← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 114

Sashe 64

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana rakabe gefe suna ta hirarsu a qalla wajen minti talatin sannan hamid yajiyo
"Au hajiga ga tare fa muke da ita" gilashin fuskarta tadan saukar kadan ta kalli asma'un sosai sannan ta jashi sama
"Na ganta....sai yau taga damar zuwa?,koda yake ai ba yau muka fara ganinta fuskarta sananniya ce" ta fadi hakan da manufa biyu,don sanda hamid din ke neman aurenta bini bini zai kwasheta suje gidansu,saidai babban abinda ya daurewa asma'un ganin yadda dukkaninsu suka sauya,kaf dinsu ba haka suke mata ba a baya kafin ta auri dan uwansu,hakanan suja sha yata sukaci hitarsu suka godewa Allah,ko ruwa ba wanda ya kalleta da shi,sai daga qarshe ne da hamid din ya cewa qanwarsa ta bashi ruwa ta hado da asma'un,saboda tsabar baqinciki da bacin rai ko kallon ruwan bata yi ba har suka tafi.

Cikin mota ta dinga fushi da kumbure kumbure,saidai ko kallo bata isheshi ba bare ya nuna yasan tana yi ba,har daga qarshe data gaji ta tanka
"Amma dama kawoni gidanku kayi don a cimin fuska?" Wani juyowa yayi ya dubeta ya watsar kafin ya bata amsa
"Kamar yaya?"
"Baka ga abinda akayimin ba kenan?"
"To su kike su tashi suyita rawa suna tsalle sunga halittar da basu taba ganin irinta ba,ni da Allah banason fitina kinji ko?" Nan sa'insa ta kaure a tsakaninsu,bata yi shuru ba har sai data ga yana da niyyar kai mata mangari,koda suka je gida a fusace ta fita daga motar ta buga mishi qofar motar
"Kiyi a hankali,don wallahi idan kika sake kika yimin barna taki zan siyar na gyara" ya fada cikin daga murya yadda zata iya jiyowa.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Kwanaki biyar ya rage su soma lacture ta shirya tsaf don tafiya makaranta,duk wani abu daya dace babu wanda ba'a siya mata ba,siyayya irin ta 'ya'yan gata,itadai kallon komai take kamar almara,kaya kaman wadda zata shekara a can,hatta da ruwan sha khalipha bai bari ba sai daya siya mata,wani abun ma har kunyar kanta da kanta take ji duk da yadda anni ke bata qwarin gwiwa,sai take jin kamar ta zame musu wani kaya ta hadasu da hidimarta.

Tana tsaye a falon sashen nasu sagale da jakarta wadda ta zuba qananun abubuwa irin namu na mata,sai take jin kewa ta soma shigarta,jikinta ya danyi sanyi kamar zata wani garin ta barsu,a haka khalipha ya fito ya taddata,atm card ya miqa mata yana kafeta da idanunshi,a sanyaye ta amsa tana son jin qarin bayani
"Duk sanda kike da buqatar wani abu ki cire kudi ki saya,naki ne accnt dinki ne,sati mai zuwa idan Allah ya kaimu da rai da lafiya nima zanyi tafiya,zanbar qasar na tsahon shekara biyu" saita daga kai tana kallonshi,hakanan zuciyarta ta raurawa,sosai take jin ba dadi,kaman cewa yayi idan ya tafi bazai dawo ba,ganin sun hada ido kaman yadda suka saba sai kowa ya kau da kanshi
"Zan dinga zuwa a duk sanda na samu chance Ya fadi kamar ya karanci abinda yake zuciyarta,kunya ce taji tana neman kamata,kardai ace ya fahimci abinda take saqawa a ranta,saita sunkuyar da kai
"Allah ya bada abinda za'a je nema,ubangiji yayi jagora ya kade dukkan abinqi"
"Ameen kema haka" ya fada a taqaice,kasancewar tun jiya yayi mata duk jan hankalin daya kamata,iya gajeran lafazinsa kawai yayi mata dadi a rai
"Na gode" ta furta a sanyaye.

Qwalla ce fal idanunta sanda suke sallama da anni,har mus'ab ya dinga sheqa musu dariya abinsa,khalipha kam falo ya koma yayi zamanshi abunsa,kewarsu take tun kafin tabar gidan,haka suka rakota har bakin mota,inda haidar zai kaita.

Rufe motar tayi ta daga kai a hankalin,take idanunta suka shiga cikin nashi,yana tsaye bakin window din da take zaune hannunsa harde a aqirji,shima ita yake kallo,sai qwallar da take tattalin kar ta zubo ta silalo saman fuskarta,sakin hannayen nashi yayi ya bar side dinta ya koma mazaunin driver,duqawa yayi ta window din motar dai dai saitin haidar,batasan me ya gaya mishi ba na tsahon minti daya kafin ya miqe yana cewa
"Allah ya tsare hanya,a kula da hanya"
"In sha Allahu yaya" haidar ya fada yana tasar motar,yana nan tsaye hannyensa goye a bayansa har motar tasu ta fice daga gidan.

Kadan kadan taci gaba da fidda qwalla tana qoqarin sharewa,haidar baice mata komai ba har sai da sukayi tafiya ta kusan minti goma sannan ya dan saki dariya
"Nikam kukan nan bansan na meye ba?,anya kukan rabuwa da anni ne bana rabuwa da yayanmu bane?" Dan harararshi tayi tana fidda qaramin murmushi,daga bisani tayi qoqarin controlling hawayenta,saidai duk da haka zuciyarta babu dadi,wayarshi ya zaro ya kira khaliphan,da alama shi ya bashi umarnin yin hakan,miqa mata wayar kawai haidar yayi yana murmushi,hannu ta sanya ta karba gami da karawa a kunnenta ba tare da tace komai ba
"Kina kuka kaman wata baby?,kinason dagawa mutane hankali,ko baki shirya ba adawo dake?" Girgiza kai tayi kama tana gabansa sannan tace
"A'ah"
"Allah ya bada sa'a" ya fada cikin low tune
"Amin na gode"
"Bashi wayar" saita waiwaya ta miqawa haidar dake boye dariyar da batsan ta meye ba,magana sukayi da bata wuce ta minti daya ba ya katse wayar yana 'yar mita
"Sai wani jaddadawa yake nayi tuqi a hankali waishi me mata,muma dai mun kusa in sha Allahu mu fara hura hanci muma" daroya ma haidar din ya bata,ita ta sani kawai dai yana jaddadawar ne saboda dan uwanshi,amma ita yaushe takai nan,haka haidar ya dinga janta da hira har ta dan saki jiki,yana bata labarin makarantar da yake can suka fara yi shi da mus'ab kafin daga bisani khalipha ya fitar da su waje.

Ajiyar zuciya ya saki yana maida wayar aljihunsa,baisan me yasha kanshi da kukanta ba harya buqaci jin yata kasance,hakanan kawai yaji yana da buqatar jin haka,sai ya sake sauke wata ajiyar zuciyar yana duban wami littafinta data dauko ta manta dashi saman kujera.

Awa guda suka isa a haka donsu tsaya cin abinci a wani gidan cin abinci dake hanya,itakam aysha har sannan babu abinda taci saboda dama can abincin safen ba damunta yayi ba,haidar na tare da ita har aka gama shigar mata da kayanta,kulawa ta musamman ta samu daga ma'aikatan dake kula da hostel din,bata san me yasa ba,saidai tuni khalipha ya gama sallamar kowa a cikinsu,hakan yasa suke ankare da zuwan ta,saidai komai ya zama normal ya tabbatar babu wani abu da zata sake buqata kaman yadda yayanshi ya umarceshi sannan yayi mata sallama,sanda zai tafin ma dai kamar zata bishi,hakanan dai ta daure ta juya zuwa ta koma hostel din.

Su uku ne a dakin,saidai sanda taje mutum biyun sun gama shirya kayansu basa nan,da alama ma ba ranar su sukazo ba,kasancewarta ita daya a dakin ya bata dama itama ta zauna ta jera komai nata a muhallinsa yadda take da buqata,koda ta gama an kusa sallar la'asar,sai kawai ta kunna gas ta dora jallop din sphaghetti sannan ta shiga bandakin dake manne da dakin ta dauro alwala.

A cooler ta aje abincin bayan ta gama,ta bude barander dake bayan dakinsu ta wanke komai ta tsaftaceshi,bata jin yunwa sai kewar gida dake damunta,tana gefan gadonta tana qarewa dakin nasu kallo,komai neat gwanin sha'awa,fata kawai take Allah yasa musulmai ne,masu halin qwarai,sai ta kasa zaman dakin,ta zari hijabinta ta zura ta lalubi muqullin dakin tanufi qofa tana duba wayarta,aliya takeson kira,yau kwana uku basu samu sunyi waya ba,kowa yana busy.

Qofar da aka turo saura qiris ta daki goshinta,da sauri taja baya tana duban mai shigowar,matashiyar budurwa ce wadda duka duka shekarunta basufi na ayshan ba,doguwa ce bata da jiki,kalarta choculet ce mai daukan ido da sheqi,tana da doguwar fuska da jerarrun fararen haqoranta,idanu ta zaro tana fadin
"Ah sorry sister....sannu Allah yasa ban bigeki ba" murmushi aliyan tayi,yanayin yadda take magana kawai ya isa ya gaya maka tana da surutu
"Babu komai,baki sameni ba"
"Alhmdlh....kece ragowar room partner dinmu da baki qaraso ba ko?" Ta fadi fuskarta qunshe da murmushi wanda ke nuna haka yanayinta yake,kai aysha ta gyada
"Eh"
"Thank god...amma naji dadi....ni sunana halimatu abdullahi musa,amma anfi kirana da hanan,daga hotoro nake,saidai iyayena duka na zaune a abuja,kefa?"
"Sunana aysha umar modibbo"
"Fulani girl?" Hanan ta tambayeta tana dage gira,dariya aysha tayi,yadda hanan din bata da wahalar sabo yake bata mamaki,kai ta gyada mata again
"Kice na shirya,na kusa koyon fillanci" tare suka sake sakin dariya gaba dayansu
"Well,na tsaidaki da surutu na ko,naga kamar fita zaki da alama uzuri gareki" komawa ayshan tayi da baya ta nemi wajan zama,don zuwa yanzu kuma bata da wani sauran dalilin fita
"A'ah,zaman shuru ne dama yamin yawa nace bari na dan fita naga yanayin hostel din"
"No more loniless tunda na dawo" ta fadi still tana murmushi gami da zube jakunkunan dake hannunta
"Naje na amshi saqo ne daga wajen uncle dina....ga wata azababbiyar yunwa da nikeji...nace ma ya tausayan ya sayan wani abu amma yaqi" ta fada tana kwabe fuska,dariya aysha tayi tana nuna mata cooler din data zu a abinci
"Ga abinci can saiki diba kici" ido ya fiddo
"Kai amma kin taimakeni wallahi,dama maman hunaifa nake saka ran idan ta rigani dawowa na samu daga wajenta,to itama kinga shuru" ta qarasa fada tana bude abincin,qamshin ya daki fuskarta saita lumshe ido
"Tun kafin naci ma nasan zatayi dadi wallahi,sauko muci"
"Kaman a qoshe fa nake"
"Ba wani nan,saidai idan nima bakiso naci ne" jin haka ya sanya aysha ta sauko,hanan ta zuba musu tare suka soma ci tana ci gaba da jan aysha da hira,itadai kallonta kawai aysha take,tana mamakin saurin sakewa irin na hanan,bata da baqunta sam,saidai ta lura tana da kirki matuqa,tana da hankali tsafta sannan uwa uba da ganinta yar qwalisa ce wato gayu,da haka suka gama cin abincin,suna tsaka da wanke hannunsu aka sake turo qofar dakin nasu,wata matashiya ce ta sake shigowa,shigowarta ya sanya hanan yin dif,da aysha suka gaisa sannan ta dubu hanan
"Kin dawo amma koki sanar min?"
"Babu buqatar hakan tunda gashi yanzu kin ganni" hanan ta fada tana miqewa ta bude bandakinsu ta shiga,ta dade matashiyar a tsaye hanan bata fito ba,hakan shi ya tilasta mata tafiya,sai data tafi sannan hanan ta fito tana jan tsaki gami da mita,ita dai aysha naji bata ce komai ba hakanan bata tambayi dalili ba,saboda ba dabi'arta bace.
Chapter 64 · 0% Book details