Sashe 97
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sha daya da rabi da minti biyar wanda yayi dai dai da sha biyu da rabi da minti biyar a cyprus,kwanciyarshi kenan saman gadonshi,kaman bazai daula ba,amma ganin kiran daga nijeria ne ya sanyashi dagawa bayan tayi kamar zata tsinke,jin muryar mace sai ya bashi mamaki,muryar da bai santa ba
"Amincin Allah ya tabbata a gareka"
"Wa'alaikumussalam warahmatullah" ya maida mata da yaren larabci
"Ina fatan kana lafiya kamar yadda nake,duk da ni din sai a hankali tawa lafiyar"
"Amm,idan babu damuwa da Allah zan iya sanin dawa nake magana"
"Kasha kuruminka,ba wata bace illa asma'u,tsohuwar masoyiyarka"
"Asma'u?,asma'u?" Haka ya dinga nanata sunan a ranshi yana son tuna wacce asma'u,asma'un ce ta fado mishi,saidai ita din a yadda ya sani matar aure ce,akanme kuma zatayi kiranshi a irin wannan lokaci?,hasalima bata da numbersa
"Idan baka gane ba bari nayi maka dalla dalla,asma'u dai wadda ka fara cewa kana so tayi kuskure da gangancin hadaka da aysha bayan ita tafi kowa dacewa dakai" gaba daya sai yaji kaman yana magana ne da zararriya,kodai ba cikin hayyacinta take ba?
"Am lafiya kike kuwa?," yana nufin cikin hankalinta take,amma fuskanci maganarsa ba
"Lafiya nake,amma ba lau ba" zuciyarshi ce ta bashi shawarar sauraro kafin yanke hukunci,saboda haka yace da ita
"Uhmm....me yake faruwa?,ina kika samu numberta?"
"Khalipha kenan...."
"Point of correction..." Yayi saurin katseta
"Yaron oga dai" a shagwabe tace dashi
"Haba don Allah,na baka haquri fa tuni,amma bai wuce a wajenka ba?kuna yanzu ma kira nayi na sake baka wani haqurin don Allah ka yafemin komai ya wuce" Tsaki yaja a bayyane wanda ya isa kunnenta
"Me kika yimin da zaki bani haquri?,idan ma kina tunanin akwai wani laifi da kika yimin ma to babu,nikam khalipha saidai nayi miki godiya ma,domin duk abinda kike zaton kinyi alkhairi ya zamewa rayuwata da ita wadda kikayi nufin cutarta,karki sake kirana daga yau,don ni bana magana da matan mutane" yana kaiwa nan yayi hanzarin kashe wayar zuciyarsa na masa wasi wasin kiran asma'u,yanayin yadda take karya mishi murya dayi masa magana kadai ya isa ya karantar dashi akwai wata a qasa,yasan halin mata da yawa hakanan dai dai gwargwado ya karancesu,shikam saidai ya bawa wani labari,kiranta ne ya dinga shigowa babu adadi har sai daya gaji ya danna mata block,sai kuma ta koma sms wanda sukayita shigowa a jajjere,tsaki ya saki sannan ya kashe wayar gaba daya,bayan ya sake blocking yadda bata da damar sake tura masa wani saqo.
Kuka asma'un ta sako sanda ta fuskanci dukan abinda yay mata,saita zauna sosai saman gado tana sharban kukanta,tana jin cewa ba zata iya haqura ba dole tayi hanzarin fita daga gidan hamid,tana tsaka da haka ne hamid ya turo qofar dakin ya shigo,kallo daya yayi mata ya dauke kanshi bai tanka mata ba,sai daya gama sabgar gabanshi sannan ya dubeta da qyar
"Ke kuma waye ya mutu kika zauna kina yiwa mutane irin wannan kukan da daren nan?" Harara ta watsa masa,cikin izgili da rashin mutunci tace
"Ban sani ba,aikin banza aikin wofi,wallahi hamid ko kafi quda naci saika sakeni,don na gama zaman aure dakai"
"Ki iya bakinki tun bai jawo miki duka ba"
"Ai wallahi nabar zama ka taba lafiyata tunda bakai ka halicceni ba,banza wawa sakaran namiji dabai da aiki sai dukan matarsa" nan fa ya harzuqa,baiyi wata wata ba ya kasheta da mari sannan ya miqe yana huci
"Laifi nane dana sassauta miki kwana biyu kinga kina ci kina qoshi,to bari na sake jaddada miki tunda dama can ke jaka ce wadda ta fita makaranta da C.O,aure yanzu na fara,babu saki tsakaninmu har abada" ya juya yabar dakin,ashar takeson danna masa amma tana son lafiyarta,haka ta hadiye sai daya fice sannna ta dinga zage zagenta tare da cin alwashin gobe sai gida.
Zaune yake cikin office din nashi wanda yana sauka a qasar can ya soma zuwa,duk da yadda ya qagu matuqa yayi tozali da ita amma dole ya soma biyawa can,yantsunshi harde cikin juna,yayin daya dorasu saman table din gabanshi,ya kuma zubawa aljh kutama idanu yayin da alhj kutaman ya hada gumi sharkaf,ilahirin jikinsa rawa yake,tsananin tashin hankalin da yake ciki bazai misaltu ba
"Alhj kutama" khaliphan ya kira sunanshi kai tsaye abinda kusan bai taba yiba,kasancewar sunyi mu'amala da mahaifinshi kamar yaron mahaifinsa ne,amma hakan baisa ya daina bashi girma ba
"Alhj kutama" ya sake kiran sunan nashi
"Na'am yallabai,ranka ya dade Allah ya taimakeka...." Ya fada cikin dimuwa da rudu
"Duk abinda kake da kudina dana samu ta hanyar halas,nake baka saboda taimako darajar iyali da kake dashi kaje ka juya ta hanyar halas,duk sanda ka samu riba ta halas ka dawomin da kudina,nasan me kake dasu,haka mukayi dakai?"
"Wallahi yallabai akasi aka samu,ba halina bane"
"Alhj kutama"
"Na'am yallabai"
"Na bala nan da jibi ka tattara dukkan kudina dana ranta maka ka dawo min dasu,ban kuma yardaba ban lamunce ka kawomin wadanda ka samu ta qazantacciyar harqallarka ba" juya kai ya soma yi zai soma roqo da bashi haquri,cikin hanzari khaliphan ya dakatar dashi
"Banason naji komai daga bakinka,magana ce munyita dakai tsahon minti ashirin,duk cikin maganarka babu gaskiya a ciki,hakanan kuma ban sameka ba sai dana sanya aka yimin bincike a kanka,so ka riqe duk abinda kake da shirin fada kayi abinda nace maka" yasan halin yaron sarai,kaifi daya ne,ya riga daya karya duk wani abu da zai sanya ya tausaya masa ko ya janye hukuncinsa a kanshi,hakan ya sanya dole ya miqe yana jan qafa cikin tashin hankalin inda zai samo masa kudinsa ya fice,don dukka kudin ya tattara aka sayi cocain dasu da zummar idan suka wuce zasu samu riba mai yawa,sai gashi an kama yaran kuma suna shirin fadar sunanshi,tabbas daga shi har hamid suna cikin masifa,don har hamid din shima ya karbi bashin kudade masu yawa daga wajenshi,yace kuma dukansu su dawo masa da kudin,kuma baya jin a yanzu akwai kudin wajen hamid din shima,yace ya zuba kudin a wani kamfani da zasu dinga bashi ribar kudade mai yawa duk qarshen sati.
Waya ya dauka ya kira hamid din,yace kome yake yabarshi ya sameshi a gida,sannan ya wuce gidan shima afujajan cikin motocin da yake yawo dasu kamar wani gwamna,yaga alama talauci ne yakeson yayi masa saukar gaggawa alhalin bai shirya taryarshi ba daga nan har randa zai bar duniya,haka motocin suka dinga tafiya da sauri sauri,wannan burgar tashi da nunawa duniya shi lallai wani ne yasa sunanshi yayi suna yayi tambari,bayan kuma baikai inda yakeson ace yakai din ba,hakanan a wajenshi dukka yaranshi suka gado qarya da fafa.
Numfashi khalipha ya sauke yana sakin ajiyar zuciya gami da lumshe idanunshi,ya kara bayanshi da kujerar da hake kai yana istigfari,sosai ranshi ya baci matuqa,ya jima yana baiwa mutumin rance ga zatonshi yana amsa ne donya tallafi kanshi,duk da ya dade yana mamakin salon rayuwarshi,ya daukaki komai nashi bayan kusan qashin bayan arziqin nasa bashi ne,saidai ganin komai na tafiya dai dai tsakaninsu ya sanya ya kauda kai daga gareshi,daga bayane yadda kudim suke saurin dawo masa gami da gwaggwabar ribar da yake gaya masa yana samu a lokaci kadan kan kasuwancin da yakeyi ne yasa masa ayar tambaya,don duk abinda khaliphan zaiyi yakanyi takatsantsan da kaucewa haramun,saboda annabi S A W yana cewa haram a bayyane take hakama halal,saidai tsakaninsu akwai al'amura masu rikitarwa da shubha,wanda ya kiyaye wannan shubhar haqiqa ya kubutar da addininsa da mutuncinsa.
Bazai lamunci ko ya yarda ya ciyar da duk wanda ya danganceshi da haramun ba,walau kana aiki qarqashinsa ne ko kuma kankat mai gaba daya mahaifiyarsa da 'yan uwansa,saboda annabi S A W yayi bayani cewa,duk jikin daya ginu da haram,to wuta ita tafi cancanta da ita(wato wuta ita tafi cancanta ta cinye wannan tsokar,jan hankali a nan a garemu mata shine,muyi qoqari mu dinga tunasar da mazanmu koda yaushe su nemo halal su kawo mana halal,musamman yanzu da babu tayi yawa,albarka ta ragu cikin dukiyoyi da kayayyakinmu,don billhil azim maganar ma'aiki ba zata tashi a banza ba,duk wanda bai kiyaye haramun ba,ya yadda ake ci dashi a tufatar dashi asha dashi da haramun,to babu shakka ranar qiyama ya lissafa kansa cikin wanda wuta zata ci,saboda haka mu yiwa kanmu 'ya'yanmu da mazajenmu gata mu dorasu kan neman halali domin samun dace da tsira ranar da wata rai ba zata tsinanawa wata rai komai ba,matan sahabbai sun kasance kullum ta Allah idan mazanau zasu fita nema,sukan tsaidasu auce,yakai wane kaji tsoron Allah,ka nemo mana halak,don zamu iya haquri da yunwa amma ba zamu iya haquri da azabar Allah ba,Allah yasa mu dace)mutane da yawa sun shaida sirrin yauqaqar arziqinsa da albarkarsa shine kiyaye haqqin Allah da yakeyi a ciki,sannan kuma biyayya ga mahaifa.
Saida ya shiga toilet ya daura alwala sannan yaji zuciyarshi na sanyaya(ki riqe wannan 'yar uwa,a duk sanda kike jin bacin rai,ko wani abu ya bata miki rai,walau tsakaninki da mijinki ko wani daban,kije ki dauro alwala sannan kiyita karanta a'uzubillahi minash shaidanir rajim,da yardar Allah zakiji zuciyarki tana, sanyi)shauqin isa zuwa gida ya dawo mishi fil,sai ya zauna kan kujerar sofa din dake office din ya tura gajeran saqo,cikin 'yan mintina mutum biyu suka shigo,daya ya soma rufe mishi jakarshi,yayin da dayan ke tsaye saman kanshi,duqawa yayi.ya maida safarshi sannan ya saka takalminshi ya miqe yayi gaba suka rufa mishi baya suka fice da kamfanin gaba daya.
53
Tunda gari ya waye ranar bata shiga sashen anni ba,tana sashensu bayan ta gama duka gyare gyaren da zatayi ta sake kwanciya,ta ware fanka da acn dake falon duka saboda zafin da ake zubawa,wanda alamun zuwan damina duka sun gama bayyana,donko a jiya hadari sosai garin ya hada har aka tsammaci samun ruwan sama,saidai ruwan bai samu ba sai yayyafi da akayi wanda shi ya sake tada zafi a garin duka yau,da kuma wani sabon hadarin dake hadowa kadan kadan yana curewa waje daya gami da bada kala mai duhu,hakan ya sanya rana ta kasa samun dama fidda haskenta,qarfe hudu saura ta tashi daga bacci,ta daura alwala ta bada faralin sallah sannan ta shiga bandaki ta saki ruwa mai sanyi ba tare data sirka ba tayi wanka,hakan ya haifarwa da zuciyarta wani irin nishadi,zuciyar da gangar jikin dukka sukayi fes dasu,iskar dake busowa cikin windows din dakin tayi mata dari,sai taji tana bata wani sanyi na musamman dake ratsawa har cikin qwaqwalwa da zuciyarta.
"Amincin Allah ya tabbata a gareka"
"Wa'alaikumussalam warahmatullah" ya maida mata da yaren larabci
"Ina fatan kana lafiya kamar yadda nake,duk da ni din sai a hankali tawa lafiyar"
"Amm,idan babu damuwa da Allah zan iya sanin dawa nake magana"
"Kasha kuruminka,ba wata bace illa asma'u,tsohuwar masoyiyarka"
"Asma'u?,asma'u?" Haka ya dinga nanata sunan a ranshi yana son tuna wacce asma'u,asma'un ce ta fado mishi,saidai ita din a yadda ya sani matar aure ce,akanme kuma zatayi kiranshi a irin wannan lokaci?,hasalima bata da numbersa
"Idan baka gane ba bari nayi maka dalla dalla,asma'u dai wadda ka fara cewa kana so tayi kuskure da gangancin hadaka da aysha bayan ita tafi kowa dacewa dakai" gaba daya sai yaji kaman yana magana ne da zararriya,kodai ba cikin hayyacinta take ba?
"Am lafiya kike kuwa?," yana nufin cikin hankalinta take,amma fuskanci maganarsa ba
"Lafiya nake,amma ba lau ba" zuciyarshi ce ta bashi shawarar sauraro kafin yanke hukunci,saboda haka yace da ita
"Uhmm....me yake faruwa?,ina kika samu numberta?"
"Khalipha kenan...."
"Point of correction..." Yayi saurin katseta
"Yaron oga dai" a shagwabe tace dashi
"Haba don Allah,na baka haquri fa tuni,amma bai wuce a wajenka ba?kuna yanzu ma kira nayi na sake baka wani haqurin don Allah ka yafemin komai ya wuce" Tsaki yaja a bayyane wanda ya isa kunnenta
"Me kika yimin da zaki bani haquri?,idan ma kina tunanin akwai wani laifi da kika yimin ma to babu,nikam khalipha saidai nayi miki godiya ma,domin duk abinda kike zaton kinyi alkhairi ya zamewa rayuwata da ita wadda kikayi nufin cutarta,karki sake kirana daga yau,don ni bana magana da matan mutane" yana kaiwa nan yayi hanzarin kashe wayar zuciyarsa na masa wasi wasin kiran asma'u,yanayin yadda take karya mishi murya dayi masa magana kadai ya isa ya karantar dashi akwai wata a qasa,yasan halin mata da yawa hakanan dai dai gwargwado ya karancesu,shikam saidai ya bawa wani labari,kiranta ne ya dinga shigowa babu adadi har sai daya gaji ya danna mata block,sai kuma ta koma sms wanda sukayita shigowa a jajjere,tsaki ya saki sannan ya kashe wayar gaba daya,bayan ya sake blocking yadda bata da damar sake tura masa wani saqo.
Kuka asma'un ta sako sanda ta fuskanci dukan abinda yay mata,saita zauna sosai saman gado tana sharban kukanta,tana jin cewa ba zata iya haqura ba dole tayi hanzarin fita daga gidan hamid,tana tsaka da haka ne hamid ya turo qofar dakin ya shigo,kallo daya yayi mata ya dauke kanshi bai tanka mata ba,sai daya gama sabgar gabanshi sannan ya dubeta da qyar
"Ke kuma waye ya mutu kika zauna kina yiwa mutane irin wannan kukan da daren nan?" Harara ta watsa masa,cikin izgili da rashin mutunci tace
"Ban sani ba,aikin banza aikin wofi,wallahi hamid ko kafi quda naci saika sakeni,don na gama zaman aure dakai"
"Ki iya bakinki tun bai jawo miki duka ba"
"Ai wallahi nabar zama ka taba lafiyata tunda bakai ka halicceni ba,banza wawa sakaran namiji dabai da aiki sai dukan matarsa" nan fa ya harzuqa,baiyi wata wata ba ya kasheta da mari sannan ya miqe yana huci
"Laifi nane dana sassauta miki kwana biyu kinga kina ci kina qoshi,to bari na sake jaddada miki tunda dama can ke jaka ce wadda ta fita makaranta da C.O,aure yanzu na fara,babu saki tsakaninmu har abada" ya juya yabar dakin,ashar takeson danna masa amma tana son lafiyarta,haka ta hadiye sai daya fice sannna ta dinga zage zagenta tare da cin alwashin gobe sai gida.
Zaune yake cikin office din nashi wanda yana sauka a qasar can ya soma zuwa,duk da yadda ya qagu matuqa yayi tozali da ita amma dole ya soma biyawa can,yantsunshi harde cikin juna,yayin daya dorasu saman table din gabanshi,ya kuma zubawa aljh kutama idanu yayin da alhj kutaman ya hada gumi sharkaf,ilahirin jikinsa rawa yake,tsananin tashin hankalin da yake ciki bazai misaltu ba
"Alhj kutama" khaliphan ya kira sunanshi kai tsaye abinda kusan bai taba yiba,kasancewar sunyi mu'amala da mahaifinshi kamar yaron mahaifinsa ne,amma hakan baisa ya daina bashi girma ba
"Alhj kutama" ya sake kiran sunan nashi
"Na'am yallabai,ranka ya dade Allah ya taimakeka...." Ya fada cikin dimuwa da rudu
"Duk abinda kake da kudina dana samu ta hanyar halas,nake baka saboda taimako darajar iyali da kake dashi kaje ka juya ta hanyar halas,duk sanda ka samu riba ta halas ka dawomin da kudina,nasan me kake dasu,haka mukayi dakai?"
"Wallahi yallabai akasi aka samu,ba halina bane"
"Alhj kutama"
"Na'am yallabai"
"Na bala nan da jibi ka tattara dukkan kudina dana ranta maka ka dawo min dasu,ban kuma yardaba ban lamunce ka kawomin wadanda ka samu ta qazantacciyar harqallarka ba" juya kai ya soma yi zai soma roqo da bashi haquri,cikin hanzari khaliphan ya dakatar dashi
"Banason naji komai daga bakinka,magana ce munyita dakai tsahon minti ashirin,duk cikin maganarka babu gaskiya a ciki,hakanan kuma ban sameka ba sai dana sanya aka yimin bincike a kanka,so ka riqe duk abinda kake da shirin fada kayi abinda nace maka" yasan halin yaron sarai,kaifi daya ne,ya riga daya karya duk wani abu da zai sanya ya tausaya masa ko ya janye hukuncinsa a kanshi,hakan ya sanya dole ya miqe yana jan qafa cikin tashin hankalin inda zai samo masa kudinsa ya fice,don dukka kudin ya tattara aka sayi cocain dasu da zummar idan suka wuce zasu samu riba mai yawa,sai gashi an kama yaran kuma suna shirin fadar sunanshi,tabbas daga shi har hamid suna cikin masifa,don har hamid din shima ya karbi bashin kudade masu yawa daga wajenshi,yace kuma dukansu su dawo masa da kudin,kuma baya jin a yanzu akwai kudin wajen hamid din shima,yace ya zuba kudin a wani kamfani da zasu dinga bashi ribar kudade mai yawa duk qarshen sati.
Waya ya dauka ya kira hamid din,yace kome yake yabarshi ya sameshi a gida,sannan ya wuce gidan shima afujajan cikin motocin da yake yawo dasu kamar wani gwamna,yaga alama talauci ne yakeson yayi masa saukar gaggawa alhalin bai shirya taryarshi ba daga nan har randa zai bar duniya,haka motocin suka dinga tafiya da sauri sauri,wannan burgar tashi da nunawa duniya shi lallai wani ne yasa sunanshi yayi suna yayi tambari,bayan kuma baikai inda yakeson ace yakai din ba,hakanan a wajenshi dukka yaranshi suka gado qarya da fafa.
Numfashi khalipha ya sauke yana sakin ajiyar zuciya gami da lumshe idanunshi,ya kara bayanshi da kujerar da hake kai yana istigfari,sosai ranshi ya baci matuqa,ya jima yana baiwa mutumin rance ga zatonshi yana amsa ne donya tallafi kanshi,duk da ya dade yana mamakin salon rayuwarshi,ya daukaki komai nashi bayan kusan qashin bayan arziqin nasa bashi ne,saidai ganin komai na tafiya dai dai tsakaninsu ya sanya ya kauda kai daga gareshi,daga bayane yadda kudim suke saurin dawo masa gami da gwaggwabar ribar da yake gaya masa yana samu a lokaci kadan kan kasuwancin da yakeyi ne yasa masa ayar tambaya,don duk abinda khaliphan zaiyi yakanyi takatsantsan da kaucewa haramun,saboda annabi S A W yana cewa haram a bayyane take hakama halal,saidai tsakaninsu akwai al'amura masu rikitarwa da shubha,wanda ya kiyaye wannan shubhar haqiqa ya kubutar da addininsa da mutuncinsa.
Bazai lamunci ko ya yarda ya ciyar da duk wanda ya danganceshi da haramun ba,walau kana aiki qarqashinsa ne ko kuma kankat mai gaba daya mahaifiyarsa da 'yan uwansa,saboda annabi S A W yayi bayani cewa,duk jikin daya ginu da haram,to wuta ita tafi cancanta da ita(wato wuta ita tafi cancanta ta cinye wannan tsokar,jan hankali a nan a garemu mata shine,muyi qoqari mu dinga tunasar da mazanmu koda yaushe su nemo halal su kawo mana halal,musamman yanzu da babu tayi yawa,albarka ta ragu cikin dukiyoyi da kayayyakinmu,don billhil azim maganar ma'aiki ba zata tashi a banza ba,duk wanda bai kiyaye haramun ba,ya yadda ake ci dashi a tufatar dashi asha dashi da haramun,to babu shakka ranar qiyama ya lissafa kansa cikin wanda wuta zata ci,saboda haka mu yiwa kanmu 'ya'yanmu da mazajenmu gata mu dorasu kan neman halali domin samun dace da tsira ranar da wata rai ba zata tsinanawa wata rai komai ba,matan sahabbai sun kasance kullum ta Allah idan mazanau zasu fita nema,sukan tsaidasu auce,yakai wane kaji tsoron Allah,ka nemo mana halak,don zamu iya haquri da yunwa amma ba zamu iya haquri da azabar Allah ba,Allah yasa mu dace)mutane da yawa sun shaida sirrin yauqaqar arziqinsa da albarkarsa shine kiyaye haqqin Allah da yakeyi a ciki,sannan kuma biyayya ga mahaifa.
Saida ya shiga toilet ya daura alwala sannan yaji zuciyarshi na sanyaya(ki riqe wannan 'yar uwa,a duk sanda kike jin bacin rai,ko wani abu ya bata miki rai,walau tsakaninki da mijinki ko wani daban,kije ki dauro alwala sannan kiyita karanta a'uzubillahi minash shaidanir rajim,da yardar Allah zakiji zuciyarki tana, sanyi)shauqin isa zuwa gida ya dawo mishi fil,sai ya zauna kan kujerar sofa din dake office din ya tura gajeran saqo,cikin 'yan mintina mutum biyu suka shigo,daya ya soma rufe mishi jakarshi,yayin da dayan ke tsaye saman kanshi,duqawa yayi.ya maida safarshi sannan ya saka takalminshi ya miqe yayi gaba suka rufa mishi baya suka fice da kamfanin gaba daya.
53
Tunda gari ya waye ranar bata shiga sashen anni ba,tana sashensu bayan ta gama duka gyare gyaren da zatayi ta sake kwanciya,ta ware fanka da acn dake falon duka saboda zafin da ake zubawa,wanda alamun zuwan damina duka sun gama bayyana,donko a jiya hadari sosai garin ya hada har aka tsammaci samun ruwan sama,saidai ruwan bai samu ba sai yayyafi da akayi wanda shi ya sake tada zafi a garin duka yau,da kuma wani sabon hadarin dake hadowa kadan kadan yana curewa waje daya gami da bada kala mai duhu,hakan ya sanya rana ta kasa samun dama fidda haskenta,qarfe hudu saura ta tashi daga bacci,ta daura alwala ta bada faralin sallah sannan ta shiga bandaki ta saki ruwa mai sanyi ba tare data sirka ba tayi wanka,hakan ya haifarwa da zuciyarta wani irin nishadi,zuciyar da gangar jikin dukka sukayi fes dasu,iskar dake busowa cikin windows din dakin tayi mata dari,sai taji tana bata wani sanyi na musamman dake ratsawa har cikin qwaqwalwa da zuciyarta.