← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 98 OF 114

Sashe 98

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tana shafawa qafafunta mai murmushi ya subuce a fuskarta sabida tuna hirarsu da khalipha ta jiya,sassanyar muryarshi,yanayin maganarshi dake fita a nutse da sauransu,saita kada kai kawai tana dariya,itama sai taga wautarta,ba lallai yana nufin abinda ya fada din ba,don yanayin maganar bai nuna cikin zafi ko fushi yayita ba,bayan ta kammala ta shafa powder da man lebe kadan don kada ya dameta,jikinta ta feshe da turare sannan ta ciro kayanta da tuni dama sun rine da qamshin turaren wuta na kaya,doguwar rigar material ce cotton mai taushi yadda bazai dameta ba,saidai hannun rigar iya dantsenta ya tsaya,sai kuma mayafinshi wanda tayi rolling daya sauka mata har gwiwar hannu ya rufe hannun nata kenan bayan ta matse kanta da ribbom wanda yasha relaxer jiya,fuskarta ta kalla a mudubi,kayan sun mata kyau sosai,bata taba sanyasu ba saiyau,bata zaci ka zasuyi mata kyau haka ba,plat din takalmi ta sanya wanda ya dace da kayan sannan ta zira carbinta a yatsanta ta fito daga sashen.

Maryam ce kawai zaune a falon,saboda haka sallama tayi mata don fita haqqin addini,ganin ta amsa mata saita wuce kitchen ba tare data ce mata komai ba,don ta lura tunda annin ta tafi kowa kanshi rawa yake,dama ita maryam ba magana take mata ba,hakan ya sanya itama ta yi mata aji irin wanda ya dace da ita ta sanyata.

Bara'atu ke kiciniyar aiki ita kadsi,duk kitchen din a lalace yake kaman wanda akayi dafe dafe na mutum talatin
"Sannu da fitowar uwar masu gida" murmushi ta saki saita tuna da baba atika,tayi kewarsu sosai ita da anni
"Yauwa bara'atu sannu da aiki,ya haka gaba daya kitchen din ya kacame?" Ajiyar numfashi tayi sannan tace
"Ai kinsan aikin su waye,wallahi bansan me yasa suke abu ba bayan sunsan bai kamata ba sarai" sai aysha taji ranta ya baci,karo na farko tun sanda suka soma iskance iskancensu na kowacce ta dafa abinda ranta yayi mata,koda anyi girkin gida in general,koda su haidar dake yaran gidan duk abinda bara'atun ta dafa ci suke,bare ita da abinci bai dameta ba
"Kiyi haquri,komai mai wucewa ne,da zarar anni ta dawo naga wanda zaici gaba da yin hakan" aysha ta fada tana tausar zuciyarta,don bata son tayi musu magana sam,hannu ta sanya tana taya bara'atun gyaran kitchen din,sai da taga komai ya hau saiti sannan ta bar mata sauran,ta samu waje ta zauna suna jira jifa jifa,bayan ta zuba dan abincin da zata ci cikin plate.

Kadan kadan take tsakurar abincin suna hirarsu,bata wani ci da yawa ba zeenart ta shigo kitchen,tana ganin ayshan ta hade girar sama data qasa,tana yiwa ayshan kallon wata babbar naqasu a garesu,wadda ta kawo cikas da kuma hana ci gaban gudanuwar dukkan al'amuransu
"Bara'atu,maza maza dafamin couse jallop,ki saka nama da yawa a ciki yunwa nakeji" a ladabce bara'atun tace da ita
"Gafa abincin da kika asaka a aka dafa dazun baki cinye ba,sannan maryam da anty rahama dukansu an dafa musu abinci gasunan duk ba wanda ya cinye,ki duba ko wani abun a ciki zaiyi miki" ta fada tana buda mata fulasan dake shaqe da abinci
"Dalla malama ban tambayeki wannan ba,couse couse nake sha'awa shi nace ko dafamin"
"Ba za'a sake dafa komai ba a gidan nan sai Allah ya kaimu gobe" aysha ta fada hankali kwance kuma kari na farko tunda suka fara rashin mutunce mutuncensu,,saidai can qasan ranta a hasale take,ta karanci takunsu gaba dayansu babu abinda ke damunsu face tsantsar mugunta da almubazzaranci,saidai muguntar da qetar ma tafi yawa,waiwayawa zeenart tayi tana dubanta
"Au,harda su kaza a cin danqo?,ke kuma waya saka da ke?to bari na gaya miki tun ba'ayi nisa ba baki isa ba"cokalin hannunta ta aje sannan ta amsata
" na isa?,ban isa ba duka wannan bata taso ba ba'akai ga can ba,magana daya ce babu abinda za'a sake dafawa a gidan nan saidai idan har mun iya cinye duk abincin dake gidan nan muna da buqatar qari to wannan fa,barema nasan wannan abincin saidai a fitarwa da mabuqata a waje"
"Ke aisha!'muryar rahama dake takowa cikin kitchen din ta katsewa zeenart niyyar bata amsa da takeyi,hannunta harde a qirji fuskarta a dinke tsaf ta qaraso gaban ayshan,hannu kawai ta miqa mata sannan tace
"Bani muqullin dakin anni"sosai ta dubi rahaman cikin ido sannan tace
"Bamuyi wannan da anni ba"
"Ki bani malama ko,abina zan dauko a ciki"
"Idan kina da buqatarsa saidai ki jirayi dawowarta,saboda amana ce a gareni bazan iya wofantar da ita ba,ni dinma ban sake taka dakin ba tun randa na rufeshi"ta bata amsa tana janyo faranti ta rufe abincin dake gefanta,tsaiwa rahaman ta gyara tana dubanta cikin bacin rai
" ke ki saurara fa,naga alamun kina wuce gona da iri,saboda kinga an zuba miko ido kina yadda kikaga dama,toba tsoronki kowa keji ba"
"Duk saboda taga anni ta daure mata gindi ai take komai,ta fifitata a kanmu" zeenart dake cike ta fada
"Koma meya karki manta auroki akayi,a yau idan aka sakeki.magana ta qare,hakanan ana iya sauya mata amma dan uwa komai lalacewarshi lalala lalala"
"Don Allah anty rahama duka mai ya kawo wannan maganganun marasa dadi haka?" Bara'atu ta fada cikin tsoro da nuna rashin jin dadi,da hannu aysha ta dakatar da ita,murmushi ta saki tana dan kada qafarta kadan kadan sannan ta dubesu daya bayan daya
"Shi dan uwa suna ya tara ai,baku da labari?,da wani dan uwan gwara bare sau dubu?" Dukkansu sai kowacce tasha jinin jikinta,ba zasu so ace tasan komai game dasu ba,ganin karta ramfo wani abu ya sanya rahama sake yunqurowa cikin kurari tace
"Malama ki bani maqullin dakin uwarki anni tunda indai bana uwarrr........"
"Rahama!!" Dakakkiyar muryarshi mai cike da mazantaka ta karade ilahirin kitchen din gami da bada sautin amsa kuwwa,ba rahama ba hatta bara'atu da zeenart hantar cikinsu sai data kada,da hanzari dukkansu suka waiwaya bakin qofa,yana takowa ne cike da nutsuwa saidai kana duban fuskarshi zaka san cewa ran 'yan maza ya baci,tun kafin ya iso zeenart ta samu wajen jingina,yayin da rahama ta gyara tsaiwarta kamar mai shirin tarbar isowarshi saidai sam jikinta ne ke rawa takeson bawa kanta qwarin gwiwa,sai daya iso tsakiyarsu ya dubesu tsaf,sannan cikin wani irin sauti yace
"Matata?,kukewa haka a cikin gidanta?" Ya jefesu da tambayar yana binsu da kallo,zeenart kam babu bakin magana,sai rahama ce don kada ta bada kanta da shekarunta tayi qarfin halin cewa
"Haba khalipha?,kai bakagani ba kuma bakasan duk abinda take mana ba tunda anni ta tafi don kawai ta......"
"Will you shutup kosai nayi qasa qasa dake a nan" zaro ido tayi cikin mamaki,kalmar da bai taba gaya mata ita ba koda wasa,ko vanza yana dan bata girmanta ta wani bangaren saboda shekarunsu da suka kusa zuwa daya,waiwayawa yayi ya yiwa zeenart wani kallo wanda ya sanya take gumi ya rufeta
"Har da ke ko?....stupid,idiot....banda darajar anni da kuke ci ke kin isa kiga matata ma nare ki samu damar yin sa'insa da ita?banda kima da isar da anni ke dashi kin isa cin abincin gida na?,banda anni abincin gidana ko wanda na zubar ne bazan lamunci kuci ba" sai ya waiwaya wajen rahama
"Baki da damar da zaki nuna cewa anni wata ce a wajenki ko ke wata ce a wajenta,sanda muke wahala daga wannan mataki zuwa wancan na rayuwa kuna ina?,sanda muke tsakanin mutuwa da rayuwa kun taba tunawa damu?,kun taba kwana da tunanin ya rayuwar ayshatu zata kasance bayan kun sallamata a dangi?,to na meye a yanzu da muka samu nutsuwar zuciya da gangar jiki duka zaku kutso cikin rayuwarmu ku hanamu sukuni?,mu ba wawaye bane hakanan kyautatawa ba rashin sanin ciwo da darajar kai bane,saka sharri da alkhairi bai nufin ka manta komai daya faru,saka sharri da alkhairi bai nufin kai shashasha ne koka sarayar da dukka haqqi da mutuncinka" waiwayawa yayi ya dubi zeenart cikin kakkausar murya
"Kije ki kiramin dukkan yarinyar da tayi saura cikin gidan nan na baku minti biyu kacal" da hanzarinta ta fice,ba jimawa sai gasu sun dawo gaba daya,yatsunshi ya hada ya murza suka bata sauti sannan cikin kaushi yace
"Na baku nan da awa guda kowacce qarfe shida tayi mata cikin gidan mahaifanta,karku yadda na fito sallar magariba na samu daya daga cikinku...ko wacece kuwa...kome nisan da take dashi" ya qarashe maganar idanunshi yana kan rahama,tasan da ita yake ita da take nijer,wani abu mai tauri ta hadiye idanunta sun sauya launi saboda bacin rai,bai kuma bi ta kansu ba ya damqi hannun aysha da duka take jin babu dadi cikin ranta,tamkar ita ta zama sila kenan ta faruwar komai,batasan ya anni zata dauki hukuncin ba,kada hakan ya zama Silar tabarbarewar kyakkyawar alaqar dake tsakaninsu,haka suka ratsasu suka fice tana biye da shi.
Chapter 98 · 0% Book details