Sashe 65
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hanan na idar da sallah aka sake knocking,wata matar ce ta sake shigowa,fara ce itama qal da ita,ba siririya bace haka bamai qiba ba,tana sanye da doguwar rigar material da mayafinta,a qalla zata girmewa su aysha da shekara hudu haka,hannunta rungume da yarinya wadda bata wuce shekara daya ba,sai jakar mata data ratayo,bayanta security ne mata dauke da jakankuna manya guda biyu,da sauri hanan ta miqe tana fadin
"Oyoyo hunaifa" ta karbe yarinyar daga hannun mamata,murmushi matar take idanunta na kan aysha
"Sannu da zuwa" ayshan ta fada itama tana murmushi
"Yauwa sannunkj,baquwa muka samu ne hanan?" Waiwayawa tayi tana duban aysha cikin murmushi
"Cikon abokiyar zamanmu ne"
"Ma sha Allah,da fatan kinzo lafiya" ta fada fana zama gefan gadonta
"Lafiya alhmdlh" ta bata amsa tana karbar hunaifa daga hannun hanan,karon farko yarinyar ta shiga ranta,tayi kyau cikin overoll pink da hula
"Ummm su mmn hunaifa,daga cewa yanzu yanzu zaki dawo sai kuma yanzu aka ganki,kodai baban hunaifa ne ya riqeki?" Dariya ta danyi tana sake hayewa gadon sosai
"Kedai bari kawai,shima yau zai wuce abuja sai dana tsaya na kintsa shi tukunna" ta fadi tana dariya,itama dariya hanan takeyi
"Kinsan yanzun zamani ya canza,idan baki iya tsayawa kin kame mijinki da kyau ba kina can kin sau baki wata zata kame miki shi,koba haka ba qanwata?" Ta qarasa fadi tana duban aysha,murmushi kawai tayi ta gyada kanta,a hankali ta furta
"Haka ne"dariya hanan ta kuma sawa
"Eh lallai wlh kam da gaskiyarki wallahi maman hunaifa,nifa iya zaman kwana hudu da mukayi dake ba qaramin qaruwa nayi ba,wannan idan na tashi aure gidanki zanzo na tare"
"Muna miki maraba,amma ki taho da glass din sawa idonki,donmu gidanmu duk baqon da zaizo saiya shirya" ihun dariya hanan ta saki yayin da aysha ke kallonsu tana murmushi,abun ya qayatar da ita sosai,haka suka jima suna hira abinsu cikin dakin,daga bisani maman hunaifa wadda asalin sunanta shine raihana tayi qorafin yunwa,saurin da takeyi ya hanata tsaiwa taci,cooler din aysha hanan ta tura mata,dubanta mmn hunaifa tayi
"A ina kika samu abinci?,kekam nasan ba abinda kika tsana irin girki bare nace ke ke kikayi"
Dariya hanan tayi tana cire hijabin sallarta ta maida rolling dinta
"Baquwarmu ce wlh da qoqari,nima zuwa nayi na tadda ta dafa"
"Sannu fa,na gode" maman hunaifa ta fada tana duban aysha,wadda tayi shuru tana mamakin hanan da akace ba abinda ga tsana irin girki,itakam sam bata ga abin wahala ko abin gudu a girki ba,sun jima suna hira a tsakaninsu,duk gaba dayansu 'yan hira ne,idan ka dauke aysha da wani abun saidai tayi murmushi kawai,hakanan yanayinsu taji yayi mata,kuma bisa dukkan alamu zataji dadin zama da su,har wajen takwas na dare suna hirarsu kowa na baiwa dan uwansa labarin dan abinda ya shafi rayuwarsa wanda ya kamata dan uwansa ya sani,itadai aysha nata surutun kadan ne,abun da ya tashi hirar tasu kiran wayar hanan da akayi ta haye gado ta barsu a nan,daga bisani itama maman hunaifa bayan ta gama lallaba hunaifa tayi bacci ta sungumi tata wayar ta haye gado,sai ya zamana aysha ce kawai ta rage,itama saita haye nata gadon ba don tana da abunyi ba,likimo tayi tana juya wayarta gami da tunanin wanda zata kira,daga bisani sai ta gwada wayar aliya,a kashe ta taddata,tilas ta sauya akalar kiran nata zuwa ga layin anni,bugu uku ta daga,muryarta cike da fara'a take cewa
"Yanzu bada jimawa ba muka gama maganarki ni dasu haidar a wajen cin abinci,yau gidan duk sai ya yoye babu dadi,khalipha ya wuce shima zai fara tsayawa a legos,rahama ta tafi gida" murmushi mai sauti ta fitar tana jin kewarsu
"Nima nan ba dadi"murmushin itama anni tayi cikin jin dadi
"To ya za'ayi,ba yadda banyi dashi ya barmin diyata a kusa ba yace min can yafi"dariya tayi
" zan saba ai anni in sha Allahu"
"To Allah ya taimaka yayi jagora,Allah ya hadaki da mutanen zama na qwarai"
"Amin anni na gode Allah ya qara girma" yan mintuna suka qara akan layi wanda yawanci tana tambayar annin jikinta da yadda tayi da 'yan abubuwan da aysha ta dauke mata,tace wani haka ta lallaba tayi wani ta haqura,da yake ba komai takeson masu aiki suyi mata ba,daga qarshe sukayi sallama da annin,bayan ta dan ja hankalinta kan ta kula da mutuncinta,wanda kusan dai duk kaman tana taya khaliphanta ne kishinta.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tsaki taja bayan ta gama zazzage ragowar madarar data rage a kwalin ta wurgar da kwalin gefe tana masifa da mita a ranta,idan akace mata haka zatayi rayuwa da hamid koda mafarki tayi zata qaryata mafarkin,wannan tafiyar da zaiyi babu abinda bai bar mata ba,ya dan rage maqon nashi kadan wanda ada bai wani dameta sosai ba saboda tana da kudinta a accnt,duk abinda take buqata shi take tabawa ta siya abinta,to wancan satin da sukayi waya da daddy yayi mata fada kan ta rage kashe kudi,ya duba accnt nata yaga kudinta sun soma yin qasa sosai,har yana cewa zai sama mata business ta dinga yi,don baison almubazzaranci da rashin adani,ya kawo mata misali da aysha wanda hakan ya qona ranta sosai,ya gaya mata har yanzu babu abinda ta cira a accnt din daya bude musu,tunawa tayi da daya accnt din nata data bude tun tana gida,bayan ta tare ta bawa a hamid ajiyar atm din,kudin cikin accnt din duk kayan aysha ne da take karbewa wanda tasha alwashin sun daina hada komai iri daya take baiwa mommy ta saka a kayanta ta saida saita karbi kudin,ciki harda wannan sabuwar motar tata da daddy ya siya musu iri daya.
Murmushi ta saki tana ayyanawa a ranta yau ga ranar plan dinta nan,a nutse ta soya qwai guda biyu daya rage mata da sauran kayan cikin data baiwa mai gadi ya kaiwa matarsa ta dafa mata ta dumamashi,don mai aikinta tunda hamid yayi tafiya itama ta tafi,shi yace mata ta tafi tunda shima baya nan,amfanin zamanta idan yana nan tunda asma'un bata iya komai ba,tunda baya nan tayi tafiyarta ita asma'un tasan ya zatayi da kanta,ya gaya mata cewar zai cire kudin aikin kwanakin bazai bata ba,tana ji tana gani ta tafin,ba irin bacin ran da asma'un batayi ba,qarshe mummy ta kira ta yiwa qorafi tana kuka,baqinciki ya hana mummyn magana,itakam har ta soma gajiya da jin matsaloli,ba ranarvAllah da zata fito ta fadi bata ji matsala daga asma'u ba sai dai daikun ranaku,wai dama haka auren masu kudin yake ne ko kuwa?,a'ah ta baiwa kanta amsa,koda wasa aysha bata taba kiranta tayi koda tarin da zai nuna cewa akwai wani abu dake faruwa ba tare da ita mara kyau,hakanan ita karan kanta shaida ce cewa bata taba wani kuka da daddy ba,hakanan mummy ke turo mata lantana ta wuni,itama daga bisani data gaji da wahala da ayyukan asma'un da basa qarewa ta tsiri ciwon qarya,dole aka sarara mata.
A nutse ta gama cin abincinta tana jin nishadi zata ciro kudinta ta kashe sabgar gabanta,don dama tun wancan satin ta rasa ya zatayi,za'ayi bikin daya daga cikin qawayensu,kuma kowacce idan bikinta ya tashi gudun mawa ake bata ta qasaita,samanta ta koma ta fesa wanka bayan ta shirya ta soma duba dakinta don dakin hamid din bai barinsa a bude,ko kasuwa zai fita saiya garqame abinsa ga tagi da muqullinsa bare wannan tafiya ta satittika,cikin sa'a kuwa ta gano atm din,ba bata lokaci ko jiran neman izini ta saka mayafinta ta fice daga gidan.
Sau uku tana tada motar taqi tashi,saidaga bisani ta lura ashe mai ne babu,haka ta sauka ta bada dari biyar aka siyo mata a bakin titi wajen 'yan bututu ta zuba ta tashi motar ta fice.
Ta samu layi sosai a ATM din,babu yadda ta iya haka tayita jira saboda taga mafadata aka hada a wajen har layi yazo kanta,saidai ga mamakinta sai ake cemata babu kudi a accnt dinta
"A'ah!" Ta fadi cike da madaukakin mamaki,ita tasan kudin ciki ya kusa dubu dari takwas da wani abu,sake maidawa tayi aka sake gaya mata hakan,take gumi ya soma yanko mata
"Hajiya kiyi da jiki da Allah,muna da yawa fa" cewar wani matashi dan ci da zuci dake bayanta
"Ba kudi ba a accnt din nata amma tazo ta wani faka mota tana yiwa mutane qarya tazo cirar kudi" inji wanda yafi kusa da ita ya fadi sanda ta fice daga layin da katin a hannunta,waiwayowa tayi da niyyar sille mishi,saboda tana ganin a girmanta ta girmi ayi mata hakan,saidai yadda idanu sukayi mata yawa yasa tayi hanzarin yin gaba ta fada motarta
Bata tsaya ba saidata isa gida,ta fada saman kujera ranta na quna,tana son tayi kuka tana cijewa,to yaushe wai har hamid ya fidda kudaden nan bata sani ba?,a fusace ta dauko wayarta ta nemi lambobinsa,bugu hudu aka dauka,saidai maimakon muryarsa muryar mace taji,a zabure ta daga wayar tana dubanta sai taga an yanke kiran,sake kiranshi tayi harta katse ba'a daga ba,sai data sake bi sannan aka daga,wannan karon shine
"Wace yar iskar ce ta daga wayarka?"
"Au....shi kika kirani kiji uwata?" Tunani ne ya fado mata,idan ta biyeshi suyita ne zatayi biyu babu,gwara ta fara sanin ina kudadenta suke tukunna
"Atm dina na wajenka,na dauka yau zanyi amfani da shi amma babu komai cikin accnt din"
"Anyi amfani dasu" ya bata amsa kai tsaye
"Kaman yaya hamid?,me kake nufi?" Ta tambayeshi tana gimtse fuska tamkar yana wajen
"Abinda nake nufi nace miki nayi amfani da su"
"Kudin nawa hamid?,wannan wanne irin abu ne daga baka ajiya zaka dauki haqqina kaci?"
"Dakata da Allah malama.." Ya katseta ba tare data gama fadin abinda zata fada din ba
"Gori zakimin kome?,karki gayan maganar banzan,nawa ni na kashe miki a rayuwa,nawa kike cimin yanzu?,to na cinye saiki qwata idan kina da qarfi" yana kaiwa nan ya datse kiran,kuka kawai ta saki saboda tsabar baqinciki da takaici,nan saman kujera ta zube duniya nayi mata qunci,wannan wace iriyar rayuwa ce,me ta yiwa hamid yake saka mata da wannan abubuwa?,haka ta dinga qwalla tana tambayar kanta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
36
Cikin sati uku kacal ta soma gane kan abubuwa na cikin makarantar,yanayin rayuwar da banbancin muhalli,yanayin jama'a kala kala,banbancin halaye dabi'u jinsi da kuma yare.
"Oyoyo hunaifa" ta karbe yarinyar daga hannun mamata,murmushi matar take idanunta na kan aysha
"Sannu da zuwa" ayshan ta fada itama tana murmushi
"Yauwa sannunkj,baquwa muka samu ne hanan?" Waiwayawa tayi tana duban aysha cikin murmushi
"Cikon abokiyar zamanmu ne"
"Ma sha Allah,da fatan kinzo lafiya" ta fada fana zama gefan gadonta
"Lafiya alhmdlh" ta bata amsa tana karbar hunaifa daga hannun hanan,karon farko yarinyar ta shiga ranta,tayi kyau cikin overoll pink da hula
"Ummm su mmn hunaifa,daga cewa yanzu yanzu zaki dawo sai kuma yanzu aka ganki,kodai baban hunaifa ne ya riqeki?" Dariya ta danyi tana sake hayewa gadon sosai
"Kedai bari kawai,shima yau zai wuce abuja sai dana tsaya na kintsa shi tukunna" ta fadi tana dariya,itama dariya hanan takeyi
"Kinsan yanzun zamani ya canza,idan baki iya tsayawa kin kame mijinki da kyau ba kina can kin sau baki wata zata kame miki shi,koba haka ba qanwata?" Ta qarasa fadi tana duban aysha,murmushi kawai tayi ta gyada kanta,a hankali ta furta
"Haka ne"dariya hanan ta kuma sawa
"Eh lallai wlh kam da gaskiyarki wallahi maman hunaifa,nifa iya zaman kwana hudu da mukayi dake ba qaramin qaruwa nayi ba,wannan idan na tashi aure gidanki zanzo na tare"
"Muna miki maraba,amma ki taho da glass din sawa idonki,donmu gidanmu duk baqon da zaizo saiya shirya" ihun dariya hanan ta saki yayin da aysha ke kallonsu tana murmushi,abun ya qayatar da ita sosai,haka suka jima suna hira abinsu cikin dakin,daga bisani maman hunaifa wadda asalin sunanta shine raihana tayi qorafin yunwa,saurin da takeyi ya hanata tsaiwa taci,cooler din aysha hanan ta tura mata,dubanta mmn hunaifa tayi
"A ina kika samu abinci?,kekam nasan ba abinda kika tsana irin girki bare nace ke ke kikayi"
Dariya hanan tayi tana cire hijabin sallarta ta maida rolling dinta
"Baquwarmu ce wlh da qoqari,nima zuwa nayi na tadda ta dafa"
"Sannu fa,na gode" maman hunaifa ta fada tana duban aysha,wadda tayi shuru tana mamakin hanan da akace ba abinda ga tsana irin girki,itakam sam bata ga abin wahala ko abin gudu a girki ba,sun jima suna hira a tsakaninsu,duk gaba dayansu 'yan hira ne,idan ka dauke aysha da wani abun saidai tayi murmushi kawai,hakanan yanayinsu taji yayi mata,kuma bisa dukkan alamu zataji dadin zama da su,har wajen takwas na dare suna hirarsu kowa na baiwa dan uwansa labarin dan abinda ya shafi rayuwarsa wanda ya kamata dan uwansa ya sani,itadai aysha nata surutun kadan ne,abun da ya tashi hirar tasu kiran wayar hanan da akayi ta haye gado ta barsu a nan,daga bisani itama maman hunaifa bayan ta gama lallaba hunaifa tayi bacci ta sungumi tata wayar ta haye gado,sai ya zamana aysha ce kawai ta rage,itama saita haye nata gadon ba don tana da abunyi ba,likimo tayi tana juya wayarta gami da tunanin wanda zata kira,daga bisani sai ta gwada wayar aliya,a kashe ta taddata,tilas ta sauya akalar kiran nata zuwa ga layin anni,bugu uku ta daga,muryarta cike da fara'a take cewa
"Yanzu bada jimawa ba muka gama maganarki ni dasu haidar a wajen cin abinci,yau gidan duk sai ya yoye babu dadi,khalipha ya wuce shima zai fara tsayawa a legos,rahama ta tafi gida" murmushi mai sauti ta fitar tana jin kewarsu
"Nima nan ba dadi"murmushin itama anni tayi cikin jin dadi
"To ya za'ayi,ba yadda banyi dashi ya barmin diyata a kusa ba yace min can yafi"dariya tayi
" zan saba ai anni in sha Allahu"
"To Allah ya taimaka yayi jagora,Allah ya hadaki da mutanen zama na qwarai"
"Amin anni na gode Allah ya qara girma" yan mintuna suka qara akan layi wanda yawanci tana tambayar annin jikinta da yadda tayi da 'yan abubuwan da aysha ta dauke mata,tace wani haka ta lallaba tayi wani ta haqura,da yake ba komai takeson masu aiki suyi mata ba,daga qarshe sukayi sallama da annin,bayan ta dan ja hankalinta kan ta kula da mutuncinta,wanda kusan dai duk kaman tana taya khaliphanta ne kishinta.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tsaki taja bayan ta gama zazzage ragowar madarar data rage a kwalin ta wurgar da kwalin gefe tana masifa da mita a ranta,idan akace mata haka zatayi rayuwa da hamid koda mafarki tayi zata qaryata mafarkin,wannan tafiyar da zaiyi babu abinda bai bar mata ba,ya dan rage maqon nashi kadan wanda ada bai wani dameta sosai ba saboda tana da kudinta a accnt,duk abinda take buqata shi take tabawa ta siya abinta,to wancan satin da sukayi waya da daddy yayi mata fada kan ta rage kashe kudi,ya duba accnt nata yaga kudinta sun soma yin qasa sosai,har yana cewa zai sama mata business ta dinga yi,don baison almubazzaranci da rashin adani,ya kawo mata misali da aysha wanda hakan ya qona ranta sosai,ya gaya mata har yanzu babu abinda ta cira a accnt din daya bude musu,tunawa tayi da daya accnt din nata data bude tun tana gida,bayan ta tare ta bawa a hamid ajiyar atm din,kudin cikin accnt din duk kayan aysha ne da take karbewa wanda tasha alwashin sun daina hada komai iri daya take baiwa mommy ta saka a kayanta ta saida saita karbi kudin,ciki harda wannan sabuwar motar tata da daddy ya siya musu iri daya.
Murmushi ta saki tana ayyanawa a ranta yau ga ranar plan dinta nan,a nutse ta soya qwai guda biyu daya rage mata da sauran kayan cikin data baiwa mai gadi ya kaiwa matarsa ta dafa mata ta dumamashi,don mai aikinta tunda hamid yayi tafiya itama ta tafi,shi yace mata ta tafi tunda shima baya nan,amfanin zamanta idan yana nan tunda asma'un bata iya komai ba,tunda baya nan tayi tafiyarta ita asma'un tasan ya zatayi da kanta,ya gaya mata cewar zai cire kudin aikin kwanakin bazai bata ba,tana ji tana gani ta tafin,ba irin bacin ran da asma'un batayi ba,qarshe mummy ta kira ta yiwa qorafi tana kuka,baqinciki ya hana mummyn magana,itakam har ta soma gajiya da jin matsaloli,ba ranarvAllah da zata fito ta fadi bata ji matsala daga asma'u ba sai dai daikun ranaku,wai dama haka auren masu kudin yake ne ko kuwa?,a'ah ta baiwa kanta amsa,koda wasa aysha bata taba kiranta tayi koda tarin da zai nuna cewa akwai wani abu dake faruwa ba tare da ita mara kyau,hakanan ita karan kanta shaida ce cewa bata taba wani kuka da daddy ba,hakanan mummy ke turo mata lantana ta wuni,itama daga bisani data gaji da wahala da ayyukan asma'un da basa qarewa ta tsiri ciwon qarya,dole aka sarara mata.
A nutse ta gama cin abincinta tana jin nishadi zata ciro kudinta ta kashe sabgar gabanta,don dama tun wancan satin ta rasa ya zatayi,za'ayi bikin daya daga cikin qawayensu,kuma kowacce idan bikinta ya tashi gudun mawa ake bata ta qasaita,samanta ta koma ta fesa wanka bayan ta shirya ta soma duba dakinta don dakin hamid din bai barinsa a bude,ko kasuwa zai fita saiya garqame abinsa ga tagi da muqullinsa bare wannan tafiya ta satittika,cikin sa'a kuwa ta gano atm din,ba bata lokaci ko jiran neman izini ta saka mayafinta ta fice daga gidan.
Sau uku tana tada motar taqi tashi,saidaga bisani ta lura ashe mai ne babu,haka ta sauka ta bada dari biyar aka siyo mata a bakin titi wajen 'yan bututu ta zuba ta tashi motar ta fice.
Ta samu layi sosai a ATM din,babu yadda ta iya haka tayita jira saboda taga mafadata aka hada a wajen har layi yazo kanta,saidai ga mamakinta sai ake cemata babu kudi a accnt dinta
"A'ah!" Ta fadi cike da madaukakin mamaki,ita tasan kudin ciki ya kusa dubu dari takwas da wani abu,sake maidawa tayi aka sake gaya mata hakan,take gumi ya soma yanko mata
"Hajiya kiyi da jiki da Allah,muna da yawa fa" cewar wani matashi dan ci da zuci dake bayanta
"Ba kudi ba a accnt din nata amma tazo ta wani faka mota tana yiwa mutane qarya tazo cirar kudi" inji wanda yafi kusa da ita ya fadi sanda ta fice daga layin da katin a hannunta,waiwayowa tayi da niyyar sille mishi,saboda tana ganin a girmanta ta girmi ayi mata hakan,saidai yadda idanu sukayi mata yawa yasa tayi hanzarin yin gaba ta fada motarta
Bata tsaya ba saidata isa gida,ta fada saman kujera ranta na quna,tana son tayi kuka tana cijewa,to yaushe wai har hamid ya fidda kudaden nan bata sani ba?,a fusace ta dauko wayarta ta nemi lambobinsa,bugu hudu aka dauka,saidai maimakon muryarsa muryar mace taji,a zabure ta daga wayar tana dubanta sai taga an yanke kiran,sake kiranshi tayi harta katse ba'a daga ba,sai data sake bi sannan aka daga,wannan karon shine
"Wace yar iskar ce ta daga wayarka?"
"Au....shi kika kirani kiji uwata?" Tunani ne ya fado mata,idan ta biyeshi suyita ne zatayi biyu babu,gwara ta fara sanin ina kudadenta suke tukunna
"Atm dina na wajenka,na dauka yau zanyi amfani da shi amma babu komai cikin accnt din"
"Anyi amfani dasu" ya bata amsa kai tsaye
"Kaman yaya hamid?,me kake nufi?" Ta tambayeshi tana gimtse fuska tamkar yana wajen
"Abinda nake nufi nace miki nayi amfani da su"
"Kudin nawa hamid?,wannan wanne irin abu ne daga baka ajiya zaka dauki haqqina kaci?"
"Dakata da Allah malama.." Ya katseta ba tare data gama fadin abinda zata fada din ba
"Gori zakimin kome?,karki gayan maganar banzan,nawa ni na kashe miki a rayuwa,nawa kike cimin yanzu?,to na cinye saiki qwata idan kina da qarfi" yana kaiwa nan ya datse kiran,kuka kawai ta saki saboda tsabar baqinciki da takaici,nan saman kujera ta zube duniya nayi mata qunci,wannan wace iriyar rayuwa ce,me ta yiwa hamid yake saka mata da wannan abubuwa?,haka ta dinga qwalla tana tambayar kanta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
36
Cikin sati uku kacal ta soma gane kan abubuwa na cikin makarantar,yanayin rayuwar da banbancin muhalli,yanayin jama'a kala kala,banbancin halaye dabi'u jinsi da kuma yare.