← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 114

Sashe 61

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dubanta ta dawo dashi kanta,filon dake saman kujerar ya janye mata alamun ta zauna,babu musu ta zauna din tana hade hannayenta waje daya,shima ya zauna daura da ita kansa na dan kallon qasa
"Kiyi haquri anni,naso muyi maganar dake kafin wannan lokacin amma na sha'afa saboda yawan hidimomin dake shigo min.....na samu wata dama ne daga wani kamfani dake da reshe a mafi yawancin qasashen duniya....to amma wannan dama daci gaba ba zasu tabbata min ba har sai na sake qaro karatuna,wanda hakan zai zamemin kamar jifan tsuntsu biyu da dutse daya ne,zan kai wani mataki mai girma cikin reshensu dake qasar nan,sannan namu kamfanin zai sake samun ci gaba da daukaka da yardar Allah,karatun duka zai daukeni ne tsahon shekara biyu....mun dauko humaira daga ainihin inda suje ruqonta don mu samawa rayuwarta nutsuwa jin dadi da kuma ci gaba,sai na tattauna da ita game da meye burint,ta sanarmin karatu ne,hakan ya sanya nayi tunanin me zai hana na maidata makaranta yadda take da buqata,nq bata zabi ita da kanta ta zabi waccar makarantar,tunda dama can ta cike first choice da second choice dinta,dalili kenan da yasa na tura ta can din....amma nasan hakan bai kamata ba,ya kamata na fara yin magana dake kafin duka na yanke wadan nan abubuwan" kai ta jinjina,ta tabbatar duk abinda khalipha zaiyi yana zurafafa tunaninsa kafin yanke komai,hakanan baya aiwatar da komai saida dalili,sannan tunda suke ita da shi bai taba yanke wani hukunci ba tare daya shawarceta ba,bai kamata don an samu akasi a wannan karon ta manta baya ba ta tuhumeshi
"Tunda har haka takeso babu damuwa,Allah ya bada sa'a ya taimaka,saidai kai din kar ka manta cewa da da yanzu ba daya bane,zaka tafi har tsahon shekara biyu wata uwa duniya?"
"Zan dinga zuwa duk sanda aka samu chance...."shuru ta sakeyi sannan daga bisani tace
"Shikenan..amma dai kayita istikhara ka barwa Allah zabinsa,idan alkhairi ne dukkan abubuwan daka zayyana Allah ya tabbatar da su,idan babu alkhairi kuma ina roqon ubangiji yayi maka musaya da mafi alkhairi,sannan kayi shawara da matarka"
"Amin ya Allah anni na gode...Allah ya jiqan magabata"
"Amin amin"
"Zan shiga ciki inason na sake hutawa kafin goma na wuce office..."
"Allah ya nuna mana" har ya miqe ya soma taku ta kira sunanshi,dawowa yayi da baya ya zauna hannun kujerar daya tashi a kai
"Khalipha...na baka shawara?" Cikin mamaki ya daga kai yana duban annin,lafazin nata ne ya dan bashi mamaki,kai ta kada
"Qwarai kuwa shawara,domin kuwa abinda ya shafi rayuwarka ne kai kadai" sai ya samu kanshi da kada kai
"Ka riqe aysha da kyau,don ina tsammatar ita din matar aure ce ta gari irin wadda kowanne namiji yakeso" iya abinda ta fada kenan taja bakinta ta tsuke,ya tabbata ta fadi hakanne ta bar mishi saura yaje yayi nazari a kai
"In sha Allahu" kawai ya fada yayi mata godiya ya miqe ya fice.

Har ya nufi sashensa sai ya sauya akala zuwa sashensu haidar,ya tura qofar ya shiga ya ratsa falonsu sai ya wuce dakin mus'ab,yana kwance dai dai saman abun sallah yana kwasar bacci abinshi,da alama yau baije masallaci ba a daki yayi sallah,hannu khalipha yasa ya daka masa duka a qeyarsa,miqewa yayi a zabure da har zai soma masifa ga zatonshi haidar ne sai kuma yaga khalipha tsaye a kanshi hannayensa harde a qirjinsa yana dubanshi,kai ya sadda yana gyara zamanshi
"Wato duk fadan da nake maka kan salla bisa jam'i baka ji ba ko?"qeya ya soma sosawa cike dajin nauyi da kunya
"wallahi ya khali...."
"Shutup.....kasan muhimmancin sallar asuba da isha'i a jam'i kuwa?,annabi S A W yace idan kaga sallolin nan guda biyu sune mafiya nauyi akan munafukai,suna yiwa munafuki wuya da nauyi, sallar asuba da isha'i,sannan ya sake cewa da mutane sunsan me yake cikinsu da sunzo musu koda dajan gindi ne...ka shiga taitayinka,karka sake ka shiga sahun wadancan mutanen,annabi S A W a lokacinsa yace badon mata da yara dake cikin gidajen wadanda basa halartar sallah asuba ba,da ya umarci wani yaja mutane sallah,shi kuma ya dauki itace ya zagaya gidajensu ya kunna musu wuta,ibn ummu makhtum mai yiwa annabi kiran sallahn farko makaho ne,ya nemi uzuri wajen annabi S A W kan bashi da d'an jagora,sannan hanya akwai kwazazzabai a hanya shin ya iya zama a gida yayi sallar asubarshi?,har annabi ya bashi daman ya zauna har ya tafi yayi kiranshi ya dawo,ya tambayeshi daga gida yana iya jiyo kiran sallah?,yace masa eh,yace to lallai lallai dole ya taho masallaci ya halacci sallah cikin jam'i,saikai da baka da wuni uzuri?,saika kai sha biyu na dare kan waya daya na dare,ka kasa tashi sallar asuba wace hujja zaka gayawa Allah" sosai jikinsa yayi sanyi,a hankali yace
"In sha Allah hakan bazai sake faruwa ba ya khalipha nayi alqawari"
"Ka kiyaye karna sake ganin irin haka ya faru,kada na sake zuwa masallaci ban ganka ba"
"In sha Allahu" ya fada cikin nadama
"Ka tabbatar ka fito qarfe goma zamu fita ni da kai,haidar ya wuce wudil,karka sake na rigaka fitowa" ya fadi yana bude qofar fita daga dakin
"In sha Allahu yaya" daga haka ya fice zuwa nashi dakin.

Koda ya shiga ya cire jallabiyyar jikinsa ya kwanta don ya sake ri tsawa sai ya kasa,maganganun anni ke dawo masa,ya kasa gane ina ta dosa,duk wata kulawa da yayi alqawari yana baiwa ayshan,ba wata takura cikin rayuwarta sam,ya kasa gano komai haka bacci yaqi daukarsa,dole ya haqura ya miqe ya sauya kayan jikinsa zuwa wanda yake amfani da su idan zai shiga gym dinshi ya fice zuwa dakin motsa jikin.

*mace nayin soyayya da dukkan zuciyarta,yayin da namiji keyin soyayya da dukkan qarfinsa*

34

Kwance take saman doguwar kujerar falonta tana kallo,tun dazu ta aika drivern gidan tare da hamid zai taho mata da shawarma don ita take kwadayin ci,saidai ta tashi babu kudi a hannuna,kasancewar ko naira biyar hamid bai bata a hannunta,hakanan ko cefane akai zaibi ba'asin ragowar canjinsa,kudinta dake accnt dinta takeso taje ta cira a atm saboda kwata kwata bata saba zama babu kudi a hannunta ba,batasan babu ba sam,mummynta ta tsaya mata bata taba neman abu ta rasa,har gwara daddy wani lokaci yakan hanata ko ya bata ba yadda ta buqata ba(qalube gareku iyaye,bawai burgewa bace ace komai yaro ya nema saika bashi,irin haka akwai matsala mai yawa a rayuwar yaro,baka da tabbas na cewa zaka ci gaba da rayuwa da shi har abada,koda kaci gaba din baka da tabbacin zaka dawwama cin wadatar da zaka dinga yi masa duk abinda yakeso,irin haka takan fara ne tun daga sanda yaro yake qarami,bani biyar bani goma bani ashirin,randa baki bashi ba ya zauna yayita yi kiki kuka,ba zaki barshi ba yaci kukansa har ya haqura saboda ya gane ba duk abinda kakeso kake samu ba,A'ah,sai kice ya isheki da kuka ungo ni ka barni na huta,daga ranar ya gane haka duk randa kika hanashi kuka zai saka miki har sai kin bashi din,diya mace 'yar gudan wani ce,idan ta saba duk abinda ta buqata zata samu kina da tabbacin wanda zata aura haka ne?,kina da tabbacin zaku rayu tare kici gaba da yi mata yadda takeso?,don Allah iyaye muyi qoqari mu gyara,kaza tana taka danta ne badon bata sonshi ba,a'ah saboda ta koya masa darasin rayuwa,yana kukan bakiso bakijin dadi har cikin ranki amma saiki danne don mi koya masa lallai abinda kikeso shiza'ayi ba abinda shi yakeso ba,Allah ya shirya mana zuri'a baki daya amin).

Driver dinne yayi sallama hannunshi riqe da baqar leda wadda taketa maiqo,miqewa tayi daga kwancen da take ta zauna sosai tana yatsina gami da cewa
"Miqo" ya qarasa ya miqa mata dariyar mugunta fal cikinsa yana dannewa,budewa tayi maimakon shawarma sai ta hangi wainar fulawa wadda ko wadataccen manja babu a ciki bare albasa,wurgi tayi da ledar cikin fushi
"Meye wannan malam zailani?,wannan wanne irin iskanci ne da rashin mutunci?,nace shawarma ka kawomin wainar fulawa a qaqqandare?" Cikin kwantar da murya yace
"Hajiya ba laifi na bane.....wallahi Allah muna cikin tafiya da shi muka biyo ta wani layi yaga ana soyawa,da kansa ya bada umarnin na tsaya naje na siyo miki....ita kanta yarinyar da ganin motar har kyautawa tayi ta sako gyara" miqewa tayi cikin fushi ta soma zazzageshi da masifa kamar zata cinyeshi danye ko kamar shi yayi mata,sake kwantar da murya yayi duk da dariya na cinsa a ciki,wulaqancin data taba yi masa rannan har yanzu bai manta ba yace
"Haka zaki haquri hajiya kici tunda duka da wancan da wannan din duk dangin fulawa ne"
"Malam zailani,ka tashi ka fiya ka bani wuri tun ban zagi uwarka ba" hannu yasa ya rufe bakinsa cikin tsananin mamaki,don bai zaci isgilancin nata yakai har nan ba
"Allah ya baki haquri" ya fada yana miqewa gami da ficewa daga dakin,komawa tayi saman kujera ta zauna kamar zata saka kuka tsabar baqinciki
"bari daddy ya aikomin da kudin da yayimin alqawari,naga wanda ya isa ya hanani cin abinda raina keso"gaba daya hamid ya sauya kamar bashi ba,a baya duk abinda tace masa tana da buqata kona miliyan nawa ne yi mata yake babu musu,sai gashi yanzu biyar tashi sai tayi da gaske take cinta,hatta da cima ya soma canza musu,don shi ba kasafai ma ya fiya cin abincin gidan ba,sam yadda ta dauki auren ba haka ta sameshi ba,ta zaci wata sabuwar duniya zata balle,ta dauki cewa rayuwar 'yanci ce fiye data gidansu,jin dadi zaman lafiya da kwanciyar hankali daya ninka na gidansu,rayuwar kece sa'a da tserewa sa'a,sai gashi komai yana zuwa mata a baibai,koya aysha?,tunatan datayi sai dariya ta qwace mata,hala itama tana can tana karbar nata gashin,ita da aka aureta ma ba so babu qauna,aka aureta ba tare da an shirya ba.
Chapter 61 · 0% Book details