← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 114

Sashe 56

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A nutse ta miqe ta dauki akwatin wanda ya danfi kit girma da kadan ta nufi qofar bedroom din daya nuna mata,cike da baqunta kamar zata tadda wani abu ta tura qofar ta shiga,babban bedroom mai kyau tsari da daukar hankali,kallon farko taji ya bugeta,babu tarkace babu kaye kaye aciki,furnitures din cikin ba wasu masu girma bane medium amma kyansu dole ka kalla ka sake kalla,gadon fes qal a mulmule kaman na amarya,a sanyaye ta aje akwatin saman mirrow don kada ta bata mishi gado,ta bude shi,wani lace ne mai azabar kyau a ciki butter colour,wanda aka yiwa dinkin riga fitted da zani simple,akwai dankunne da sarqa a ciki da abun hannu,zai wani.plate din takalmi dake maqale da mayafi dukka kalar da zasu shiga da lace din,sai body cream da powder da sauran tarkacen kayan makeup duka na kamfani guda,shafa lace din ta sake yi karo na kusan uku,ko baka san kudin kaya ba kaganshi kasan cewa ba qarami bane,jikinta yayi sanyi tana jin shakku cikin zuciyarta,anya ko bata zura kai da yawa ba kuwa?,zama tayi sosai tana ci gaba da kallon kaya,bata iya tuna wata rana guda data saka kaya kamar haka masu kyau da tsada,a qalla ta kusa kashe minti goma kafin ta iya tashi ta debi kayan ta shige toilet din da su,don ba zata iya fitowa ba ta shirya cikin dakin.

A toilet dinma sai da wasu abubuwan suka bata mata lokaci da batasan ya zatayi operating nasu ba,daga bisani ta gama wankan ta tsane jikinta ta saka wadancan,har shafa man duka a bayi tayi ta gyara gshinta,sai data gama ta dawo gaban madubi ta shafa powder ta dan goga jambaki kadan daya qarawa lips dinta colour pink dinsu ya sake fita,ninke wadancan data cire tayi ta maida cikin akwatin,tana shirin rufewa taji knocking,wuri wuri tayi da idanu tana duban mayafin da aka hada mata cikin kayan,sam bashi da wani kauri,jin ana turo qofar ya sanyata ala dole taja mayafin ta yane kanta.

Dubanta yayi sanda ya shigo na tsahon minti daya,kanta na qasa tana rufe akwatin,dagowa tayi suka hada ido saiya basar,yana tuna sanda anty ruqayya ta dauko lace din ta dinga kodashi da fadin zaiyi ma mutum kyau,a sannan shidai kawai yana biye da ita ne,saboda indai ba anni ba bansan ya zai sayawa mata kaya ba,gashi dai maison ado ne da kwalliya amma baisan ya zai saya ba,kodan bashi da 'yar uwa mace,wani abu ya taba zuciyarshi a lokacin daya tuna da hajar,har hakan yasa yanayin fuskarsa ya dan sauya,duk sanda zai tuna da ita da yadda ta tafi ta barsu komai walwalar da yake ciki sai yanayinsa ya sauya
"Mu tafi" ya fada yana fita daga dakin,gaba daya jin dakin yake kaman ba nashi ba,saboda tsahon rayuwarshi ba macen data taba shiga masa daki idan ka dauke anni,takalman ta duqa ta zira a qafarta sannan tabi bayanshi,yana gaba tana bayanshi,suna dab da shiga sashen annin ya tsaya sai itama ta tsaya
"Qaraso kusa" ya fada ba tare daya waiwayo ba,kusa da shi ta qaraso din dab da bayanshi,sai ya sake matsowa baya suka dai daita tsahonsu sannan suka ci gaba da takawa zuwa ciki.

Mutum biyar ne cikin falon,anni amal da wasu maza biyu da mace daya da aysha batasan su waye ba,da fara'a anni ta amsa sallamar tasu tana yiwa aysha sannu,yayin da amal ta zubawa ayshan idanu tana dubanta ita da daya baquwar,duk kunya saita kama ayshan na yadda anni ke karramata haka,bayan ita din ba abar karramawa bace a ganinta
"Kai.....kaddai kece auntyn tamu?" Haidar ya fada fuskarsa cike da fara'a da kuma mamaki,dubanshi sukayi su duka,mus'ab yadan tabe fuska
"Yanzu zaka ce ka santa ko?"
"Qwarai kuwa"
"A'ina?" Amal tayi saurin tambaya,hararta yayi sannan ya amsa
"A school....,gaskiya yaya kayi zabe mai kyau,she was verry kind and innocent wallahi...."
"Tell us ya akayi kasan hakan?" Daya baquwar da batayi magana ba ta fada cikin yauqi,sai a sannan khalipha ya dora idanunsa a kanta,idonta daya ta kashe masa sannan tace
"Yeah...muna buqatar mu sani,angon da babu gayyata gashi mu mun kawo kanmu"
"Anni....ya kamata muci abinci haka dare yana yi" ya furta yana duba agogon hannunshi,ko daya baiji dadin zuwan rahama ba gidan,ya santa yasan halinta sarai,gwara amal sau dubu da ita,baya son takura baya son sa ido duka rahama ta hada su
"Ya kamata" anni ta fada tana yunqurin miqewa,wanda hakan ya saka kowa ma ya miqe zuwa dining area,saidai rahama data danyi jinkiri tana ta bayan khalipha
"Ya khalipha...kaman bakayi murna da gani na bako,bayan laifin boyemin bikinka da kayi baka sanarmin ba,ina niger ina nigeria?"
"Tunda kin sani yanzu no need of qorafi....."
"Amaryar tamu ma sha Allah....baka gabatar mata da ni ba"
"Da wuri haka?..." Ya bata amsa a kaikaice,bakinta taja tayi shuru kawai ba tare data sake cewa komai ba,tana gudun kada ajinta ya zuba a idanun aysha,a haka suka qarasa wajen,amal dake ankare da duk abinda ke faruwa tana tsaye kishi ya hanata zama,har sai da kowa ya zauna sannan ta soma serving din kowa da abinda ranshi keso,kala biyu suke girki duk dare,saidai basa yin mai yawan da zai zama asara,suna yinsa dai dai da yadda za'a iya cinyewa,rahama wadda tunda suka zauna take satar kallon aysha,ba haka taso taddata ba sam,saidai duk da haka tana jin ba wani abu da zai rageta da shi
"Har yanzu anni kuna girkin kun nan kala biyu?"
"In sha Allahu" anni ta bata amsa,sai ta dauke idonta ta maida kan aisha
"Wannan tsarin ya khalipha ne,yana da son abinci mai dadi diffrent colurs...Allah yasa amaryar tamu expert ce ta wannan bangaren" shuru teburin ya dauka kowa da tunanin daya zo masa,khalipha ne ya katse shurun da cewa
"Abu na farko data soma sani kenan game da ni.....wai ke yaushe kika zo?,wa kika barwa karatun naki?" Idanunta ta juya sannan tace
"Sun tafi strike ne na sai baba ta gani,so shi yasa na samu chance na zuwa na tayaku murnar biki...amma amaryar taka kamar bata magana" ta qarshe maganar idanunta kan aysha,da alama ta tsaye mata a rai,wanda ayshan batasan dalilin haka ba,banda faduwar gaba ba abinda takehi,addu'a take kada Allah yasake jarrabtarta da jama'ar da zasu hanata sukuni,jama'ar da zasu zame mata tarnaqi a rayuwarta
"Kirkinta ne yayi yawa yaa rahama.." Haidar ya sake fada yana murmushi,khalipha ya daga kai ya kalleshi yana tunanin a ina ya santa ne wai?,duk suna son dagula masa lissafi baki daya baison yana cin abinci ana damunshi da hira barkatai,tunda rahama tazo kuma sai yadda hali yayi
"Ya khalipha ka tuna sanda muka shiga makaranta ganin wani abokinka lacturer bayan mun tashi daga office nace am starving,zanje na nemi abinci naci?" Kai ya gyada masa.

Daki daki ya bada labarin duk abinda ya faru tun daga shigarsa,watsa mata lemo da qarasowar aliya zuwa fitarsu daga wajen,shuru kowa yayi a wajen,sai a sannan aysha ta daga kai ta dubeshi,tabbas ta tuna abinda ya farun,saidai fuskar tashi ce ba zata tuna ba banda ya fada din,tabe baki rahama tayi,don ita gaba daya abun bai burgeta ba
"Kaman wani labarin arziqi ka ishemu da karadi" hararta yayi itama duk da ta girmeshi
"Idan kece i know saikinyi tashin hankali sosai kaman yadda qawarta taso tayi,musamman idan aka jiqa wannan foundation face din naki" dariya suka kece da ita gaba daya,banda anni dake qoqarin tsawatar musu,sai kuma khalipha daya dan murmusa kadan yana kada kai kafin ya tsuke tashi fuskar,aysha kam baka gane yanayin fuskarta,har kowa ya nutsu amma banda amal,sosai abun yayi mata suger,ta tsani zuwan rahama da zeenart gidan sam,karma rahama taji labari da take musu gani gani,ita daga bangaren anni take,da yake tana da tarihin me ya wakana tsakanin anni da su dangin baban khalipha,sai ya zama kamar ta samu wani abune da take yawan yi misu shagube da shi

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

32

Khalipha ne ya soma miqewa daga zaman cin abincin,anni ta dubeshi
"Ka gama kenan?"
"Eh..ban jima da cin abinci ba ai..."
"Ko amarya dai ta cika maka cikinka?" Rahama ta fada da salon bin qwaqwqwafi,wani kallo yayi mata kawai ya dauke kai ya soma sauka daga wajen,ture plate din aysha itama tayi wadda bata ci wani abun arziqi ba sam,don ko yunwar ma bata ji batasan me yasa ba
"Aishatu kardai ace kema kin qoshi?" Kai ta gyada a kunyace
"Don dai ya khalipha ya qoshi ne shi yasa" amal ta fada can qasan ranta tana jin kishi,dariya suka saka tsakanin mus'ab da haidar,murmushi anni tayi sannan tace
"Saiku wuce hakanan ku samu ku huta ko muhammadu?" Anni ta fada
"Ohk...ohk" khalipha ya fada cikin dan daburcewa kadan wanda ba lallai ka lura da hakan ba,yayi zaton anni zata bata daki ta wuce ta kwana a nan,amma sai ya raya a ransa me yiwuwa saboda idon yaran ta gwada hakan
"Aishatu wuce ku tafi sai da safe"kunya ta sakata ta kasa motsawa daga nan,idon rahama na kanta haka ma amal na satar kallonta,tsaf anni ta lura kunya take,sai tace da khalipha
"Wuce amal ta rakota"
"Ohk to..." Ya fada yana jin dadi cikin ransa,don baisan yadda zai kwana daki daya da mace ba.

Yana fita daga falon anni ta dubi amal
"Qarasa ci ki rakata.."
"Toh" ta amsa wani abu yana dunqule mata a maqoshi,hakanan amal ta dinga yangar cin abincin da gayya tana sani,bata gama ba har sai da khalipha yaci wajen awa daya da tafiya sannan ta sha ruwa ta miqe hakanma ba don taso ba
"Allah ya bamu alkhairi"
"Amin" aysha ta amsawa anni.
Chapter 56 · 0% Book details