Sashe 40
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Dukkan abinda yake gudana kusan yana sane da shi ana gaya masa,kama daga events na bikin da yadda komai na gidan ke wakana,hakan ya sanya qarfe tara na dare yayi kiranta,a sannan tana gyarawa su gwaggo wajen kwanciya suna dan taba hira ita da gwaggon da mero,don karime babu wani sabo tsakaninsu,har gwara inna kulu a kanta,don bata taba fito da muguntarta tsirara ba a kanta.
Bata samu ta dauki wayar ba har sai data gama gyara musu wajen sannan ta duba mai kiran,bin kiran tayi don tana da credit wanda daddy ne yakan sanya mata lokaci lokaci,a cewarsa bata iya tambayarsa komai koda tana da buqatar hakan,ita kuma bata saba bane,tun tasowarta bata saba ayi mata abu na,shi yasa ma bata tambaya
"Anata hidimar biki ko ke babu ke...kiyi haquri" abinda yace da ita kenan bayan sun gama gaisawa
"Yayan naki talaka ne...." Ya sake fada a karo na biyu
"Uhmmm" kawai tace tana gyata tsaiwarta,don ita gaba daya tama mance da ana wani abu a biki banda asma'u na nata taron,dan bata sha'awa ma koda zatayi ma wa zata gayyata wa take da shi?,ita duka wannan ba damuwarta bane
"Kinje wajen ne?" Ya tambayeta karo na farko,don yasan ba lallai tayi magana illa kudin wayar da zaita tafiya a haka
"A'ah" ta amsa masa a taqaice
"Saboda me?"
"Iyayena sunzo daga takai...mummy tace na shaida maka gobe zasu zo jere"
"Gashi kuma inaa..." Katsewa yayi da hazari jin ya kusa baranbarama
"Ohk....shikenan...babu damuwa,Allah ya kaimu,zan aiko wani dan uwa na sai ya rakasu"
"Tohm" ta fada kana tayi shuru tana saurare ba tare data ce komai ba,shima jin shirun daga nashi bangaren yasan hirar tasu ta qare saboda haka ya katse kiran,aje wayar tayi suka ci gaba da hirarsu dasu gwaggo.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun tara na safe motar kayan jeran aysha take tsaye qofar gidan wanda kayan ta siyesu ne a zooroad maimakon dubai kamar yadda daddy ya tsara a siya musu kowacce set biyu daga waccar qasa,yayin da wadanda zasu jeran suke shiryawa,wanda yawancinsu ba don Allah zasu je ba,zasu je ne kawai saboda gulma,duk da cewa yau ne dinner din asma'un.
Goma da minti biyar kira ya shiga wayarta da baquwar lamba,cikin mamaki ta daga wayar ta kara a kunneta
"Ranki ya dade nine wanda yallabai ya aiko nayi wa 'yan jere rakiya" cikin mamakin yanda yayi maganar cike da girmamawa tace
"Ohk...to zakayi haquri kadan jirasu na mintina,bari na sanar musu"
"To babu damuwa..." Katse kiran tayi sannan ta dubi inna wadda shigowarta dakin kenan tana taya su mero hada kayan da za'a tafi jeran da su
"Inna...." Ta fada a sanyaye
"Na'am indo"
"Wai wanda zai rakasun ya iso yana bakin gate"
"Toh...toh bari a sanar da su" ta fada tana sakin jakar baccon da take zugewa kana ta fice.
Shiru ayshan tayi kanta a qasa,duk da tana sauraren hirarsu gwaggo asabe jefi jefi,saidai faduwar gaba da damuwa sun mata yawa,fargabar auren take qwarai,gani take kamar zata koma 'yar gidan jiya,yayin da gefe guda na zuciyarta ke cike da damuwa,ina mahaifiyarta ta shiga?,shin ko labarin aurenta ya isa kunnenta?,tasan aure zatayi kuwa?,tana son tambayar gwaggo asabe tun jiya tana jin nauyi da fargaba,Allah kadai shi yasan yadda take ji a zuciyarta
"Ya dai indon baffale?,ko fargabar auren ce irin ta amare?" Mairo wadda ta dafa kafadarta ta fada qasa qasa yadda su kadai zasu ji cikin murmushi,kai ta daga cikin qarfin hali ta maida mata murmushin
"Karki damu....zaki dace in sha Allahu wannan karon" murmushin kawai ta sake mata,kafin tace wani abu muryar inna laraba ta tsaidasu
"Zasu qarasa shiryawa ne saimu wuce".
Har suka gama shuryawar su wadan can 'yan rakiyar basu gama ba,har suka zauna suka huta bayan sun gama nasu aikin suka taba hira shiru kake ji,a qalla saida sukayi jiran awanni biyu sannan suka ce sun gama din su fito.
Da mamaki inna laraba take duban 'yan zuwa jeran,ko a mafarki bata taba tunanin zasu taka gidan aysha ba bate suyi mata jeran aure,dadewarta a gidan ya sanya zata iya fadin halin kowanne daya daga cikin dangin mummy,kai kawai ta gyada cikin ranta tana tabbatarwa kanta cewa akwai lauje cikin nadi,akwai dalilin wannan gangankon nasu,to koda ma saboda Allah zasun 'yammata irin wadan nan masu ji da kai da yauqi ina zasu tsaya yin wani jere,haka dai ta barwa ranta suka shiga motocin da zasu kaisu wajen wanda yawancinsu motocin 'yammatan ne suke ta shewa,duk su qi shiga motar da khalipha ya aiko da sunan wadda zata kaisu sun raina ajinta,sai inna laraba da su gwaggo asabe ne suka shiga.
Yana gaba saman babur dinshi lifan motocin dake dauke da kaya da su inna na biye da shi har suka isa unguwar
"Ya haka?,ya zai kawo mu wata unguwar daban kuma?" Cewar anty halima cikin fushi,da yake gwanar fushi ce ita din,abu kadan yake tunzurata
"Nima dai kamar ba unguwar da asma'u tace mana bace" inji farida tana wulwulga idanu,saboda ita kanta unguwar na daya daga cikin burinkanta a wajen zama.
Shiru ne yaci gaba da wanzuwa har zuwa sanda ya tsaida babur dinshi qofar wani katafaren gida,wanda idan ka tsaya ka qarewa gine ginen kallo kaf layin ba gidan da ya kai girma da tsaruwarshi,suma bakin gidan suka tsaida motocinsu
"Ku zauna...basai kun fito ba" ya fada yana zaro wayarshi daga aljihu,daddadannata yayi sannan ya kara a kunnenshi,waya yayi ta sakan biyar,ba'a cika sakanni goma ba katafariyar qofar gidan ta wangale,mai gadi cikin unifoarm na musamman ya bayyana,daga bayanshi kana iya hanho.
hango makekiyar harabar gidan,wadda ta qawatu da grass carfet da fitilu gami da furanni na alfarma da fitilu dake kunne,da hannu ya musu alamun su shigo,hakan nan suka dinga cusa motocinsu ciki wanda suka tashi laqwam a wajen,ba wanda ya iya magana cikinsu har suka gama dai daita motocin nasu kusa da wadansu kyawawan sabbi fil din motoci guda biyu
"Wai ina ne nan ne?,ina ya kawomu?,karfa yace yana nufin ya kawomu gidan uban gidan sa ne mu soma gaisheshi,an gaya masa mu mabarata ne?....ko qarqashin wani muke ci?" Cewar anty halima sanda suke fiffitowa daga motocin kowa yana qarewa harabar gidan kallo,daga yadda ta tsaru tun daga waje ya isa ya gayawa mutum cewa akwai kallo a ciki ba qarami ba
"Kaga malam mufa ba wasa ne ya kawomu ba muna da abinyi....ba gaida uban gidansa muka zo yi ba wannan matsalarsu,ka kaimu gidan qasa muje mu juye mata kayanta mu wuce"
"Kwantar da hankalinki hajiya....nan ne gidan amaryar" tofa!....sai aka soma kallon kallo tsakaninsu,yayin da murmushin farinciki ya subuce a fuskar mero inna laraba dama gwaggo asabe,duk da mamaki daya cika zuciyarsu fal suma
"Kaman yaya?...mu ba wannan fa gidan ya soma kaimu ba,bashi muka sani ba,sannan yanzu ace nan ne?,hasalima fa wancan gidan gidan qasa ne"
"Gidan qasa?" Mutumin ya fada cike da mamaki yana musu wani kallo
"Boss ne zai zauna cikin gidan qasa?....ai ko masinjansa ke ko mai masa wankin mota yafi qarfin zama cikin gidan qasa ko talauci irin haka,ina tsammanin dai a mafarki hakan ta faru kikai zaton a gaske ne"
"Uwar mafarki nayi....nace maka uwar mafarki nayi ba mafarki ba" ta fada cikin hasalar abu biyu,na farko yana son nuna mata raini raini gaban qannenta,na biyu ta yadda khalipha ya raina musu wayo ya rufesu,tashin hankali ta dinga ji yana rufto mata,ta tabbatar ko asma'u gidanta bai qarasa wannan ba,duk kyan gidanta tasan da zata ga wannan din shi zata fi so,ta yaya hakan ta kasance a kan aysha?
"Allah ya baki haquri hajiya....abun duk baikai ya haka ba...ni dan aike ne....kuma boss yace na girmamaku saboda akwai iyayenta a ciki....ga wadan can" ya fada yana nuna saitin sababbin motocin dake qasan rumfa
"Na amarya ne....ga muqullan idan kuna buqata a baku kukai mata" ya fadi yana ciro muqullan daga aljihunsa,dukkansu mutuwar tsaye sukai ba wanda ta iya magana a cikinsu,baki dayansu ba wadda batasan nawa ne kudin mota duk guda daya ba a ciki
"A'ah ka maida masa ya aje mata....duk randa aka kawo masa ita ya bata da hannunsa" cewar inna laraba da saurinta saboda tsoron karsu amshi key din wani abu yaje ya dawo,sam bata damu da kallon da suka soma jeho mata ba
"To shikenan" ya furta yana maida muqullan aljihun nasa
"Mu qarasa ciki ko?" Ya fada yana yin gaba gami da ciro wasu muqullan daban,inna laraba,mero,gwaggo asabe sune kan gaba,ba abinda bakunansu ke furtawa sai
"Ma sha Allah...alhamdulillah...kai Allah abun godiya" musamman inna laraba da tasan zaman aysha a cikin gidan,muryarta tafi ta kowa dagawa,kuma da biyu take da gayya take,ba qaramin farinciki bane a zuciyarta,ta tabbatar da cewa Allah baya zaluntar bawa saidai bawa ya zalunci kansa,hakanan ubangiji baya mantuwa,karamcinsa baiwarsa da kuma kyautarsa yawa gareta.
Qofar falon kawai tun daga nan suka sallama,inda suka gama miqa wuya sanda suka shiga falon zuwa dakunan baccin dake gidan,gini ne mai kyau mai daukar hankali wanda aka yishi cikin hikima da fasaha,tun daga falon gidan zuwa dakuna zuwa kitchen babu abinda bai saka ba na alatun rayuwa harda ma qaari
"Kai Alhamdulillah...Aysha Allah ya miki baiwa....Allah ya zaba ya baki....Allah ya tabbatar dake cikin wannan gida...yasa tsohuwar gida ce" abinda inna laraba ke fada kenan cikin farinciki suna kewaye gidan,mero ba abinda take cewa ita da gwaggo asabe sai
"Amin...amin" cikin farinciki.
Bata samu ta dauki wayar ba har sai data gama gyara musu wajen sannan ta duba mai kiran,bin kiran tayi don tana da credit wanda daddy ne yakan sanya mata lokaci lokaci,a cewarsa bata iya tambayarsa komai koda tana da buqatar hakan,ita kuma bata saba bane,tun tasowarta bata saba ayi mata abu na,shi yasa ma bata tambaya
"Anata hidimar biki ko ke babu ke...kiyi haquri" abinda yace da ita kenan bayan sun gama gaisawa
"Yayan naki talaka ne...." Ya sake fada a karo na biyu
"Uhmmm" kawai tace tana gyata tsaiwarta,don ita gaba daya tama mance da ana wani abu a biki banda asma'u na nata taron,dan bata sha'awa ma koda zatayi ma wa zata gayyata wa take da shi?,ita duka wannan ba damuwarta bane
"Kinje wajen ne?" Ya tambayeta karo na farko,don yasan ba lallai tayi magana illa kudin wayar da zaita tafiya a haka
"A'ah" ta amsa masa a taqaice
"Saboda me?"
"Iyayena sunzo daga takai...mummy tace na shaida maka gobe zasu zo jere"
"Gashi kuma inaa..." Katsewa yayi da hazari jin ya kusa baranbarama
"Ohk....shikenan...babu damuwa,Allah ya kaimu,zan aiko wani dan uwa na sai ya rakasu"
"Tohm" ta fada kana tayi shuru tana saurare ba tare data ce komai ba,shima jin shirun daga nashi bangaren yasan hirar tasu ta qare saboda haka ya katse kiran,aje wayar tayi suka ci gaba da hirarsu dasu gwaggo.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun tara na safe motar kayan jeran aysha take tsaye qofar gidan wanda kayan ta siyesu ne a zooroad maimakon dubai kamar yadda daddy ya tsara a siya musu kowacce set biyu daga waccar qasa,yayin da wadanda zasu jeran suke shiryawa,wanda yawancinsu ba don Allah zasu je ba,zasu je ne kawai saboda gulma,duk da cewa yau ne dinner din asma'un.
Goma da minti biyar kira ya shiga wayarta da baquwar lamba,cikin mamaki ta daga wayar ta kara a kunneta
"Ranki ya dade nine wanda yallabai ya aiko nayi wa 'yan jere rakiya" cikin mamakin yanda yayi maganar cike da girmamawa tace
"Ohk...to zakayi haquri kadan jirasu na mintina,bari na sanar musu"
"To babu damuwa..." Katse kiran tayi sannan ta dubi inna wadda shigowarta dakin kenan tana taya su mero hada kayan da za'a tafi jeran da su
"Inna...." Ta fada a sanyaye
"Na'am indo"
"Wai wanda zai rakasun ya iso yana bakin gate"
"Toh...toh bari a sanar da su" ta fada tana sakin jakar baccon da take zugewa kana ta fice.
Shiru ayshan tayi kanta a qasa,duk da tana sauraren hirarsu gwaggo asabe jefi jefi,saidai faduwar gaba da damuwa sun mata yawa,fargabar auren take qwarai,gani take kamar zata koma 'yar gidan jiya,yayin da gefe guda na zuciyarta ke cike da damuwa,ina mahaifiyarta ta shiga?,shin ko labarin aurenta ya isa kunnenta?,tasan aure zatayi kuwa?,tana son tambayar gwaggo asabe tun jiya tana jin nauyi da fargaba,Allah kadai shi yasan yadda take ji a zuciyarta
"Ya dai indon baffale?,ko fargabar auren ce irin ta amare?" Mairo wadda ta dafa kafadarta ta fada qasa qasa yadda su kadai zasu ji cikin murmushi,kai ta daga cikin qarfin hali ta maida mata murmushin
"Karki damu....zaki dace in sha Allahu wannan karon" murmushin kawai ta sake mata,kafin tace wani abu muryar inna laraba ta tsaidasu
"Zasu qarasa shiryawa ne saimu wuce".
Har suka gama shuryawar su wadan can 'yan rakiyar basu gama ba,har suka zauna suka huta bayan sun gama nasu aikin suka taba hira shiru kake ji,a qalla saida sukayi jiran awanni biyu sannan suka ce sun gama din su fito.
Da mamaki inna laraba take duban 'yan zuwa jeran,ko a mafarki bata taba tunanin zasu taka gidan aysha ba bate suyi mata jeran aure,dadewarta a gidan ya sanya zata iya fadin halin kowanne daya daga cikin dangin mummy,kai kawai ta gyada cikin ranta tana tabbatarwa kanta cewa akwai lauje cikin nadi,akwai dalilin wannan gangankon nasu,to koda ma saboda Allah zasun 'yammata irin wadan nan masu ji da kai da yauqi ina zasu tsaya yin wani jere,haka dai ta barwa ranta suka shiga motocin da zasu kaisu wajen wanda yawancinsu motocin 'yammatan ne suke ta shewa,duk su qi shiga motar da khalipha ya aiko da sunan wadda zata kaisu sun raina ajinta,sai inna laraba da su gwaggo asabe ne suka shiga.
Yana gaba saman babur dinshi lifan motocin dake dauke da kaya da su inna na biye da shi har suka isa unguwar
"Ya haka?,ya zai kawo mu wata unguwar daban kuma?" Cewar anty halima cikin fushi,da yake gwanar fushi ce ita din,abu kadan yake tunzurata
"Nima dai kamar ba unguwar da asma'u tace mana bace" inji farida tana wulwulga idanu,saboda ita kanta unguwar na daya daga cikin burinkanta a wajen zama.
Shiru ne yaci gaba da wanzuwa har zuwa sanda ya tsaida babur dinshi qofar wani katafaren gida,wanda idan ka tsaya ka qarewa gine ginen kallo kaf layin ba gidan da ya kai girma da tsaruwarshi,suma bakin gidan suka tsaida motocinsu
"Ku zauna...basai kun fito ba" ya fada yana zaro wayarshi daga aljihu,daddadannata yayi sannan ya kara a kunnenshi,waya yayi ta sakan biyar,ba'a cika sakanni goma ba katafariyar qofar gidan ta wangale,mai gadi cikin unifoarm na musamman ya bayyana,daga bayanshi kana iya hanho.
hango makekiyar harabar gidan,wadda ta qawatu da grass carfet da fitilu gami da furanni na alfarma da fitilu dake kunne,da hannu ya musu alamun su shigo,hakan nan suka dinga cusa motocinsu ciki wanda suka tashi laqwam a wajen,ba wanda ya iya magana cikinsu har suka gama dai daita motocin nasu kusa da wadansu kyawawan sabbi fil din motoci guda biyu
"Wai ina ne nan ne?,ina ya kawomu?,karfa yace yana nufin ya kawomu gidan uban gidan sa ne mu soma gaisheshi,an gaya masa mu mabarata ne?....ko qarqashin wani muke ci?" Cewar anty halima sanda suke fiffitowa daga motocin kowa yana qarewa harabar gidan kallo,daga yadda ta tsaru tun daga waje ya isa ya gayawa mutum cewa akwai kallo a ciki ba qarami ba
"Kaga malam mufa ba wasa ne ya kawomu ba muna da abinyi....ba gaida uban gidansa muka zo yi ba wannan matsalarsu,ka kaimu gidan qasa muje mu juye mata kayanta mu wuce"
"Kwantar da hankalinki hajiya....nan ne gidan amaryar" tofa!....sai aka soma kallon kallo tsakaninsu,yayin da murmushin farinciki ya subuce a fuskar mero inna laraba dama gwaggo asabe,duk da mamaki daya cika zuciyarsu fal suma
"Kaman yaya?...mu ba wannan fa gidan ya soma kaimu ba,bashi muka sani ba,sannan yanzu ace nan ne?,hasalima fa wancan gidan gidan qasa ne"
"Gidan qasa?" Mutumin ya fada cike da mamaki yana musu wani kallo
"Boss ne zai zauna cikin gidan qasa?....ai ko masinjansa ke ko mai masa wankin mota yafi qarfin zama cikin gidan qasa ko talauci irin haka,ina tsammanin dai a mafarki hakan ta faru kikai zaton a gaske ne"
"Uwar mafarki nayi....nace maka uwar mafarki nayi ba mafarki ba" ta fada cikin hasalar abu biyu,na farko yana son nuna mata raini raini gaban qannenta,na biyu ta yadda khalipha ya raina musu wayo ya rufesu,tashin hankali ta dinga ji yana rufto mata,ta tabbatar ko asma'u gidanta bai qarasa wannan ba,duk kyan gidanta tasan da zata ga wannan din shi zata fi so,ta yaya hakan ta kasance a kan aysha?
"Allah ya baki haquri hajiya....abun duk baikai ya haka ba...ni dan aike ne....kuma boss yace na girmamaku saboda akwai iyayenta a ciki....ga wadan can" ya fada yana nuna saitin sababbin motocin dake qasan rumfa
"Na amarya ne....ga muqullan idan kuna buqata a baku kukai mata" ya fadi yana ciro muqullan daga aljihunsa,dukkansu mutuwar tsaye sukai ba wanda ta iya magana a cikinsu,baki dayansu ba wadda batasan nawa ne kudin mota duk guda daya ba a ciki
"A'ah ka maida masa ya aje mata....duk randa aka kawo masa ita ya bata da hannunsa" cewar inna laraba da saurinta saboda tsoron karsu amshi key din wani abu yaje ya dawo,sam bata damu da kallon da suka soma jeho mata ba
"To shikenan" ya furta yana maida muqullan aljihun nasa
"Mu qarasa ciki ko?" Ya fada yana yin gaba gami da ciro wasu muqullan daban,inna laraba,mero,gwaggo asabe sune kan gaba,ba abinda bakunansu ke furtawa sai
"Ma sha Allah...alhamdulillah...kai Allah abun godiya" musamman inna laraba da tasan zaman aysha a cikin gidan,muryarta tafi ta kowa dagawa,kuma da biyu take da gayya take,ba qaramin farinciki bane a zuciyarta,ta tabbatar da cewa Allah baya zaluntar bawa saidai bawa ya zalunci kansa,hakanan ubangiji baya mantuwa,karamcinsa baiwarsa da kuma kyautarsa yawa gareta.
Qofar falon kawai tun daga nan suka sallama,inda suka gama miqa wuya sanda suka shiga falon zuwa dakunan baccin dake gidan,gini ne mai kyau mai daukar hankali wanda aka yishi cikin hikima da fasaha,tun daga falon gidan zuwa dakuna zuwa kitchen babu abinda bai saka ba na alatun rayuwa harda ma qaari
"Kai Alhamdulillah...Aysha Allah ya miki baiwa....Allah ya zaba ya baki....Allah ya tabbatar dake cikin wannan gida...yasa tsohuwar gida ce" abinda inna laraba ke fada kenan cikin farinciki suna kewaye gidan,mero ba abinda take cewa ita da gwaggo asabe sai
"Amin...amin" cikin farinciki.