← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 109 OF 114

Sashe 109

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A nutse ya tura qofar yayi sallama,cikin sa'a ayshan ce kadai zaune tana shan fruit salad na musamman da aka zuba mishi zuma da madara,wanda a fakaice anni ta hada mata shi saboda qarin ni'imar jikinta,ita kuwa tunda ta d'an d'ana taji yayi mata shikenan ta samu abinyi,idonta ta daga ta kalleshi sanda shima yake dubanta bayan ya kalli bowl din gabanta mai dauke da fruit salad din,murmushi ta saki tana nuna mishi kwanon
"Ya khalipha bismillah" harara ya dan watsa mata qasa qasa yadda anni ba zata ji ba yace
"Bana sha...ki tashi ki shirya mu wuce gida" saita langwabe kai,tana jin dadin zamanta da anni sosai
"Ya khalipha ka bar....." Sai ya dora yatsanshi akan lips
"Shshshshsh.....bana son jin komai ki tashi kawai"
"Yaya dai khalipha?" Anni dake fitowa daga toilet ta ambata tana dubanshi,sai ya dan sosa kanshi kadan yana cewa
"Babu komai anni" juyawa yayi ya sake jaddadawa aysha maganar da ido sannan ya juya zai fice
"Zo nan" anni tace dashi tana qoqarin zama,dawowa yayi
"Ka kora min yara shine zaka wuce kubarmin gida ni daya kenan ko?" Ta fada tana dubanshi,sai yayu shuru yana shafa kanshi
"Zauna" ta nuna mishi waje,zaman yayi yana kaucema kallon annin
"Duk inda musulmi yake ana son ya zama mai manta sharri,mara manta alkhairi,anason idan mutum ya maka sharri kai ka saka masa da alkhairi,a sanda duk Allah ya maka sauyin yanayi na alkhairi ganin damarshi ne,sanda Allah yayi maka arziqi ka wadata mabuqata,sabida wannan arziqin ba kai kadai ya bawa ba ya baka ne harda su,sai ya sanyashi a hannunka,babu abinda zai rageka dashi donka kyautatawa wanda ya zalunceka,sai qarin daukaka da zaka samu wajen ubangiji,na yaba maka sosai da yadda kayi haquri kuma kabi maganata,ka dauki ragamar kyautata musu kamar yadda mahaifinka yayi kafin yabar duniya duk da nasan tanqwara zuciyarka kawai kake,a yanzu bazan sake takuraka kan zamansu amal cikin gidan nan ba,don na tabbatar gudun faruwar matsala yasa kayi haka,nima kuma daga bisani na hangi hakan,zuwa yanzu dama yaci ace kowacce ta maida hankalinta jikinta ta fitar da mijin aure tunda gaba dayansu sun kai munzali"
"Hakane anni,kiyi haquri idan kinji babu dadi...yanzu haka mun gama magana da mijin anty ruqayya zai baki nadiya 'yarsa in sha Allahu taci gaba da zama dake,saboda ina tunanin...." Sai kuma ya kasa qarasawa ya soma shafa qeya,tasan yana jin nauyin abinda zai fada mata ne,saita saki murmushi
"Uhmmm"
"Cyprus zamu wuce nida humaira" har qasan zuciyar anni farinciki ne ya lullubeta,abinda take zato ya tabbata,tun ranar farko data gansu taga burbushin haka,dukkan alamu sun suna akwai wata dangantaka mai qarfi atsakaninsu,akwai wani lamari mai girma daya yiwa junansu dabaibayi,amma donson ta sake tabbatarwa sai tace
"Wani irin cyprus?,nata karatun fa?,ba inda zaka daukemin diya ka kaita"
"Wallahi anni bazan iya tafiya na barta ba don Allah karkice na tafi na barta,in kika ce haka kona tafi bazan iya qarasa nawa karatun ba kuma nawa yafi nata muhimmamci...."yayi subutar bakin fadan wadannan kalmomin ba tare daya shirya fadarsu ba
"Dakata..." Tayi hanzarin tsaidashi karya ballo maganar data fi haka nauyi
"Saikun dawo Allah ya kiyaye hanya,ke ayshatu tashi maza ku wuce gidanku nima nan kwanciya zanyi,idan kun fita ku turomin mus'ab ko atika" sai a sannan ya tuna abinda yace mata,kunya duka ta kamashi,amma da yake namiji ne saiya murje ya shigar da godiyarsa,don kada ma ayshan ta bata masa lokaci sai ya tsaya yana jiran ta gama laqai laqai dinta ta tashi,haka ta gama din kuwa ta yiwa anni sallama suka fice.

Tun a gidan annin dama takejin son tayi kuka,wani abu ya takoreta a wuya,tun a can take toshe kukan,suna shiga falon gidansu ta kasa haquri kawai saita saki kukan,juyawa kawai khalipha yayi yana kallonta baki sake,kamar wadda akayiwa wahayin kuka?,bai wani bata bakinsa ba wajen lallashi kawai ya sunkuci abarsa,bai direta ko ina ba sai dakin bacci,sai daya gama budurinsa ya biya dukkan bashin dake kansa sannan ya soma aikin lallashi,nan ta narke masa itama ta zuba shagwabarta son ranta shi kuma ya biye mata,sai daya sha rarrashi sannan ya samu kanta suka shiga wanka tare,wanda kusan al'adarshi ce haka,saboda koyi da fiyayyen halitta annabi muhammad S A W.

Bayan kwana biyu akayi bikin bude katafaren shagon nata,wanda walima tayi dai dai gwargwado,donta rage wani abunma saboda mutuwar daddy amma tayi walima sosai anci an sha anyi sadaka.

Kwanaki bakwai suka qara a nigeria suka shirya don komawa cyprus ita dashi,ana washegari zasu koma taje gidan daddy donta qara ganin mummy.

Ba qaramin tausayi mummyn ta bata ba yadda ta rame tayi baqi ta zabge lokaci guda kamar ba ita ba,ba qaramin duka mutuwar daddy tayi mata ba,fuskarta a sake ta amshi ayshan har hakan ya bata mamaki,don bata tsammaci haka daga gareta ba
"Allah ya kiyaye hanya yasa aje a sa'a" mummyn ta fada cikin sanyin jiki,abinda bai taba hadata da mummyn ba,jakarta ta bude ta ciro kudi dubu dari da khalipha ya bata ta basu ta miqawa mummyn,kai ta girgiza
"Bazan iya karbar komai naki ba ayshah,na gode"
"Idan kika ce haka nima baki daukeni kaman asma'u ba kenan?" Kai ta kada hawaye na cika idanunta ta amsa
"Allah yayi miki albarka,ki yafemin aysha dukkan wata cutarwa dana taba yi miki a rayuwa,shaidan ya rufe idanuna,a sanda kike kyautata min idanuna sun rufe,bana ganin dukkan wani alkhairi naki,duk yadda kika kai ga kyautata mana bamu qareki da komai ba face sharri da makirci da muke bibiyarki dashi,mutuwar daddy babbar izina ce a wajena,tabbas dan adam ba'a bakin komai yake ba"
"Ban taba riqonki ba mummy dai dai da rana daya,na yafemiki mummy,Allah ya yafe mana gaba daya" da haka ta fito daga gidan jikinta a sanyaye,daga nan gidan anty safiyya ya kaita,sosai tayi murna da zuwan ayshan,ta dan jima zaune suna hira da ita,sannan ta gaya mata zancan tafiyarsu gobe,sosai ta mata fatan alkhairi
"Nikam kaman qiba naga kin soma aysha,karfa ki zama bindiga?" Murmushi ta saki
"Haba anty,nida na rasa uba wacce qiba zanyi?"murmushi anty safiyya tayi,har cikin zuciyarta tana jin dadin dace da aysha tayi
" ba daga nan take ba aysha,shi ciwon mutuwa Allah yake daukewa bawa shi,banda haka da mutane da dama sun hallaka saboda ciwon rasuwar makusantansu,kekam kinyi haquri a rayuwarki wanda ya zamemiki alkhairi"sai tayi shuru tana aje numfashi,ta gefe guda tana jin tausayin asma'u,tana jin ciwon rayuwar da take ciki,saidai bata karanci komai na nadamarta ko rashin nadamarta ba
"Ki daure ki yafewa asma'u koda bata nemi yafiyarki ba,ki kuma sanyata a addu'a"
"Ni babu komai tsakanina da ita anty,kusan zan iya cewa itace silar matakin dana ke kai yanzu"
"Batayi don alkhairi ya sameki ba,amma dai ki daure ki yafe mata"
"Nikam na yafe mata duniya da lahira" saida khalipha ya kirata sannan ta fito suka tafi.

Suna shirin kwanciya bacci saiga kiran anni ya shigo wayar ayshan,a ladabce cikin kulawa suka gaisa
"Bani khaliphan aysha na kira lambarsa a kashe"
"Toh anni" ta fada tana miqa masa dai dai sanda yake fitowa daga wanka,amsar wayar yayi da daya hannun nashi dayan kuma ya janyota cikin jikinshi ya rungumeta,runtse idanu tayi sanda fatar jikinta ta hadu da tashi,lemar ruwan dake gashin qirjinsa ta ratsa towel din jikinta zuwa fatarta,suna tsaye a haka suka gama gaisawa da annin
"Idris ne fa ba lafiya"idanunsa ya dan lumshe,ko sunanshi baison ji
"wanne idris"
"Gidanku,idris kawunka mana,bashi da lafiya sosai yana jin jiki,lafiya akwa kwanta dashi sai ihunshi aka ji,yanzu haka yana asibi an kwantar dashi,kayi qoqari gobe kafin ku wuce kuje ku dubashi"
"Zanje in sha Allahu"
"Yauwa saida safe"
"Allah ya bamu alkhairi" ya kashe wayar yana sake jan ayshan cikin jikinsa yana sauke ajiyar zuciya,dukkaninsu shuru sukayi,tasan yanzun zaya shiga damuwa daga ambato masa sunan idris,daga bisani ayshan ta juyo da wani irin hanzari ta rungumeshi sosai tana cusa kanta cikin qirjinsa,da qafa daya ta janyo tum tum din dake gefansu ta haye sannan ta samu tsahonsu yazo daya,saita riqe kanshi sosai ta hada hancinsa da nata,bakinta tasa tadan ciji lebansa kadan saiya saki qara
"Wayyo bakina anni zata cinye miki bakin yaro" dariya ta qyalqyale da ita tana daneshi
"Kasan kaci bashina jiya,kuma saika biya?...." Bai barta ta qarasa maganarba ya dauketa cak ya cilla saman gado ya bita yana cewa
"Aga matsoraci tsakanina dake,ke kike tsoron biyan bashi bani ba" tattare jikinta ta soma yi tana dariya gami da bashi haquri,bai yarda ba saida suka fafata ya gajiyar da ita tubus sannan yace ya haqura,tayi shuru na maida numfashin kokawar daya sanyata,tana jin dadi cikin zuciyarta na nasarar shafe masa bacin ran daya so yin tasiri cikin zuciyarsa data yi
"Yarinyar nan qiba naga kin fara yi fa" khalipha ya fada yana dora kanshi saman cinyarta,gami da zagaye qungunta da hannayensa,baki ta zumburo
"Ni ba wani qiba,bayan kaine duk ka hanani qibar,kai baka ga yadda ka soma tumbi ba" qayataccen murmushi ya saki yana maida kwanciyarshi rigingine yana shafa cikinsa da tafin hannunsa daya,ta yadda hakan ya bashi damar kallon fuskarta sosai
"Ni aike nakeso na gani da tumbi,irin tumbin da zaki bani baby fa" kukan shagwaba ta sake masa tana bubbuga hannayenta
"Da wuyafa ya khalipha da wuya..." Dariya ya saki
"Kinsan kuwa jiya nayi mafarki kin haifamin twince masu kama dani?kuma duk mata"
"Sonkai?" Ta fada tana zaro ido tana dariya
"Kona tashi maza zan haifa masu kama da anni koni" idonshi shima ya waro
"Da gaske baby girl nakeso ki haifamin uwaisha..."
"Ni kuma baby boy nakeso,so nake na haifa daddy"
"Shikenan,idan kika haifa mace ni zan saka mata suna,idan namiji ne ke zaki saka"
"Na yarda"
"Mu qulla alqawari" ya fada yana miqa mata qarmin yatsanshi,sai ta miqa masa ita wanda ya shammaceta ya jawota ya maye gurbinta.
[16/03, 11:12 PM] +234 806 544 7089: 59
Chapter 109 · 0% Book details