← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 114

Sashe 2

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata ankara ba taga lokaci ya ja,har qarfe tara saura na safiya,idanu ta zaro don tun jiyan da daddare anty asma'u ta ja mata kunne cewar qarfe tara zata fita,kuma driver ba tsayawa jiranta zaiyi ba,ruwanta ta shirya da wuri ruwanta karta shirya ta samu mai ajjiyeta makaranta"hakan ya sanya ta tattare komai a gurguje ta soma shiryawa saman qawataccen teburin cin abincin dake sashe na musamman dake cikin falon.

Plates da spoons suka rage suta dauko ta dawo da niyyar ajewa daga nan ta shiga ciki ta shirya itama,duk da cewa ita sai goma zata fita,amma dole ta shirya tabi asma'un koda qarfe bakwai asma'un zata fita,tsaye ta tadda ta shirya tsaf cikin wata doguwar rigar material,ta zuba makeup sosai,hannunta maqale da 'yar madaidaiciyar hand bag mai azabar kyau,kafadarta rataye da mayafinta wanda wanda haka qa'idar saka mayafinta yake,qwayar idanunta saye da tafkeken sun glasses wanda ya kusan cinye rabin fuskarta,table din take qarewa kallo har sanda aysha ta qaraso wajen tana dora plates din saman teburin gami da gaida asma'un.

Bata damu da amsa gaisuwar da take mata ba saima tambayar data jefo mata
"Waima baki shirya ba?" Ta fada cikin bacin rai tana zare glass din fuskarta kasancewarta mace wadda qanqanin abu sai ya bata mata rai ko ya tunzurata
"Yanzun zan shirya in sha Allahu" ta fada a tausashe,cikin hasala asma'un tace
"Kada ma ki shirya wannan ya rage naki,ni dama na soma gajiya da tafiya dake gaskiya,ya kamata daddy ya barni haka nan ya raba mana tafiya tunda babu dole.....ina cewa tun jiya na sanarmiki lokacin da zan fita,amma saboda tsabar raini da salon ki jawa mutum fada baki tashi kin gama komai a kan lokaci ba"
"Kai...kai me yake faruwa haka da sassafen nan kuma lafiya?" Cikin bacin rai asma'u ta juya tana kallon mahaifiyarta dake saukowa daga stairs,shirye cikin tsadajjen lace na alfarma,hannayenta da wuyanya duka sanye da jewels da banguls masu tsada
"Mommy nida yarinyar nan ne mana,wai ki duba fa jiya gabanki na gaya mata when zan fita shine wai har yanzu bata shirya ba"
"Garin yaya ke ayshatu?...." Jin tambayar tayi banbarakwai,tunda dukkaninsu sunsan me ya tsaidata,hidimar abincin safen asma'un ne,wanda dukkansu sun kwana da sanin cewa don ta itama a soke abincin safe,totally ma ba damuwarta bane abinci
"Ya kuma kika tsaya,jeki ki shirya,idan kuma har ta gama baki fito ba sai ki samu napep ya kaiki" ta fada itama tana jan daya daga cikin kujerun dining din da alama karyawa zatayi akwai muhimmiyar fita kenan.

Juyawa tayi a hankali ta doshi corridor din da dakunansu suke,sam batayi mamaki ba tunda ba yau bane farau,hajiya sa'adatu irin matan nan ne da basu cika ganin aibu ko laifin dansu ba,bugu da qari tana da attitude na idont care kan lamuran da ba nata ba,tayi ma rawar gani yau data tanka,idan da taso Allah ya kyauta kawai zata ce tayi zamanta ta hau hidimar gabanta ya tasu koma ya zasu qarke ohon mata,indai hakan bazai shafi shalelen tata ba ko kuma ita bazai kawo mata wani cikas ba.

Duk da cewa a gurguje ta shirya amma hakan bai sata ta samu nasarar tadda asma'un ba,saima hajiya sa'adatu data samu tana yunqurin bude murfin mota zasu fita ita da drivanta,kallo daya tayi mata tace
"Gashi har asma'un ta wuce tun dazun,saidai ki qarasa titi kibi ta haya" ta qarashe maganar tana shigewa motar tare da yunqurin rufewa
"Ba komai zan qarasa din mommy,a dawo lafiya"
"Allah yasa" ta masa sanda drivern ya fara jan motar suna niyyar ficewa daga gidan ba tare data damu da yadda ayshan zata kai kanta makarantar ba.

Tana nan tsaye har motar mommy ta fice sa'annan ta soma takawa a hankali cike da nutsuwar data zama tambarinta tabi bayan qurar motar ta fice daga gidan ta 'yar qaramar qofar dake maqale jikin get din.

Duk da yake akwai 'yar tazara kadan tsakanin gidan nasu da bakin titi amma sam bata ji tafiyar ba,hakan ya faru ne sakamakon yadda qwaqwalwa da zuciyarta baki daya sukayi zurfin tare da nisan kiwo wajen tunani,tunani qwaya daya da ko yaushe bata gajiya da shi,hakanan batasan randa babin tarihin rayuwarta zai rufe ba,hakan batasan meye qarshen nasa ba,yaya qarshen nasa zai kasance?,wata iriyar cukurkudaddiyar rayuwa da tayi take kuma kanyi ita ke mata kai kawo cikin qwaqwalwarta.

Sam ta sha'afa sai data tsaida mai napep sukayi cinikin nawa zai kaita sannan ta laluba jakarta cikin fargabar ta fito da kudi?,Allah ya taimaketa jakar a ciki ta sanya kudaden da daddy ya bata sanda zaiyi tafiya,ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana hamdala cikin zuciyarta.

Kusan babu wanda ta tarar cikin ajin,sakamakon akwai tazarar awa guda daga lokacin da za'a shiga lacture din da sanda tazo,guri ta samu na musamman inda tafi sha'awar zama ta zauna,sa'an nan ta zaro handout dinta taci gaba da dubawa kafin lokacin da zasu zana test din ya cika.

*mrs muhammad ce*👑
[09/01, 4:17 PM] +234 803 238 4602: 🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣

*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)✍

0⃣2⃣

Kusan rabi da rabi take karatun,fiye da rabin hankalinta ya ta'allaqa ne akan wayarta,wadda ba komai take kalla ba sai wasu numbers wanda ke rubuce da sunan MAMA NA,ta kallesu yafi sau shurin masaki,ta kwatanta kira fiye da irgen yatsun hannunta saidai ta kasa hakan,ba wani abu bane ya jawo haka ba illa tsoro da fargabar abinda kiran zai biyo baya,taji ance bata ji dadi ba,tana so ta kirata ta mata sannu da jiki,saidai bata da wannan damar,ba qaramin qunar baqin wake take ba duk sanda tayi jarumtar kiranta,wanda hakan daga qarshe baya haifar mata da d'a mai idanu.

"Qawata sarkin sammako" taji an ambata ta gefanta,wayar ta rufe ya dago kai fuskarta qunshe da murmushi tana duban Aliya dake sauke jakarta daga kafada kana ta yiwa kanta mazauni kusa da ayshan itama tana murmushi
"To ya za'ayi" ayshan ta maida mata amsa tana gyara zamanta
"Hala yauma uwar masu gidan zata fito da wuri ne kika kwaso qafa kika biyota?" A maimakon ta bata masa murmushi ayshan ta saki,tasan halin rigima sarai irin na Aliya.

'Yar tsama suke qwarai da asma'u,basa hada hanya da ita,saboda banbancin halaye qwarai dake tsakaninsu,bugu da qari tana jin haushin yadda take mu'amalantar ayshan wadda ta zame mata qawa kuma aminiya a dui fadin makarantar,sosai Aliya keson aysha sabo managartan halayenta,nutsuwa haquri gami da kunya,uwa uba ayshan na daya daga cikin daliban da sukayi fice a duk fadin department dinsu,kai bama iya tsangayar tasu kadai ba a duka makarantar ma.

Kai Aliya ta kada cikin takaici,saidai ayshan bata bata damar cewa komai ba ta tareta
"Kinso yau ki makara qawata,ya akai haka?"
"Hmmm,wlh yau mama ta tsaidani sai dana hadawa ya khalil breakfast,Allah ne ya soni na masa sharp sharp na fece,da Allah ne kadai ya san makarar da zanyi" duka tana zancan ne sanda take ciro handout dinta daga jaka,kafin su sake cewa komai lacturer din ya shigo ajin.

Qarfe uku na rana ta kammala duk abinda zatayi cikin makarantar,hakan ya sanya ta tattara komai nata ta fito don ta qarasa inda zata samu asma'u,saidai koda taje wayam taga wurin babu alamun motarta,hakan ke nuna bata cikin makarantar,bata wani damu ba ta soma takawa da qafa don zuwa bakin get din makarantar don ta sami abun hawa,don yau Aliya ta rigata tafiya gida,ita ta tsaya ta dudduba wasu karatuttuka.

Jin qarar mota a bayanta ya sanyata sake rabewa don bawa motar damar wucewa,a sannan idonsu ya hadu da drivern,asma'u ce,ita da wasu mutum biyu a motar,da alama qawayenta ne,dauke kai asma'un tayi tamkar bata ganta ba,sai tama qarawa motar wuta tayi hanzarin wuce ayshan,sam hakan bai dameta ba,saboda ba yau farau ba,babu abinda asma'un ta tsana nan gidan duniya irin alaqar da zata bayyanar da cewa ayshan jininta ce,gida daya suka fito ko suna da dangantaka,tunda ayshan ta fahimci hakan sai itama take baya baya da duk wata alaqa da zata hadata da asma'u cikin bainar jama'a.

Kai ta jinjina kawai taci gaba da takawa zuwa qofar makaranta,wannan abun na asma'u zata iya cewa bai bata ranta ko kadan,idan ma ya bata din bai wuce digo daya cikin dari ba,a yanzu qyamatar da take fuskanta take kuma bata mamaki ta shafe ko wacce iriyar qyama da qiyayya da dukkan wata halitta zata nuna mata a doron duniya,dukkan wata tsana saidai ta biyo bayan waccar,da wannan tunanin ta tsaida wani dan sahu dake niyyar gifatata ta masa kwatance inda zata ta fada ciki.

Kamar kullum yauma a qalla ya kusa shafe mintuna ashirin yana tsaye yana jiranta,har sai data kaishi ga qosawa ya haye saman babur din da yazo da shi ya zauna,saboda rashin sabo saura kadan babur din ya tuntsira da shi Allah ya taimaka cikin zafin nama yayo gaba ya dawo ya zauna dai dai,mahmoud dake zaune cikin motarsu dake fake a wani layi ya tuntsire da dariya harda duqawa,ba don ba dabanba da ya fito ya masa vedio ya ajjiye saboda tarihi,saidai yana tsoron tashin balli tilas ya zauna cikin motar kamar yadda yayi masa umarni.

Sake duba agogonsa yayi yana qissimawa ranshi mintinan da zai qara wanda matuqar bata fito ba zai qara gaba,a gajiye yake,daga airphort yake ko gida bai isa ba ya sauya kaya ya canza akalar tafiyar tasa zuwa gidansu,bayan ya yiwa daya daga cikin yaranshi waya ya kawo masa babur din,kwanaki goma ya kwashe a qasar da yaje,bai kuma samu damar kiranta ba tunda ya tafi saboda gudun tonuwar asiri,don kada ta tsammaci ya janye hakan ne ya sanyashi tahowa kai tsaye gidansu.

Kamar ko yaushe yauma haka fuskarta take,ta qaraso inda yake saidai a yau waya take amsawa,ganin ta iso gareshi yasa ta bada uzurin zata sake kira ta kashe wayar ta lanqwasheta a hannunta yauma tana sake qare masa kallo a kaikaice
"Allah ya baka kyau na nunawa sa'a,saidai hakan ba zaiyi tasiri a raina ba saboda kana da babban naqasu na rashin hatimin nasara" duka take wannan maganar a ranta,sama sama suka gaisa tamkar baqin juna,shi kansa yana jin wani irin cikin ranshi,duk yadda yaso kawo sabo da shaquwa tsakaninsu zulaihat taqi bashi dama.
Chapter 2 · 0% Book details