Sashe 44
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk wadda ta gaya mata baqa kan rashin haihuwarta saita maida masa martani,inna yelwa kawai take dagawa qafa,itama randa ta gaji ranar ta maida mata,daganan cacar baki ta barke a tsakaninsu,har baffale ya dawo ya taddasu haka
"Na gaji da zaman wannan yarinyar mara mutunci a cikin zuri'ata,yarinyar kamar 'yar fata,kamar 'yar Allah bani?,to lallai lallai saidai ka saketa ta koma gidansu,yau dai ba zata kwana cikin zuri'ar modibbo ba" kai baffale ya kwantar yana bata haquri amma sam inna yelwa tace batasan wannan zance ba,tace saidai ya zaba ko matarsa ko ita,hakanan baffale yana ji yana gani yayi mata saki daya,tana kuka ta tattara kayanta ta dawo gida
Zaman nata a gida nan ma ba wani dadi ne dashi ba,saboda adawa suka dinga sosai da inna kulu,kusan ta wani janibin idan aka karanci halayyar mahaifiyarki lafiya lau za'a zauna da ita,duk da tana da wuyar sha'ani amma tana da dadin zama,duk da baffale ya saketa sai ya zamana kamar ba'a rabu ba,kullum suna tare kusan idan baida wani uzurin da zai gabatar to suna tare da ita,tuni ya maidata da baki,gidanne kawai bai maida ta ba,sanda labari ya kai kunnen inna yelwa tayi tashin hankalin rabasu amma ina sam haqanta yaqi cimma ruwa,a sannan ma ashe tana da ciki tun kafin ta baro gidan mahaifinki,bai bayyana kansa ba sai a sannan.
Tofa sai sabon rikici ya kunno kai,inna yelwa ta kafe kai da fata kan cewar ciki bana danta bane,yayin da mero ta kafe itama ciki na baffale ne,a sannan baffale baya nan,ya tafi neman kudi garin legos,rigima taqi ci taqi cinyewa,inda alqali ya sake shiga karo na biyu,yace a jira har sanda Allah zai dawo da baffale aji ta bakinsa,hakanan mahaifiyarki ta dinga rainon cikinta a gida,har sanda cikinta ya isa haihuwa baffale bai dawo ba,da yawa suna cewa zaunar da shi inna yelwa tasa akayi don kar ya dawo sabo da ita,haka dai zance keta yamadidi.
Wata tara da kwanaki ta haifeki,kama ta bayyana ta zahiri,kama irin ta ahalin gidan moddibo,ran kwana bakwai aka saka miki sunan aishatu,ba ragon suna ba rigar sakawa,babu kuma wani daga gidansu mahaifinki,a sannan naja'atu bata damu ba,tasan cewa da masoyinta ya dawo komai zai dai daita.
Watanki takwas sannan mahaifinki ya dawo,ranar daya dawo bai zarto ko ina ba sai wajen naja'atu,yayi murna matuqa da samunki sannan ya sake jaddadawa naja'atu cewa zata dawo dakinta ranar juma'ar da zata zagayo,a haka suka rabu,daga bangarenshi ba wanda yasan da wannan magana,ita kuwa tuni ta shaidawa 'yan uwanta ta kuma soma shiri,labari yakai kunnen inna yelwa,ta kuma ci alwashin daukar mataki,wanda shi ya kaita ga barin garinmu na kwana biyu sannan ta dawo,ba wanda ta gayawa me tayi,babu kuma wanda ta gayawa imda taje,ta dai dawo ta ja bakinta tayi shiru.
Ranar juma'ar kuwa aka yi mata rakiya,saidai inna yelwa ta tsare qofa ta hana a shiga da ita ciki,ta cika ta tunzura da taimakon zugar faccalolin ta,budar bakinta ma cewa tayi ita sam bata yarda da cewa ma diyar baffale bace goye a bayanta,tana shakka,tunda shi tunda ya dawo bai nemesu ba bai kuma yi maganar 'yar ba,bai kuma ce tashi bace,yayin da naja itama ta dage kan ba zata koma gida ba...gidan mijinta yau zata kwana,tunda shi ya maidata,babu dalilin komawarta gidansu,sannan 'ya ta baffale ce ko sama da qasa zasu hadu shi ya san da hakan,a nan inna yelwa ta bazama yara nemanshi sai gashi kuwa,tsatstsareshi tayi da ido tana tambayarsa yaushe ya maida naja bai nemi yardarta ba,rudewa yayi ba irin wadda ya saba ba duk sanda yayi mata laifi,ya kuma hau kame kamen cewa naja din ce ta dage kan komawarsu,abinda ya bata mamaki kenan ya daure mata kai,itadai tasan tare sukai maganarsu,ya kuma nemi ta koma din ya kuma amince,to amma duka ba wannan ne babban abinda ya girgizata ba,yadda inna yelwa ke shegantaka masa yarinya tana ba cikinsa bane yayi gum da bakinsa bayan yasan nashi ne,a nan fa halinta na qwatarwa kai 'yanci ya motsa,tace ba zata yarda ba,ta garzaya wajen alqali wanda ya saba shiga rigimar tasu,nan ya tattarasu ya tambayesu,sai a nan baffale ya amsa kaman yana dari dari da inna yelwa,da alamu dai akwai wata a qasa kenan,ganin ya amsa alqali ya kashe case din,naja'atu ta koma dakinta,saidai abinda baffalen yayi ba qaramin bata mata rai yayi ba.
Bayan komawarta sai zaman nasu ya sauya salo,ba wani jituwa can tsakaninsu,haka ma jama'ar gidan abun nasu ya sake qamari,bata shiga sabgar kowa suma basa shiga tata,duk wanda ya sake ya shiga gonarta kuwa zata nuna masa kurensa,bata barin kota kwana,hakan ya sake saka rashin jituwa mai qarfi tsakaninsu,baffale kam tana zaune da shine kawai saboda darajar soyayyar da sukayi a baya bata manta wannan ba,kasancewarta mace wadda bata da saurin mance abu.
Al'amarin ya fara ne lokacin da naja'atu tayi watanni hudu da dawowa gidanta,a sannan kika cika shekara guda a duniya,mahaifin naja'atu da muke kira baffa salihu ya hada mata gara mai yawa,garar haihuwa ce wadda ba'a yi mata ba saboda bata dakinta a sannan.
Ranar kai garar ina cikinsu,a sannan nima ina goyon suwaiba,naja batasan da zuwanmu ba,saboda haka tana sashinta,da sallamarmu gami da guda muka shiga gidan,duk matan gidan suna qasan bishiyar nan da sukan zauna kulli yaumin,sai aka rasa mai amsa mana sallamarmu sai ido suka bimu da shi,ganin haka rakiyar mai bin naja tace mu wuce bangaren najar kawai,kai tsaye can muka dosa,sanda muka shiga gidan mun isketa a sashenta tana dinkin hula,fes da ita ita da sashen nata kasancewarta gwanar tsafta,da farincikinta ta shinfide mana tabarma a tsakar gidanta tana fadin
"Amma kun yimin ba zata,da kun iske ni kuma bana nan fa?"
"Saimu koma da kayanmu mu cewa baffa salihu kince bakiso" dariya aka saki baki daya sannan tace cikin farinciki
"Kayan baffa ai bana mayarwa bane".
Kayan muka soma nuna mata,sai ta dakatar da mu tace bari ta kira sauran matan gidan,tayi hakanne saboda haka ake,a qa'ida ma su zasu tarbemu,uwar mijin kuma ita zata saukemu a wajenta,tana shirin fita da goyonki a bayanta saiga inna yelwa afujajan cikin fushi,sauran surukanta matan 'ya'yanta biye da ita,da kallo naja ta bisu da shi,duk sanda irin hakan ta faru tasan Allah ne kadai yasan sharrin da aka yi mata wajen inna yelwa,Allah ne kadai yasan me akaje aka gaya mata,tasan cewa yau babu zaman lafiya kenan,ta quduri aniyar komai ta fanjama fanjam ba zata lamunci a taka ta ba
"ku tashi ku fito munafukai algungumai irin masifa jinin tsiya,manufukar data gaya muku babu abinci a gidan nan qaryarta tasha qarya...tun kafin ayi daran akai kwandi....tun kafina a haifi uwar mai sabulu balbela take da farinta,bamu gaji yunwa ba bamu santa ba,kuma zuwanta cikinmu bazaisa a fara yunwa ba,ku kwashe tsiyarku ku koma da ita tun rayuka basu baci ba" baba ladi dattijuwar cikinmu,wadda take yaya ce ga baffa salihu tace
"Haba yelwa...haba ke kuwa....idan ana harkar arziqi ai tsiya bata shigo ba,gara ce ta jikarki da aka saba yi wadda bamuyi ba wancan karon saboda najar bata dakinta yanzu muka biya ta..." Tsawa inna yelwa ta daka mata gami da kiranta tsohuwar banza tayi wa mutane shiru,hakan shi ya sake tunzura zuciyar naja itama ta tanka
"Karki sake kiran uwata da tsohuwar munafuka...akan meye ne inna duka wannan masifa da bala'in?,tunda na auri danki ban huta ba...wai duka dai akan baffale ne wannan?"
"Eh...a kansa ne idan kin haifu cikin uwarki sahura da ubanki salihu ki barmin dana kiga idan baqar magana ma zata sake shiga tsakanina dake har abada....kai manu...matsa kuyimin koli koli da kayan wadan nan matsiyatan na daina ganinsu" ta baiwa matasan jikokinta umarni,kafin qiftawa da bismillah yaran sun soma diban kayan suna watsawa farfajiyar gidan,wadda ki cike da kwatami da qazanta,haka suka dinga watsi da duk abinda muka zo da shi yana dilmiya cikin tabi da gulbi muna kallo,tsabar baqinciki naja kuka ta saka ta dora hannu a ka,ana tsaka da wannan abu baffale ya shigo,ranta sai ya danyi sanyi tayi wajenshi tana zayyana masa abinda yake faruwa ga zatonta zai dakatar da su,sai yayi wajen mahaifiyarsa wadda ta dubeshi kai tsaye ta bashi umarni
"Ka saketa baffale idan ni na haifeka,saki biyunta nakeso ka qarasa mata" juyawa yayi ya dubi naja,kai take kadawa cikin kuka
"Karka aikata abinda zai zama dana sani a garemu...karka karya alqawarin daka yimin..."
"Bazan taba dana sani ba don na rabu dake.....naja na sakeki saki biyu....kai manu ku shiga dakinta ku fitar mata da kayanta" ya sake baiwa yaran umarni,kafin kace kwabo kayan ta sun soma watangaririya,tun daga tsakat gida har zuwa katangar bayan gida ta nan suka dinga jefa wasu sai da muka zagaya muka tsince,hatta da suturarta ta sawa basu damu da wankinta da guga ba haka suka dinga watsi da ita.
Mun jata kan ta wuce kawai mu tafi don wasu kayan ma ba zasu debu ba amma ta doje,ta koma ta dubi innayelwa daje tsaye ita da surukanta,wanda kowaccw farinciki take yau naja tabar gidan tsabar hassada da kishin banza mara amfani
"Yelwa....saboda danki kika yimin haka?....burinki ya cika danki ya sakeni....amma ki sani akwai ranar nadama,idan danki ne na barshi kenan har abada,ba danki ba duk abinda ya danganceku ma..." Ta qarashe maganar tana kwantoki daga bayanta,a sannan kina bacci duka bakisan abinda ke faruwa ba,shimfide musu ke tayi,tana shirin juyawa inna yelwa ta saka dariya
"idan kin haifu ke cikakkiyar 'yar halak ce ki sallama mana ita kiga idan ba zata rayu ba" wani irin kallo ta juya tayiwa inna yelwa,ta yiwa baffale nashi sannan ta qaraso cikinmu cikin matsanancin fushi mukayi gaba,a sannan babu wanda yaga rashin dacewar barinki saboda bacin ran abinda suka yi mana,a sannan babu wanda ya zaci wannan qiyayyar zata shafeki ta raba tsakaninki da mahifiyarki,babu wanda ya zaci lamarin zaiyi dogon zango har ya cimma wadan nan shekarun,yadda naja tace ta bar baffale har abada hakan ce ta faru,hatta da qofar gidan ta daina wucewa,hakanan duk wani lamari daya danganceki ta shafeshi a babin rayuwarta,bata zancanki bata yarda ayi mata zancanki,bata rabarki bata yarda ki rabeta.
"Na gaji da zaman wannan yarinyar mara mutunci a cikin zuri'ata,yarinyar kamar 'yar fata,kamar 'yar Allah bani?,to lallai lallai saidai ka saketa ta koma gidansu,yau dai ba zata kwana cikin zuri'ar modibbo ba" kai baffale ya kwantar yana bata haquri amma sam inna yelwa tace batasan wannan zance ba,tace saidai ya zaba ko matarsa ko ita,hakanan baffale yana ji yana gani yayi mata saki daya,tana kuka ta tattara kayanta ta dawo gida
Zaman nata a gida nan ma ba wani dadi ne dashi ba,saboda adawa suka dinga sosai da inna kulu,kusan ta wani janibin idan aka karanci halayyar mahaifiyarki lafiya lau za'a zauna da ita,duk da tana da wuyar sha'ani amma tana da dadin zama,duk da baffale ya saketa sai ya zamana kamar ba'a rabu ba,kullum suna tare kusan idan baida wani uzurin da zai gabatar to suna tare da ita,tuni ya maidata da baki,gidanne kawai bai maida ta ba,sanda labari ya kai kunnen inna yelwa tayi tashin hankalin rabasu amma ina sam haqanta yaqi cimma ruwa,a sannan ma ashe tana da ciki tun kafin ta baro gidan mahaifinki,bai bayyana kansa ba sai a sannan.
Tofa sai sabon rikici ya kunno kai,inna yelwa ta kafe kai da fata kan cewar ciki bana danta bane,yayin da mero ta kafe itama ciki na baffale ne,a sannan baffale baya nan,ya tafi neman kudi garin legos,rigima taqi ci taqi cinyewa,inda alqali ya sake shiga karo na biyu,yace a jira har sanda Allah zai dawo da baffale aji ta bakinsa,hakanan mahaifiyarki ta dinga rainon cikinta a gida,har sanda cikinta ya isa haihuwa baffale bai dawo ba,da yawa suna cewa zaunar da shi inna yelwa tasa akayi don kar ya dawo sabo da ita,haka dai zance keta yamadidi.
Wata tara da kwanaki ta haifeki,kama ta bayyana ta zahiri,kama irin ta ahalin gidan moddibo,ran kwana bakwai aka saka miki sunan aishatu,ba ragon suna ba rigar sakawa,babu kuma wani daga gidansu mahaifinki,a sannan naja'atu bata damu ba,tasan cewa da masoyinta ya dawo komai zai dai daita.
Watanki takwas sannan mahaifinki ya dawo,ranar daya dawo bai zarto ko ina ba sai wajen naja'atu,yayi murna matuqa da samunki sannan ya sake jaddadawa naja'atu cewa zata dawo dakinta ranar juma'ar da zata zagayo,a haka suka rabu,daga bangarenshi ba wanda yasan da wannan magana,ita kuwa tuni ta shaidawa 'yan uwanta ta kuma soma shiri,labari yakai kunnen inna yelwa,ta kuma ci alwashin daukar mataki,wanda shi ya kaita ga barin garinmu na kwana biyu sannan ta dawo,ba wanda ta gayawa me tayi,babu kuma wanda ta gayawa imda taje,ta dai dawo ta ja bakinta tayi shiru.
Ranar juma'ar kuwa aka yi mata rakiya,saidai inna yelwa ta tsare qofa ta hana a shiga da ita ciki,ta cika ta tunzura da taimakon zugar faccalolin ta,budar bakinta ma cewa tayi ita sam bata yarda da cewa ma diyar baffale bace goye a bayanta,tana shakka,tunda shi tunda ya dawo bai nemesu ba bai kuma yi maganar 'yar ba,bai kuma ce tashi bace,yayin da naja itama ta dage kan ba zata koma gida ba...gidan mijinta yau zata kwana,tunda shi ya maidata,babu dalilin komawarta gidansu,sannan 'ya ta baffale ce ko sama da qasa zasu hadu shi ya san da hakan,a nan inna yelwa ta bazama yara nemanshi sai gashi kuwa,tsatstsareshi tayi da ido tana tambayarsa yaushe ya maida naja bai nemi yardarta ba,rudewa yayi ba irin wadda ya saba ba duk sanda yayi mata laifi,ya kuma hau kame kamen cewa naja din ce ta dage kan komawarsu,abinda ya bata mamaki kenan ya daure mata kai,itadai tasan tare sukai maganarsu,ya kuma nemi ta koma din ya kuma amince,to amma duka ba wannan ne babban abinda ya girgizata ba,yadda inna yelwa ke shegantaka masa yarinya tana ba cikinsa bane yayi gum da bakinsa bayan yasan nashi ne,a nan fa halinta na qwatarwa kai 'yanci ya motsa,tace ba zata yarda ba,ta garzaya wajen alqali wanda ya saba shiga rigimar tasu,nan ya tattarasu ya tambayesu,sai a nan baffale ya amsa kaman yana dari dari da inna yelwa,da alamu dai akwai wata a qasa kenan,ganin ya amsa alqali ya kashe case din,naja'atu ta koma dakinta,saidai abinda baffalen yayi ba qaramin bata mata rai yayi ba.
Bayan komawarta sai zaman nasu ya sauya salo,ba wani jituwa can tsakaninsu,haka ma jama'ar gidan abun nasu ya sake qamari,bata shiga sabgar kowa suma basa shiga tata,duk wanda ya sake ya shiga gonarta kuwa zata nuna masa kurensa,bata barin kota kwana,hakan ya sake saka rashin jituwa mai qarfi tsakaninsu,baffale kam tana zaune da shine kawai saboda darajar soyayyar da sukayi a baya bata manta wannan ba,kasancewarta mace wadda bata da saurin mance abu.
Al'amarin ya fara ne lokacin da naja'atu tayi watanni hudu da dawowa gidanta,a sannan kika cika shekara guda a duniya,mahaifin naja'atu da muke kira baffa salihu ya hada mata gara mai yawa,garar haihuwa ce wadda ba'a yi mata ba saboda bata dakinta a sannan.
Ranar kai garar ina cikinsu,a sannan nima ina goyon suwaiba,naja batasan da zuwanmu ba,saboda haka tana sashinta,da sallamarmu gami da guda muka shiga gidan,duk matan gidan suna qasan bishiyar nan da sukan zauna kulli yaumin,sai aka rasa mai amsa mana sallamarmu sai ido suka bimu da shi,ganin haka rakiyar mai bin naja tace mu wuce bangaren najar kawai,kai tsaye can muka dosa,sanda muka shiga gidan mun isketa a sashenta tana dinkin hula,fes da ita ita da sashen nata kasancewarta gwanar tsafta,da farincikinta ta shinfide mana tabarma a tsakar gidanta tana fadin
"Amma kun yimin ba zata,da kun iske ni kuma bana nan fa?"
"Saimu koma da kayanmu mu cewa baffa salihu kince bakiso" dariya aka saki baki daya sannan tace cikin farinciki
"Kayan baffa ai bana mayarwa bane".
Kayan muka soma nuna mata,sai ta dakatar da mu tace bari ta kira sauran matan gidan,tayi hakanne saboda haka ake,a qa'ida ma su zasu tarbemu,uwar mijin kuma ita zata saukemu a wajenta,tana shirin fita da goyonki a bayanta saiga inna yelwa afujajan cikin fushi,sauran surukanta matan 'ya'yanta biye da ita,da kallo naja ta bisu da shi,duk sanda irin hakan ta faru tasan Allah ne kadai yasan sharrin da aka yi mata wajen inna yelwa,Allah ne kadai yasan me akaje aka gaya mata,tasan cewa yau babu zaman lafiya kenan,ta quduri aniyar komai ta fanjama fanjam ba zata lamunci a taka ta ba
"ku tashi ku fito munafukai algungumai irin masifa jinin tsiya,manufukar data gaya muku babu abinci a gidan nan qaryarta tasha qarya...tun kafin ayi daran akai kwandi....tun kafina a haifi uwar mai sabulu balbela take da farinta,bamu gaji yunwa ba bamu santa ba,kuma zuwanta cikinmu bazaisa a fara yunwa ba,ku kwashe tsiyarku ku koma da ita tun rayuka basu baci ba" baba ladi dattijuwar cikinmu,wadda take yaya ce ga baffa salihu tace
"Haba yelwa...haba ke kuwa....idan ana harkar arziqi ai tsiya bata shigo ba,gara ce ta jikarki da aka saba yi wadda bamuyi ba wancan karon saboda najar bata dakinta yanzu muka biya ta..." Tsawa inna yelwa ta daka mata gami da kiranta tsohuwar banza tayi wa mutane shiru,hakan shi ya sake tunzura zuciyar naja itama ta tanka
"Karki sake kiran uwata da tsohuwar munafuka...akan meye ne inna duka wannan masifa da bala'in?,tunda na auri danki ban huta ba...wai duka dai akan baffale ne wannan?"
"Eh...a kansa ne idan kin haifu cikin uwarki sahura da ubanki salihu ki barmin dana kiga idan baqar magana ma zata sake shiga tsakanina dake har abada....kai manu...matsa kuyimin koli koli da kayan wadan nan matsiyatan na daina ganinsu" ta baiwa matasan jikokinta umarni,kafin qiftawa da bismillah yaran sun soma diban kayan suna watsawa farfajiyar gidan,wadda ki cike da kwatami da qazanta,haka suka dinga watsi da duk abinda muka zo da shi yana dilmiya cikin tabi da gulbi muna kallo,tsabar baqinciki naja kuka ta saka ta dora hannu a ka,ana tsaka da wannan abu baffale ya shigo,ranta sai ya danyi sanyi tayi wajenshi tana zayyana masa abinda yake faruwa ga zatonta zai dakatar da su,sai yayi wajen mahaifiyarsa wadda ta dubeshi kai tsaye ta bashi umarni
"Ka saketa baffale idan ni na haifeka,saki biyunta nakeso ka qarasa mata" juyawa yayi ya dubi naja,kai take kadawa cikin kuka
"Karka aikata abinda zai zama dana sani a garemu...karka karya alqawarin daka yimin..."
"Bazan taba dana sani ba don na rabu dake.....naja na sakeki saki biyu....kai manu ku shiga dakinta ku fitar mata da kayanta" ya sake baiwa yaran umarni,kafin kace kwabo kayan ta sun soma watangaririya,tun daga tsakat gida har zuwa katangar bayan gida ta nan suka dinga jefa wasu sai da muka zagaya muka tsince,hatta da suturarta ta sawa basu damu da wankinta da guga ba haka suka dinga watsi da ita.
Mun jata kan ta wuce kawai mu tafi don wasu kayan ma ba zasu debu ba amma ta doje,ta koma ta dubi innayelwa daje tsaye ita da surukanta,wanda kowaccw farinciki take yau naja tabar gidan tsabar hassada da kishin banza mara amfani
"Yelwa....saboda danki kika yimin haka?....burinki ya cika danki ya sakeni....amma ki sani akwai ranar nadama,idan danki ne na barshi kenan har abada,ba danki ba duk abinda ya danganceku ma..." Ta qarashe maganar tana kwantoki daga bayanta,a sannan kina bacci duka bakisan abinda ke faruwa ba,shimfide musu ke tayi,tana shirin juyawa inna yelwa ta saka dariya
"idan kin haifu ke cikakkiyar 'yar halak ce ki sallama mana ita kiga idan ba zata rayu ba" wani irin kallo ta juya tayiwa inna yelwa,ta yiwa baffale nashi sannan ta qaraso cikinmu cikin matsanancin fushi mukayi gaba,a sannan babu wanda yaga rashin dacewar barinki saboda bacin ran abinda suka yi mana,a sannan babu wanda ya zaci wannan qiyayyar zata shafeki ta raba tsakaninki da mahifiyarki,babu wanda ya zaci lamarin zaiyi dogon zango har ya cimma wadan nan shekarun,yadda naja tace ta bar baffale har abada hakan ce ta faru,hatta da qofar gidan ta daina wucewa,hakanan duk wani lamari daya danganceki ta shafeshi a babin rayuwarta,bata zancanki bata yarda ayi mata zancanki,bata rabarki bata yarda ki rabeta.