Sashe 15
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana fitowa a kitchen din anty safiyya ta shigo,inna laraba dauke da yaronta al_amin,ba laifi duk cikin yaran mummy sa'adatu ta fisu kirki,tana da dadin mu'amala da son jama'a,tana da fadin gsky saidai tana da fada idan akai ba dai dai ba,cikin fara'a aysha ta qarasa ta karbe al'amin daga hannu inna,ta dosana kan hannun daya daga cikin kujerun falon ta zauna tanawa al'amin wasa ta basu dama su gama gaisawa da mummy sa'ada dake baje a falon cikin takardu tana lissafe lissafen business dinta
"Aysha indo 'yammata....,ba'a ganinku sai anzo gidanku ko?" Cewar anty safiyya tana duban aysha cikin murmushi,itama murmushi tayi ta soma gaidata ba tare data amsata ba,tana cikin tambayarta sauran yaranta asma'u ta sauko daga sama,tayi kwalliya sosai cikin wani irin yadi wanda cikin tsarabar daddy ce,tayi masifar kyau,don dama itadin ba baya bace wajen kwalliya
"Mara mutunci" anty safiyya ta fadi tana gasa mata harara,narke fuska asma'un tayi tana cewa
"Mummy ki mata magana Allah,kinga daga zuwanta ko?"
"Hala wancan me shegen jin kanne yazo" ta sake fadi tana jifanta da harara
"Allah mummy kiyi mata magana.....duk yadda yake ganin mutuncinki shine zaki gaya masa haka?"ta fada cikin bacin rai shimfide saman fuskarta,miqewa aysha tayi ta miqa mata al'amin daya soma neman nono ta soma barin wajen sanda anty safiyya ke cewa
" to basai ki rama masa ba....tunda na zagi qanin mummy"
"Ya isa haka safiyya...ke kullum qorafinki kan hamid ne....kinsan kuma indai ita tana wajen baida aibu" fuuuu asma'un ta wuce ranta naci gaba da baci,babban takaicinta ma yadda anty safiyyan tayi mata a gaban ayshan,yarinyar da taqi jini,ta kuma qi jinin ta rainata ko a disgata agabanta.
Bayan komawarta daki wanka ta sauya ta soma shiryawa,madaidaiciyar kwalliya tayi,tayi kyau cikin laffayar data nade jikinta marron mai adon baqi,tana cikin fesa turare aka turo qofan,asma'u ce ta dubeta
"Ki tambayi lantana kayan da na saka a hada min ki dauko ki kawo min,muna gefan garden"
"To" kawai aysha tace ba tare data dubeta ba,saboda babu abinda ta tsana a rayuwarta irin hamid din yazo asma'u tace taje ta kai musu wani abu,batasan me yasa takeson mata hakan ba,ko da yake hakan baya rasa nasaba da yadda ko yaushe bata da burin daya wuce taga ta qasqantar da ayshan ta kuma nuna cewa ita ba kowa bace a wajenta,hakanan ita din ba jininta bace iqirarinta kenan koda yaushe.
Harta tura qofar dakin sai kuma ta sake dawowa tace
"Ke" tana dubanta,fararen idanunta kawai ta daga ta dubeta
"in zaki zo ki nemi hijabi ki saka,karki zomin a haka" tana gama fadi tayi gaba,hakanan taga ayshan tayi mata kyau,yadda marron din laffayar ta zauna saman fatar farar bufalatanar mace hakan ya sata qyashin ganinta a haka.
Sai data gama komai ta dauko jakarta ta fito baki daya sannan ta qarasa kitchen ta amshi kyakkyawan farantin da aka cika da kayan motsa baki ta nufi inda ta gaya matan.
Suna zaune daf da juna kan fararen kujerun da aka aje a wajen saboda zama da shan iska,isowarta wajen baisa sun gyara zamansu ba,idanun hamid jifa jifa nakan asma'un rabi na kan wayarshi,yayin da asma'un ta tattara dukka nutsuwarta da idanunta a kansa,sallama tayi ta dire sannan tace
"Ina yini" kai ya daga ya dubeta sannan ya maida kan wayar kafin ya amsa,juyawa tayi tana qoqarin wucewa
"Sai yanzu kika ga damar kawo wa?..." Ta fadi da saigar tambaya,tsaiwa kawai tayi ba tare data amsa kota ce wani abu ba,tsaki ta saki sannan tace
"Me kika tsaya kuma yi....aisaiki wuce ko malama" nan bata tanka ta ba ta juya tabar wajen,halayen asma'un ba baqo bane wajenta,koma waye tana iya masa haka idan taso,abu daya ta sani kome mutanen gidan suke mata suna da qima a idanunta,na farko koba komai sun riqeta suna zaune da ita,ta samu ingantuwar rayuwarta wadda abaya bata zaceta ba bakuma ta tsammaci samunta ba,na biyu kuma girma da qimar daddy ya shafe komai,ya danne duk wani abu da za'a mata,karamcinsa a gunta ba abune mai yiwuwa a manta da shi ba.
Ciki ta koma kawai tayiwa mommy sallama ta amsa mata,tana shirin juyawa zata fita a falon sukayi karo da ahmad dan gidan hajiya laraba,murmushi ya sakar mata itama saita maida masa tana matsawa gefe
"Ina zuwa haka da wannan yammacin?"
"Ina yini" ta zabi gaidashi maimakon amsa mishi tambayarsa
"Mu qarasa ciki saimu gaisa ko?....ko zan bata miki lokaci?" Ba haka taso ba,amma sai ta kada kanta kawai tana juyawa zuwa cikin.
Da fara'a mommy ta tarbeshi,aysha na gefe ta gaidashi sannan ta miqe
"Shiga ciki ki samo masa wani abun" cewar mummy,duk da cewa ko cikin kitchen din akwai masu aiki dake aikin abincin dare.
Miqewa yayi ya soma yiwa mummy sallama sanda aysha ta sake ficewa da niyyar tafiya
"Saurin me kike haka ina zuwa?" Tajishi daga bayanta yana fadi,ahmad ne,murmusawa kadan tayi tana noqewa baya kadan saboda qarasowa da yayi yana niyyar jerawa da ita
"Zani dubiyar wata qawata ne" ta amsa masa
"Ohk...muje na saukeki mana" kai ta kada
"A'ah...na gode....zan qarasa na hau napep"
"Amma ina duka drivers din gidan?,bansan gidan nan ana hawa abun haya ba..."
"Wataqila basa nan"ta fada cikin zaquwar ya tsaya daga nan,don sun kusa isa wajen aje motoci,ga asma'u data hango daga nesa idanunta na kansu
"Fine....tunda wataqila basa nan muje ni na saukeki"
"Allah ka barshi"
"Bakison na samu ladar gaida mara lafiya kenan?"
"A'ah ai....."
"Indai ba haka bane muje na kaiki" ya katseta,batasan me kuma zata sake ce masa ba,hakan ya sanya tilas ta bishi wajen motarshi.
Tana gefen sit din driver amma jinta take a matuqar takure ,jinta take kamar wadda ta aikata babban zunubi,kanta na qasa ta jiyoshi yana cewa
"Malama aysha....ya makaranta ya kuma samari?" Banbarakwai ta ji maganar,itakam tsahon rayuwarta ba zata iya tuna wani qwaqwaqwaran saurayi data taba yi ba,tun tana qauye zuwa yanzu,dama makarantar yace dai,kusan yanzu bata da wani abu da ya wuce makarantar a wajenta
"Ya kika yi shuru?" Ya sake tambayarta yana kallonta kafin ya dauke kai
"Makaranta alhmdlh" ta fada tana sauke boyayyar ajiyar zuciya
"Ma sha Allah,samarin fa?" Ya fada yana murmushi
"Hmmmm" kawai tace
"Hmm...kardai kice min babu?" Ya fada cikin sigar zolaya,gaba daya a takure take,sam batason maganar,jinta take kaman ta girmi kanta,bata ma da muhalli ko gurbi sam a rayuwarta ta yanzu,buri gareta na karatu mai zurfi,wanda zai zameta qaqqarfar garkuwa da zata tare duk wani abu mai cutarwa daka iya ci gaba da kawowa rayuwarta farmaki
"Idan har da gaske ne babun?...me zai hana ni a bani dama na shiga layi kuma mutum na farko ko?"shiru tayi tana jin zuciyarta na bugawa,kaman yaya me yake nufi?
"Uhmmm aysha?,kinyi shiru?,ko na barki kiyi nazari?"
"Eh" ta fadi da sauri,saboda shi daya ne mafitar a yanzu don bata da amsar bashi
"Ayi tunani mai kyau" ya fada yana karya kwanar da zasu shiga bayan ta masa nuni da yatsa.
Qofar gidan ya tsaida motarsa tana yunqurin fita ta masa godiya
"Ki daina saurin godiya haka,saboda zan dawo daukarki" kai ta girgiza
"Na yafe wallahi...bansan ma lokacin da zan koma gida ba karna wahal da kai"
"Na gane dai bakison na dawo....fine...samin phone number dinki" ya fada yana miqa mata wayarshi,da ka ta saka masa number sannan ta miqa masa yayi serving,sai data shige cikin gidan sannan yaja motarsa yabar wajen.
Tana shiga aliya tayi tsalle ta riqeta
"Ke...waye ya kawoki?" Murmushi ta saki mai sanyi cikin siririyar muryarta tace
"Wannan itace tarbar da za'amin dama?"
"Yi haquri sashen...wallahi dadi ne ya sakani fadin haka....yau naga abinda ban taba gani ba"
"Rakani na soma gaida mama tukunna"
"Mama bata nan,amma kafin ki tafi zata dawo" ta fadi tana jan hannunta zuwa kan kujerun falon.
Sai data cikawa aysha gabanta da kayan ciye ciye kala kala harta rasa wanne zata ci?,bata barta ba sai data ci tasha sannan suka shiga hira,yawanci aliya ke baiwa ayshan labarai kala kala,ta kuma kwaso mata hotuna ta kalla har ta gaji,daga bisani ta sake tada mata zancan,bata boye mata komai ba don aliya qawa ce ta gari
"Aysha....ki bashi dama ina ganin..bakisan me Allah zaiyi ba,ki manta da da rayuwarki ta baya...ki manta dake wacece ki ki amshi sabuwar rayuwarki" zame hannunta tayi daga na aliya qwalla na cika idanunta
"Ta yaya Aliya zan manta wace ni?,kin manta har yanzu akwai tabo cikin rayuwata,Aliya....mahaifiyata...ta yaya zanyi aure?,ta yaya zan sanarwa da wanda zan aura bahagon labarin dake wanzuwa tsakanina da mahaifiyata...ta yaya zan fahimtar da shi...da wanne ido zan kalleshi na sanar masa?koda na mance komai komai ya wuce banda wannan aliya" ta qarasa tana girgiza kai qwalla na bin kuncinta,can qasan zuciyarta tana jin suya,hannu aliya ta saka tana share mata hawayen fuskarta
"Kinzo gidanmu maimakon ki samu farinciki saiki qare da kuka?,banason haka sashin" murmushi ta saki wanda qasan sa ciwo ne da radadi
"Kinsan me?.....bari na kira ummi kiji ki sake tabbatarwa da maganata na kan hanya" ta fadi tana zaro wayarta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku tana mata gargadin kiranta amma bata fasa yunqurin kiran nata ba.
Dab da zata tsinke aka daga,sallamar ummin ta bayyana cikin muryarta,shuru ayshan tayi ta kasa cewa komai har sai data ce
"Wake magana ne?"
"Nic....ce...aysha ce"
"Wace ayshan?" Ta tambaya a dan gintse saboda hasashen da zuciyarta ta mata
"Aysha indo"
"Bakiji me na gaya miki ba ko?.....ke wacce iriyar yarinya ce mara zuciya?....koda yake ba mamaki jininsu sama'ila yake yawo a jininki,gargadina dake na qarshe karki sake nemana na gaya miki" daga haka ta yanke wayar,a matuqar sanyayar jiki aysha ta sauke wayar daga kunjeta,murmushi mai ciwo na tashi saman fuskarta
"Kin ji kuma kin gani ko aliya?" Ta fada a rarrabe muryarta na rawa,saman kafadarta aliya ta dora ayshan sai kuwa ta fashe da kukan data jima tana so tayi bai fita ba,sai qunci da takurar zuci da take fama da shi,babu wanda zata zauna gabanshi tayi kuka har haka,idan ma akwai aminiyarta ce qwaya daya da tayi mata nisa tana nata muhallin a qauyensu.
"Aysha indo 'yammata....,ba'a ganinku sai anzo gidanku ko?" Cewar anty safiyya tana duban aysha cikin murmushi,itama murmushi tayi ta soma gaidata ba tare data amsata ba,tana cikin tambayarta sauran yaranta asma'u ta sauko daga sama,tayi kwalliya sosai cikin wani irin yadi wanda cikin tsarabar daddy ce,tayi masifar kyau,don dama itadin ba baya bace wajen kwalliya
"Mara mutunci" anty safiyya ta fadi tana gasa mata harara,narke fuska asma'un tayi tana cewa
"Mummy ki mata magana Allah,kinga daga zuwanta ko?"
"Hala wancan me shegen jin kanne yazo" ta sake fadi tana jifanta da harara
"Allah mummy kiyi mata magana.....duk yadda yake ganin mutuncinki shine zaki gaya masa haka?"ta fada cikin bacin rai shimfide saman fuskarta,miqewa aysha tayi ta miqa mata al'amin daya soma neman nono ta soma barin wajen sanda anty safiyya ke cewa
" to basai ki rama masa ba....tunda na zagi qanin mummy"
"Ya isa haka safiyya...ke kullum qorafinki kan hamid ne....kinsan kuma indai ita tana wajen baida aibu" fuuuu asma'un ta wuce ranta naci gaba da baci,babban takaicinta ma yadda anty safiyyan tayi mata a gaban ayshan,yarinyar da taqi jini,ta kuma qi jinin ta rainata ko a disgata agabanta.
Bayan komawarta daki wanka ta sauya ta soma shiryawa,madaidaiciyar kwalliya tayi,tayi kyau cikin laffayar data nade jikinta marron mai adon baqi,tana cikin fesa turare aka turo qofan,asma'u ce ta dubeta
"Ki tambayi lantana kayan da na saka a hada min ki dauko ki kawo min,muna gefan garden"
"To" kawai aysha tace ba tare data dubeta ba,saboda babu abinda ta tsana a rayuwarta irin hamid din yazo asma'u tace taje ta kai musu wani abu,batasan me yasa takeson mata hakan ba,ko da yake hakan baya rasa nasaba da yadda ko yaushe bata da burin daya wuce taga ta qasqantar da ayshan ta kuma nuna cewa ita ba kowa bace a wajenta,hakanan ita din ba jininta bace iqirarinta kenan koda yaushe.
Harta tura qofar dakin sai kuma ta sake dawowa tace
"Ke" tana dubanta,fararen idanunta kawai ta daga ta dubeta
"in zaki zo ki nemi hijabi ki saka,karki zomin a haka" tana gama fadi tayi gaba,hakanan taga ayshan tayi mata kyau,yadda marron din laffayar ta zauna saman fatar farar bufalatanar mace hakan ya sata qyashin ganinta a haka.
Sai data gama komai ta dauko jakarta ta fito baki daya sannan ta qarasa kitchen ta amshi kyakkyawan farantin da aka cika da kayan motsa baki ta nufi inda ta gaya matan.
Suna zaune daf da juna kan fararen kujerun da aka aje a wajen saboda zama da shan iska,isowarta wajen baisa sun gyara zamansu ba,idanun hamid jifa jifa nakan asma'un rabi na kan wayarshi,yayin da asma'un ta tattara dukka nutsuwarta da idanunta a kansa,sallama tayi ta dire sannan tace
"Ina yini" kai ya daga ya dubeta sannan ya maida kan wayar kafin ya amsa,juyawa tayi tana qoqarin wucewa
"Sai yanzu kika ga damar kawo wa?..." Ta fadi da saigar tambaya,tsaiwa kawai tayi ba tare data amsa kota ce wani abu ba,tsaki ta saki sannan tace
"Me kika tsaya kuma yi....aisaiki wuce ko malama" nan bata tanka ta ba ta juya tabar wajen,halayen asma'un ba baqo bane wajenta,koma waye tana iya masa haka idan taso,abu daya ta sani kome mutanen gidan suke mata suna da qima a idanunta,na farko koba komai sun riqeta suna zaune da ita,ta samu ingantuwar rayuwarta wadda abaya bata zaceta ba bakuma ta tsammaci samunta ba,na biyu kuma girma da qimar daddy ya shafe komai,ya danne duk wani abu da za'a mata,karamcinsa a gunta ba abune mai yiwuwa a manta da shi ba.
Ciki ta koma kawai tayiwa mommy sallama ta amsa mata,tana shirin juyawa zata fita a falon sukayi karo da ahmad dan gidan hajiya laraba,murmushi ya sakar mata itama saita maida masa tana matsawa gefe
"Ina zuwa haka da wannan yammacin?"
"Ina yini" ta zabi gaidashi maimakon amsa mishi tambayarsa
"Mu qarasa ciki saimu gaisa ko?....ko zan bata miki lokaci?" Ba haka taso ba,amma sai ta kada kanta kawai tana juyawa zuwa cikin.
Da fara'a mommy ta tarbeshi,aysha na gefe ta gaidashi sannan ta miqe
"Shiga ciki ki samo masa wani abun" cewar mummy,duk da cewa ko cikin kitchen din akwai masu aiki dake aikin abincin dare.
Miqewa yayi ya soma yiwa mummy sallama sanda aysha ta sake ficewa da niyyar tafiya
"Saurin me kike haka ina zuwa?" Tajishi daga bayanta yana fadi,ahmad ne,murmusawa kadan tayi tana noqewa baya kadan saboda qarasowa da yayi yana niyyar jerawa da ita
"Zani dubiyar wata qawata ne" ta amsa masa
"Ohk...muje na saukeki mana" kai ta kada
"A'ah...na gode....zan qarasa na hau napep"
"Amma ina duka drivers din gidan?,bansan gidan nan ana hawa abun haya ba..."
"Wataqila basa nan"ta fada cikin zaquwar ya tsaya daga nan,don sun kusa isa wajen aje motoci,ga asma'u data hango daga nesa idanunta na kansu
"Fine....tunda wataqila basa nan muje ni na saukeki"
"Allah ka barshi"
"Bakison na samu ladar gaida mara lafiya kenan?"
"A'ah ai....."
"Indai ba haka bane muje na kaiki" ya katseta,batasan me kuma zata sake ce masa ba,hakan ya sanya tilas ta bishi wajen motarshi.
Tana gefen sit din driver amma jinta take a matuqar takure ,jinta take kamar wadda ta aikata babban zunubi,kanta na qasa ta jiyoshi yana cewa
"Malama aysha....ya makaranta ya kuma samari?" Banbarakwai ta ji maganar,itakam tsahon rayuwarta ba zata iya tuna wani qwaqwaqwaran saurayi data taba yi ba,tun tana qauye zuwa yanzu,dama makarantar yace dai,kusan yanzu bata da wani abu da ya wuce makarantar a wajenta
"Ya kika yi shuru?" Ya sake tambayarta yana kallonta kafin ya dauke kai
"Makaranta alhmdlh" ta fada tana sauke boyayyar ajiyar zuciya
"Ma sha Allah,samarin fa?" Ya fada yana murmushi
"Hmmmm" kawai tace
"Hmm...kardai kice min babu?" Ya fada cikin sigar zolaya,gaba daya a takure take,sam batason maganar,jinta take kaman ta girmi kanta,bata ma da muhalli ko gurbi sam a rayuwarta ta yanzu,buri gareta na karatu mai zurfi,wanda zai zameta qaqqarfar garkuwa da zata tare duk wani abu mai cutarwa daka iya ci gaba da kawowa rayuwarta farmaki
"Idan har da gaske ne babun?...me zai hana ni a bani dama na shiga layi kuma mutum na farko ko?"shiru tayi tana jin zuciyarta na bugawa,kaman yaya me yake nufi?
"Uhmmm aysha?,kinyi shiru?,ko na barki kiyi nazari?"
"Eh" ta fadi da sauri,saboda shi daya ne mafitar a yanzu don bata da amsar bashi
"Ayi tunani mai kyau" ya fada yana karya kwanar da zasu shiga bayan ta masa nuni da yatsa.
Qofar gidan ya tsaida motarsa tana yunqurin fita ta masa godiya
"Ki daina saurin godiya haka,saboda zan dawo daukarki" kai ta girgiza
"Na yafe wallahi...bansan ma lokacin da zan koma gida ba karna wahal da kai"
"Na gane dai bakison na dawo....fine...samin phone number dinki" ya fada yana miqa mata wayarshi,da ka ta saka masa number sannan ta miqa masa yayi serving,sai data shige cikin gidan sannan yaja motarsa yabar wajen.
Tana shiga aliya tayi tsalle ta riqeta
"Ke...waye ya kawoki?" Murmushi ta saki mai sanyi cikin siririyar muryarta tace
"Wannan itace tarbar da za'amin dama?"
"Yi haquri sashen...wallahi dadi ne ya sakani fadin haka....yau naga abinda ban taba gani ba"
"Rakani na soma gaida mama tukunna"
"Mama bata nan,amma kafin ki tafi zata dawo" ta fadi tana jan hannunta zuwa kan kujerun falon.
Sai data cikawa aysha gabanta da kayan ciye ciye kala kala harta rasa wanne zata ci?,bata barta ba sai data ci tasha sannan suka shiga hira,yawanci aliya ke baiwa ayshan labarai kala kala,ta kuma kwaso mata hotuna ta kalla har ta gaji,daga bisani ta sake tada mata zancan,bata boye mata komai ba don aliya qawa ce ta gari
"Aysha....ki bashi dama ina ganin..bakisan me Allah zaiyi ba,ki manta da da rayuwarki ta baya...ki manta dake wacece ki ki amshi sabuwar rayuwarki" zame hannunta tayi daga na aliya qwalla na cika idanunta
"Ta yaya Aliya zan manta wace ni?,kin manta har yanzu akwai tabo cikin rayuwata,Aliya....mahaifiyata...ta yaya zanyi aure?,ta yaya zan sanarwa da wanda zan aura bahagon labarin dake wanzuwa tsakanina da mahaifiyata...ta yaya zan fahimtar da shi...da wanne ido zan kalleshi na sanar masa?koda na mance komai komai ya wuce banda wannan aliya" ta qarasa tana girgiza kai qwalla na bin kuncinta,can qasan zuciyarta tana jin suya,hannu aliya ta saka tana share mata hawayen fuskarta
"Kinzo gidanmu maimakon ki samu farinciki saiki qare da kuka?,banason haka sashin" murmushi ta saki wanda qasan sa ciwo ne da radadi
"Kinsan me?.....bari na kira ummi kiji ki sake tabbatarwa da maganata na kan hanya" ta fadi tana zaro wayarta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku tana mata gargadin kiranta amma bata fasa yunqurin kiran nata ba.
Dab da zata tsinke aka daga,sallamar ummin ta bayyana cikin muryarta,shuru ayshan tayi ta kasa cewa komai har sai data ce
"Wake magana ne?"
"Nic....ce...aysha ce"
"Wace ayshan?" Ta tambaya a dan gintse saboda hasashen da zuciyarta ta mata
"Aysha indo"
"Bakiji me na gaya miki ba ko?.....ke wacce iriyar yarinya ce mara zuciya?....koda yake ba mamaki jininsu sama'ila yake yawo a jininki,gargadina dake na qarshe karki sake nemana na gaya miki" daga haka ta yanke wayar,a matuqar sanyayar jiki aysha ta sauke wayar daga kunjeta,murmushi mai ciwo na tashi saman fuskarta
"Kin ji kuma kin gani ko aliya?" Ta fada a rarrabe muryarta na rawa,saman kafadarta aliya ta dora ayshan sai kuwa ta fashe da kukan data jima tana so tayi bai fita ba,sai qunci da takurar zuci da take fama da shi,babu wanda zata zauna gabanshi tayi kuka har haka,idan ma akwai aminiyarta ce qwaya daya da tayi mata nisa tana nata muhallin a qauyensu.