Sashe 70
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Parlour din ya koma ya zauna saman daya daga cikin kujerun falon yana dafe da goshinsa da hannu daya ya zaro wayarshi ya lalubi lambar anni,bugu daya ta daga,sai yayi qoqarin saisaita temper dinsa
"Anni,wace take amfani da bedroom dina?"
"Bedroom dinka?,wace banda matarka,aysha ce"
"Aysha kuma?" Ya tambaya cikin mamaki
"Eh ita,wani abu ne?"
"A'ah,ta tsorata ne kawai ta shiga toilet tayi zaton wani ne" yayi saurin fada don karta dago wani abu
"Aifa aysha ba baya ba wajen tsoro,saika gaya mata wane ai" daga haka ta katse wayar,jifa wayar yayi gefanshi sannan ya miqe qafafunshi ya soma zare takalmin qafarsa da socka din duka gaba daya,ya rage daya daga cikin three in one suit din dake jikinsa ya sassauta tie dinsa sannan ya sake komawa dakin,tsai yayi yana qarewa dakin kallo,komai a tsaftace yake,sai towel bressier da pant dake kan gadon,sai kayan gyaran gashi dake saman madubi da cumb din data watsar waje guda saboda tsoronta,dauke kanshi yayi ya shigo ciki sosai ya doshi toilet din.
Daga can taji 'yar qara alamun an sake bude qofar bedroom din,wani tsoron ya sake kamata,sautin kukanta ya sake qaruwa sanda taji ana taba qofar bandakin,yana iya jiyo sautinta kadan kadan,haushi ya kamashi,wanne irin tsoro ne da ita haka,knocking ya fara yi saidai maimakon ta bude sake firgicewa tayi,gabanta yaci gaba da bugun uku uku,ta duba duk bandakin ba wajen tsira,kuma ta tabbata ko ihu tayi ba wanda zai jiyota cikin gidan,ganin ba alamun zata bude sai kukan banza da takeyi ba tare da yasan me takewa kukan ba ya sanyashi bude bakinsa,cikin muryarshin nan yace
"Bude mana" saboda tsoro sam bata iya tantance muryar waye ba,sai kawai zuciyarta ta bata muryar aljanu ce,cikin sautin kuka tace
"Wallahi bazan bude ba"
"Kwana zakiyi a ciki?"
"Nidai kuyi haquri don Allah"
"Mu suwa?" Ya tambayeta cikin qosawa,bata bashi amsa ba sai dif da tayi,ganin tana neman bata mishi lokaci yasa ya koma inda ya aje kayan hannunshi ranshi fal takaici,ya lalubi muqullansa daya amsa a hannun anni ya koma yana gwada na toilet din,jin ana alamun budewa ya sake sawa ta tsure,saikawai ta qarasa shigewa cikin bathtube din ta takure waje daya tana dana sanin zama abangaren ita kadai,dama tun dazun take jin motsi,dazu kuma musa'ab ya gama bata labarin ya taba gamo tsohon gidansu,tana ta dariya da tsokanarshi duk labarin ya dan bata tsoro kadan ashe da gaske yake
Sai daya gwada muqullai kusan uku abinda ya sake gajiyar dashi sannan ya dace dana bandakin,a hankali ya tura qofar ya shiga,can ya hangota ta takure gu daya,gashin kanta da bata samu damar daurewa ba ya bazu ko ina har fuskarta,daga kai tayi cikin tsoro ta dubeshi,sai a sannan ainihin siffarshi ta bayyanar mata,khalipha ne sosai tsaye cikin bandakin,sanye cikin baqaqen suit,saidai a yanzu ya cire sun glasses din dake fuskarshi,ya sake haske da kyau,sumar kanshi data fuskarshi luf da ita tana fidda wani sheqin baqi,ya sake murjewa hakanan idanunshi sun sake kyau,daga tsoro sai yanayin ta ya sauya zuwa kunya da fargaba,ta tafka babban abun kunya,bugu da qari tuna abinda ke daure a jikinta kawai ya sake sawa hankalinta ya tashi,kamar ta bace ya daina gannta haka taji,sai kawai ta maida kanta taci gaba da dunqulewa waje guda gana pretending din firgitar dazu ce bata saketa ba
"Saiki tashi ki koma ciki ki bani waje zanyi wanka" ya fada yana dubanta,duk da qoqarin kauda idanunshi da yakeyi amma hakan ya gagara,jin idanunsa take yake ko ina akanta,batajin zata iya motsawa ta wuce haka ya gabanshi
"Ki tashi matsoraciya kawai ko har yanzu baki gane wane ba?" Ya tambayeta yana harde hannunsa a qirji,shuru tayi don bata da amsar bashi
"Ko ba zaki tashi ba sai nazo na daukeki da kaina?" Jin haka ya sanyata zumbur ta miqe,saidai da qyar take iya daga qafafunta ta fito daga cikin bathtube din ta raba ta gabanshi zata fice daga bandakin,caraf yayi ya riqo hannunta yana sani,a firgice ta dago kai suka hada idanu,saita soma neman wajen buya,wanda abin dariyar jikinsa takeson shigewa ko zai daina kallonta,ba shiri ya saketa yana dariya cikin ranshi,bai fasa kallonta ba har sai data fita din sannan ya koma ya rufe bandakin da muqulli ya dawo ciki ya tara ruwan wanka.
Hawaye ne ya sake qwace mata takaici na cinta na ganinta haka da yayi,gashinan shi yanzu ya saka muqulli ya kulle kanshi zaiyi wanka amma ita asirinta abayyane,qwafa tayi ita kadai tana zumburo baki.
Haka ta shirya tana qananun hawaye a gurguje don kada ya sake fitowa ya taddata a haka,duk da haka bata fasa yin kyau ba,doguwar rigar buba ce ta atamfa shadda baqa mai matuqar kyau da tsada,an mata zanen jajayen flowers manya a jiki,bata nemi dan kwali ba saita yane kanta da madaidaicin jan mayafi bayan ta hade gashinta ya bada jela daya data sauka har bayanta.
Har taje zata fita sai kuma ta kasa,bai kamata ba,ba wani magana da sukai tsakaninsu koda ta sannu da zuwa ce,saita koma kan kujerar falon ta zauna tana murza tafin hannunta a hankali tana tuna yadda abun ya faru,dama tun dazu a tsorace take da labarin mus'ab,shi ya sake tunzurata ta sake tsorata.
Idanunsa lumshe suke ruwan na ratsa jikinsa,tabbas haka ne kowa yabar gida gida ya barshi,wani dadi yake ji gashi a gida,Allah Allah kawai yake ya koma wajen anni susha hira,a hankali ya tuna abinda ya faru dazu mintina kadan da suka wuce,murmushi ya saki abun yana son bashi dariya,bai taba sanin matsoraciya bace har haka bayan sanyin da yasan a baya tana da shi ba sai yau,kai ya kada kafin ya dauraye jikinsa ya fito.
Tunani kadan tayi sai ta miqe ta fice zuwa cikin gidan,ya kamata ace tayi masa wani abu da zaiji dadi,tunda bata jin gidan sun tanadar masa wani abun don ba alamun suna da masaniyar zuwanshi a yau,ta tabbata da anni zata sanar mata,haidar da mus'ab ne kawai a falon suna shigo da jakankuna,dariya mus'ab ya sa yana dan satar kallonta,har ta wuceshi ta share sai ta tuna abinda taji yana cewa anni dazu na suprise,sai ta dawo da baya tana dubansa
"Zan rama fa,kaci bashi ne,yaa haidar harda kai aka hada baki ko?" Ta fada tana duban haidar,murmushi yayi yana daga hannu sama
"Nikam babu ruwana bansan me akeyi ba,yace min ne kawai nazo na rakashi airphort" kai ta jinjina tana wa mus'ab sign na alwashi ta wuce kitchen.
Duka 'yan aikin ma ciki sun kacame da aiki
"A'ah duk girkin meye wannan?" Ta tambayi baba atika
"Mai gida yayi zuwan bazata kinga dole a tashi a shirya masa lafiyayyen abinci" hakanan taji cewa dutynta ne wannan,ita ya kamata tayi masa wannan karramawar,koba komai ta dan nuna dan wani yanki na godiya kan kyautatawarsa a gareta,duk da baikai ya kawo ba amma zata kwatanta
"Bari ku gani,wannan girkin naku ai lokaci zai dauka baku gama ba" cikin qanqamin lokaci ta hado duk abinda take buqata ta dora,ta koma gefe ta niqa abarba tayi mishi pineapple juice wanda kafin ta garma dan qwarya qwarayar girkinta ya dauki sanyi.
Mintina talatin ta gama ta shirya komai kan wani faffadan tray mai azabar kyau,ba wanda yawunshi bai tsinke ba a kitchen din(harda ni mai rubutun 😜).
Tana goge hannunta da zummar idan ta gama ta fita da abincin amal ta shigo,kana ganinta kasan bata jima da yin kwalliyar ba cikin dinkin lace
"Wai baba atika me kuke dafawa baqonmu,qamshi ya cika gidan amma shuru baku gabatar masa da komai ba?"
"Ai aikin uwar masu gida ne,gashinan da kanta ba saqo ba" baba atikar ta fada cikin murmushi wanda hakan yaja hankalin amal zuwa wajen aysha wadda take sake jera kwanukan,cikin yaqe take kallonta,nutsatsiyar kwalliyarta wadda girkin da tayi bai bata ta ba,yadda ta jera kayan abincin da qamshin da suke fiddawa,wani abu mai nauyi taji ya tokare qirjinta,sai ta kasa cewa komai ta juya ta fice cikin sanyin gwiwa.
"Anni,wace take amfani da bedroom dina?"
"Bedroom dinka?,wace banda matarka,aysha ce"
"Aysha kuma?" Ya tambaya cikin mamaki
"Eh ita,wani abu ne?"
"A'ah,ta tsorata ne kawai ta shiga toilet tayi zaton wani ne" yayi saurin fada don karta dago wani abu
"Aifa aysha ba baya ba wajen tsoro,saika gaya mata wane ai" daga haka ta katse wayar,jifa wayar yayi gefanshi sannan ya miqe qafafunshi ya soma zare takalmin qafarsa da socka din duka gaba daya,ya rage daya daga cikin three in one suit din dake jikinsa ya sassauta tie dinsa sannan ya sake komawa dakin,tsai yayi yana qarewa dakin kallo,komai a tsaftace yake,sai towel bressier da pant dake kan gadon,sai kayan gyaran gashi dake saman madubi da cumb din data watsar waje guda saboda tsoronta,dauke kanshi yayi ya shigo ciki sosai ya doshi toilet din.
Daga can taji 'yar qara alamun an sake bude qofar bedroom din,wani tsoron ya sake kamata,sautin kukanta ya sake qaruwa sanda taji ana taba qofar bandakin,yana iya jiyo sautinta kadan kadan,haushi ya kamashi,wanne irin tsoro ne da ita haka,knocking ya fara yi saidai maimakon ta bude sake firgicewa tayi,gabanta yaci gaba da bugun uku uku,ta duba duk bandakin ba wajen tsira,kuma ta tabbata ko ihu tayi ba wanda zai jiyota cikin gidan,ganin ba alamun zata bude sai kukan banza da takeyi ba tare da yasan me takewa kukan ba ya sanyashi bude bakinsa,cikin muryarshin nan yace
"Bude mana" saboda tsoro sam bata iya tantance muryar waye ba,sai kawai zuciyarta ta bata muryar aljanu ce,cikin sautin kuka tace
"Wallahi bazan bude ba"
"Kwana zakiyi a ciki?"
"Nidai kuyi haquri don Allah"
"Mu suwa?" Ya tambayeta cikin qosawa,bata bashi amsa ba sai dif da tayi,ganin tana neman bata mishi lokaci yasa ya koma inda ya aje kayan hannunshi ranshi fal takaici,ya lalubi muqullansa daya amsa a hannun anni ya koma yana gwada na toilet din,jin ana alamun budewa ya sake sawa ta tsure,saikawai ta qarasa shigewa cikin bathtube din ta takure waje daya tana dana sanin zama abangaren ita kadai,dama tun dazun take jin motsi,dazu kuma musa'ab ya gama bata labarin ya taba gamo tsohon gidansu,tana ta dariya da tsokanarshi duk labarin ya dan bata tsoro kadan ashe da gaske yake
Sai daya gwada muqullai kusan uku abinda ya sake gajiyar dashi sannan ya dace dana bandakin,a hankali ya tura qofar ya shiga,can ya hangota ta takure gu daya,gashin kanta da bata samu damar daurewa ba ya bazu ko ina har fuskarta,daga kai tayi cikin tsoro ta dubeshi,sai a sannan ainihin siffarshi ta bayyanar mata,khalipha ne sosai tsaye cikin bandakin,sanye cikin baqaqen suit,saidai a yanzu ya cire sun glasses din dake fuskarshi,ya sake haske da kyau,sumar kanshi data fuskarshi luf da ita tana fidda wani sheqin baqi,ya sake murjewa hakanan idanunshi sun sake kyau,daga tsoro sai yanayin ta ya sauya zuwa kunya da fargaba,ta tafka babban abun kunya,bugu da qari tuna abinda ke daure a jikinta kawai ya sake sawa hankalinta ya tashi,kamar ta bace ya daina gannta haka taji,sai kawai ta maida kanta taci gaba da dunqulewa waje guda gana pretending din firgitar dazu ce bata saketa ba
"Saiki tashi ki koma ciki ki bani waje zanyi wanka" ya fada yana dubanta,duk da qoqarin kauda idanunshi da yakeyi amma hakan ya gagara,jin idanunsa take yake ko ina akanta,batajin zata iya motsawa ta wuce haka ya gabanshi
"Ki tashi matsoraciya kawai ko har yanzu baki gane wane ba?" Ya tambayeta yana harde hannunsa a qirji,shuru tayi don bata da amsar bashi
"Ko ba zaki tashi ba sai nazo na daukeki da kaina?" Jin haka ya sanyata zumbur ta miqe,saidai da qyar take iya daga qafafunta ta fito daga cikin bathtube din ta raba ta gabanshi zata fice daga bandakin,caraf yayi ya riqo hannunta yana sani,a firgice ta dago kai suka hada idanu,saita soma neman wajen buya,wanda abin dariyar jikinsa takeson shigewa ko zai daina kallonta,ba shiri ya saketa yana dariya cikin ranshi,bai fasa kallonta ba har sai data fita din sannan ya koma ya rufe bandakin da muqulli ya dawo ciki ya tara ruwan wanka.
Hawaye ne ya sake qwace mata takaici na cinta na ganinta haka da yayi,gashinan shi yanzu ya saka muqulli ya kulle kanshi zaiyi wanka amma ita asirinta abayyane,qwafa tayi ita kadai tana zumburo baki.
Haka ta shirya tana qananun hawaye a gurguje don kada ya sake fitowa ya taddata a haka,duk da haka bata fasa yin kyau ba,doguwar rigar buba ce ta atamfa shadda baqa mai matuqar kyau da tsada,an mata zanen jajayen flowers manya a jiki,bata nemi dan kwali ba saita yane kanta da madaidaicin jan mayafi bayan ta hade gashinta ya bada jela daya data sauka har bayanta.
Har taje zata fita sai kuma ta kasa,bai kamata ba,ba wani magana da sukai tsakaninsu koda ta sannu da zuwa ce,saita koma kan kujerar falon ta zauna tana murza tafin hannunta a hankali tana tuna yadda abun ya faru,dama tun dazu a tsorace take da labarin mus'ab,shi ya sake tunzurata ta sake tsorata.
Idanunsa lumshe suke ruwan na ratsa jikinsa,tabbas haka ne kowa yabar gida gida ya barshi,wani dadi yake ji gashi a gida,Allah Allah kawai yake ya koma wajen anni susha hira,a hankali ya tuna abinda ya faru dazu mintina kadan da suka wuce,murmushi ya saki abun yana son bashi dariya,bai taba sanin matsoraciya bace har haka bayan sanyin da yasan a baya tana da shi ba sai yau,kai ya kada kafin ya dauraye jikinsa ya fito.
Tunani kadan tayi sai ta miqe ta fice zuwa cikin gidan,ya kamata ace tayi masa wani abu da zaiji dadi,tunda bata jin gidan sun tanadar masa wani abun don ba alamun suna da masaniyar zuwanshi a yau,ta tabbata da anni zata sanar mata,haidar da mus'ab ne kawai a falon suna shigo da jakankuna,dariya mus'ab ya sa yana dan satar kallonta,har ta wuceshi ta share sai ta tuna abinda taji yana cewa anni dazu na suprise,sai ta dawo da baya tana dubansa
"Zan rama fa,kaci bashi ne,yaa haidar harda kai aka hada baki ko?" Ta fada tana duban haidar,murmushi yayi yana daga hannu sama
"Nikam babu ruwana bansan me akeyi ba,yace min ne kawai nazo na rakashi airphort" kai ta jinjina tana wa mus'ab sign na alwashi ta wuce kitchen.
Duka 'yan aikin ma ciki sun kacame da aiki
"A'ah duk girkin meye wannan?" Ta tambayi baba atika
"Mai gida yayi zuwan bazata kinga dole a tashi a shirya masa lafiyayyen abinci" hakanan taji cewa dutynta ne wannan,ita ya kamata tayi masa wannan karramawar,koba komai ta dan nuna dan wani yanki na godiya kan kyautatawarsa a gareta,duk da baikai ya kawo ba amma zata kwatanta
"Bari ku gani,wannan girkin naku ai lokaci zai dauka baku gama ba" cikin qanqamin lokaci ta hado duk abinda take buqata ta dora,ta koma gefe ta niqa abarba tayi mishi pineapple juice wanda kafin ta garma dan qwarya qwarayar girkinta ya dauki sanyi.
Mintina talatin ta gama ta shirya komai kan wani faffadan tray mai azabar kyau,ba wanda yawunshi bai tsinke ba a kitchen din(harda ni mai rubutun 😜).
Tana goge hannunta da zummar idan ta gama ta fita da abincin amal ta shigo,kana ganinta kasan bata jima da yin kwalliyar ba cikin dinkin lace
"Wai baba atika me kuke dafawa baqonmu,qamshi ya cika gidan amma shuru baku gabatar masa da komai ba?"
"Ai aikin uwar masu gida ne,gashinan da kanta ba saqo ba" baba atikar ta fada cikin murmushi wanda hakan yaja hankalin amal zuwa wajen aysha wadda take sake jera kwanukan,cikin yaqe take kallonta,nutsatsiyar kwalliyarta wadda girkin da tayi bai bata ta ba,yadda ta jera kayan abincin da qamshin da suke fiddawa,wani abu mai nauyi taji ya tokare qirjinta,sai ta kasa cewa komai ta juya ta fice cikin sanyin gwiwa.