin ranta tana qissima yadda dramer zata kaya,lallai yau akwai film guda a sanda asma'u ta fahimci meke faruwa,yau zata gane a rayuwa kafi wani ne wani ya fika,kuma dole kai qasan wani kake komai kyanka,iliminka dukiyarka ko nasabarka.
Sanda ta shiga dakin bata taddasu aysha ba,su gwaggo sun miqa ta wajen mummy da nufin suyi sallama,kalaman da aysha tayi ga mummy ba ita kadai ba har wanda ke wajen ya tabasu,wannan karon duk da yadda mummyn kejin zafin aysha...jin zafi mara dalili ta daure tayi mata fatan alkhairi,kuka take sosai cikin mayafinta,kukan rashin uwa,uwar da zata tallafeta ta rungumeta,kukan rashin uwar da zata gaya mata dokoki da hanyoyin zaman gidan auren,uwar da zata nuna alhinin na haqiqa saboda sun raba muhalli...uwar da zata roqa mata salama da samun tabbatuwa da zaman lafiya a sabon muhallin da zata soma rayuwa,yau jinta take cikin matsanancin quncin da zata iya cewa tamkar ninka mata shi akayi,a haka take takawa tana ficewa daga gidan,kuka na sarqe numfashinta kamar zata shide.
Kowa ya san yadda mata keda kwadayi da rububin zuwa gidan amarya,hakan ce kuwa ta kasance sanda aka soma bude motocin daukar aysha,dangi da 'yan uwan da kaso tara cikin goma na asma'u ne suka soma duruwa ciki,suna tsammamin motocin rakiyarta ne,don da yawa daga cikinsu suna da kabarin irin mijin da ayshan zata aura,basu da labarin yadda lamari ya sauya lokaci daya,so babu wanda ya kawo cewa mijin nata zai iya aiko da wadannan motocin bare suyi tunanin nata ne,a haka labari ya bazama cikin gida masu son zuwa kai amarya wadanda basu da ababen hawa suka soma fitowa.
Farida ce ta shiga dakin da asma'u da qawayenta suke ta sanar musu an soma tafiya fa,a sannan wata yayar mummy ta shiga ta kai asma'un wajen mummy don suyi sallama,ba wata sallama bace ko wasu kalamai illa kuka da suka dinga yi,saida aka riqe asma'u wanda kusan rabi pretending ne,don dai kawai kar aga rashin kunyarta,bata tunanin don zata koma zama da masoyi kuma ya zame mata abun kuka,a haka aka lullube asma'u aka dannata cikin daya daga cikin motocin daukar amarya da zasu gidan aysha ba tare da sun sani ba.
*_Ya Allah,ya ubangiji ka rabamu da sharrin mutum da aljan_🙏🏽🙏🏽*
*mrs muhammad ce*👑
*mrs muhammad ce*👑🏡🏡🏡💋💋💋💋💋💋
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: *_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300
*KO WANNAN NUMBER*
07067124863
*DB*
29
Ita kadai da qawayenta ne suka shiga motar,saboda a cewarta idan aka hadata da tsofaffi zasu hanasu sakewa,suna shiga ta yaye lullubin kanta tana kallon cikin motar,ita mayyar mota take ta burgeta,tayi mata kyau sosai komai yaji,tana ji a ranta ita ko irinta zata sa mahmoud ya siya mata,nan suka rare cikin motar abinsu kamar ba amarya ba,ta yiwa driver magana ya saka musu waqa,saida suka zaba daya daga cikin waqoqin mutanen kudu
"Asmaa....haka friends din hamid suka hadu?....ke kinga wani guy dana gani a cikinsu kowa....ke inaga rabo ke kira na nazo bikinki" cewar husna duk girman kanta da fadin ranta,dariya suka sheqe da ita gaba da
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: qawayenta mutum uku,baya son qorafi baya son kuma ya qarajin wani abu ya biyo baya,tasan daddyn har yau na ciki da ita kan maganar aysha,tilas ta haqura,aka dauki yayarta daya yayar daddy daya,qawayenta biyu,qawayen asma'un biyu,abun mamakin shine sanda suka fita da amaryar akwai motoci kusan guda takwas,saidai biyu ne kawai nasu saura dangin hamid ne mata,wanda a qa'ida su zasu shiga su fito da amarya amma suka qame cikin mota ba wadda ta tako waje har aka saka asma'un cikin motar aka soma tafiya.
Qarfe tara na dare ayarin motocinsu khalipha da abokanshi suka shigo gidan,daga inda take zaune tana iya jiyo qararsu da maganganu sama sama,duka duka ba'a fi mintuna goma sha biyar ba taji motocin sun sama ficewa daga gidan,cikar mintuna ashirin taji dif alamun babu kowa a harabar gidan.
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: tsantsar bacin ran dake fuskarta na nunawa,duk da qoqarin danneshi da take
"Motoci biyu?...motoci biyu kuma?" Mummy ta tambaya tana yatsine fuska
"Ki aika a gano miki" anty safiyya ta fada tana cire mayafinta ta wuce bandaki,don ita bata jin zata ma iya zuwa.
Kai tsaye dakin asma'u mummy ta wuce tana tambayarta zancan motoci biyu da aka ce,ta tabbatar mata haka ne,nan mummy ta hau masifa tana fadin idan ma qyashin bada motocin suke su zasu bada wadanda zasu isa
"Mummy.....kiyi haquri kawai don yace baya buqatar mota sama da biyu",wannan batun shi ya tunzura mumnyn,tana ganin kawai hamid ya shirya wulaqanta su ne,ta taya har aisha zata fisu yawan 'yan rakiya da ababen hawa?,ganin yadda mummyn ta hau sosai taqi sauka daga qudurinta na qara motoci,sannan ita ta sani idan haka ta kasance komai zai iya faruwa,saboda haka tayi hanzarin kiran daddy ta gaya masa komai,kashe wayar yayi ba tare daya ce komai ba ya nemi mummyn da kanshi ya bata umarnin ta bada yarinya a tafi kaita,a hadata da manya mutum uku
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: ,bata iya bata amsa ba sai hannunta data kama suka shige motar anty haliman suka tada ta,tilas saura suka sake hawa motocin da aka kawosu akayi jigilar maidasu.
Tun cikin mota ta dinga jin ta muzanta,duk da cewa ba wadda ta sake ce mata komai amma saitaji a karan kanta ta tsargu da kanta,ba abinda ke mata yawo cikin idanu da kwanya irin gidan aysha,ita kanta ta tabbatar da cewa khalipha ya yayiwa hamid fintikau ya tsere masa,tako ina WUTSIYAR RAQUMI tayi nesa da qasa(daya daga cikin littafan zafafa biyar na billyn abdul),yau BURI DAYA (zafafa biyar mamuhghee)da take da shi ya cika,saidai ta raina cikar burin nata,ashe abinda take hangowa akwai sama da haka?ta yaya akai haka ta faru?,inama ace zata samu SAUYIN QADDARA(zafafa biyar na hafsat rano). Sai takwas na dare sannan ya kirata ya sanar mata zuwan motocin,anty safiyya ce ta fita sai gata ta dawo ta dubi mummy
"Sai a zabi wadanda zasu je kaita"
"Kamar yaya....kowa zaije kamar yadda aka je na indo"
"Da motoci biyun?" Anty safiyya ta fada
[10/02, 8:40 PM] +234 810 044 6653: Duk yawan motocin tsaf harabar gidan ta lanqwame su,a jere daya bayan bayan daya suka jeru sannan jama'ar ciki suka fara fitowa,kowa ka kalla ido a waje yake duban gidan,kowa tanka kyau da tsarin gidan yake,tun daga harabar gidan zuwa cikin gidan,a sannan asma'u na cikin mayafi farinciki kaman ta taka rawa,tana tsammamin ana magana ne kan gidanta,sai a sannan ta soma zagin su nusaiba cikin ranta,wato qarya suke mata da suka wassafa yadda gidan aysha yafi nata kyau kenan?,so suke su haukatata kenan saboda sunsan yadda ta tsani tayi qasa a rayuwa.