← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 114

Sashe 52

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Aliya ta fada tana murmushi,wani anu ne ya daki zuciyar asma'u,ta yamutae fuska ta cikin mayafinta tana sauraren bugun zuciyarta dason gane me kalaman aliyar ke nufi,bata kai ga wannan gacin ba muryar anty halima ta karade ilahirin falon
"Ke asma'u garin yaya kuka hau motocin rakiyar aysha?,ko haka dama aka tsara?,kin batmu muna can bilayin nemanki badon Allah yasa fatima taga fitarku ba" anty haliman ta furta da alamun bacin rai qarara ga fuskarta ta ratso falon wadda ta shigo afujajan
"What?!" Asma'u ta fada a zabure tana yaye mayafin kanta tana ware idanunta,da daya da daya idanunta ya dinga sauka kan kowanne lungu da saqo na falon tana qarewa dukiyar da aka xuba kallo a fakaice,a lokacin anty halima na fadan kuskuren da aka samu wanda da biyu take masifar,basu saurareta ba tuni suka sada aysha da daya daga cikin dakunan baccinta.

Bata iya tsayawa ta gama kallon dakin ba ta miqe a fusace ta baro falon,zuciyarta kamar zata fito,ranta na tafarfasa,sai data gwammace bata yaye lullubinta ba.

bare tayi tozali da irin falon da take mafarki yau gashi ya zama mallakin aysha,ko a harabar gidan duk yadda taso ta hana idanunta ganin komai hakan ya gagara,iya fitilun da suka haske harabar gidan tarwai kamar rana kawai abun kallo ne,cikin fushi ta ciro wayarta ta soma neman lambar hamid,dama yasan ba ita ya kawowa motocin ba,yasan da haka amma yayi shuru baice komai ba,ya janyo mata abun kunya,me xai kata taka gidan aysha?,yqnzu yarinyar zata dinga tutiya da jin ita asma'u da kanta ta rakota gidanta kenan,sai data kusa tsinkewa sannan ya daga
Qoqarin controlling fushinta tayi don kada qilu ta jawo bau,duk zafin kantabtasan inda take tasan halin hamid din sarai
"Haba hamid....ya zaka yimin haka don Allah fisabilillahi....?"
"Lafiya?....keda wa?"
Ya tambaya cikin halin ko in kula,tasan halin kayanta sarai,shariya da halin idont care
"Munbi motocin daukan aysha munyi zaton ni ka aikowa da su?"
"Ni na gaya miki naki ne?...." Shuru ta danyi sannan tace
"Yanayin abunne nayi zaton nawa ne"

"Ni na gaya miki naki ne?...." Shuru ta danyi sannan tace
"Yanayin abunne nayi zaton nawa ne"
"Amma ai already na gaya miki cewa motoci biyu xan kawo,kuma da sunzo din xan kira ki na sanar miki ko?"
"Habba dear ka rufamin asiri don Allah...motoci biyu kaman za'a rakiyar kaza....ai ba girma na bane...kaga motocin rakiyar aysha ne?"
"Ke bana son rainin wayo malama....haka nakeso haka na tsara...bana son hayaniya da hauka aje a batawa mutum waje ba'asan nawa ka kashe ba...ni xaki hada da muhammad mai goro?" Ya qarashe maganar ta sigar tambaya wanda bata fahimci me yake nufi ba
"Am sorry" ta fada a sanyaye
"If kina son zaman lafiya da kwanciyar hankali kibi dokata,ban kuma lamince a qara wata motar kan wadda nace ba" daga haka ya kashe kiran,shuru kawai tayi tana duban su nusaiba dake tsaye gabanta,duk yadda taso ta daure saida kuka ya qwace mata,hamid yana son ruguza ta da gadar mata da abun kunya kuma abun fada,ta yaya za'ayi rakiyarta da mota biyu kacal,anty halima ce ta qaraso wajen tana tambayar meke faruwa

,bata iya bata amsa ba sai hannunta data kama suka shige motar anty haliman suka tada ta,tilas saura suka sake hawa motocin da aka kawosu akayi jigilar maidasu.
Tun cikin mota ta dinga jin ta muzanta,duk da cewa ba wadda ta sake ce mata komai amma saitaji a karan kanta ta tsargu da kanta,ba abinda ke mata yawo cikin idanu da kwanya irin gidan aysha,ita kanta ta tabbatar da cewa khalipha ya yayiwa hamid fintikau ya tsere masa,tako ina WUTSIYAR RAQUMI tayi nesa da qasa(daya daga cikin littafan zafafa biyar na billyn abdul),yau BURI DAYA (zafafa biyar mamuhghee)da take da shi ya cika,saidai ta raina cikar burin nata,ashe abinda take hangowa akwai sama da haka?ta yaya akai haka ta faru?,inama ace zata samu SAUYIN QADDARA(zafafa biyar na hafsat rano). Sai takwas na dare sannan ya kirata ya sanar mata zuwan motocin,anty safiyya ce ta fita sai gata ta dawo ta dubi mummy
"Sai a zabi wadanda zasu je kaita"
"Kamar yaya....kowa zaije kamar yadda aka je na indo"
"Da motoci biyun?" Anty safiyya ta fada

tsantsar bacin ran dake fuskarta na nunawa,duk da qoqarin danneshi da take
"Motoci biyu?...motoci biyu kuma?" Mummy ta tambaya tana yatsine fuska
"Ki aika a gano miki" anty safiyya ta fada tana cire mayafinta ta wuce bandaki,don ita bata jin zata ma iya zuwa.

Kai tsaye dakin asma'u mummy ta wuce tana tambayarta zancan motoci biyu da aka ce,ta tabbatar mata haka ne,nan mummy ta hau masifa tana fadin idan ma qyashin bada motocin suke su zasu bada wadanda zasu isa
"Mummy.....kiyi haquri kawai don yace baya buqatar mota sama da biyu",wannan batun shi ya tunzura mumnyn,tana ganin kawai hamid ya shirya wulaqanta su ne,ta taya har aisha zata fisu yawan 'yan rakiya da ababen hawa?,ganin yadda mummyn ta hau sosai taqi sauka daga qudurinta na qara motoci,sannan ita ta sani idan haka ta kasance komai zai iya faruwa,saboda haka tayi hanzarin kiran daddy ta gaya masa komai,kashe wayar yayi ba tare daya ce komai ba ya nemi mummyn da kanshi ya bata umarnin ta bada yarinya a tafi kaita,a hadata da manya mutum uku

qawayenta mutum uku,baya son qorafi baya son kuma ya qarajin wani abu ya biyo baya,tasan daddyn har yau na ciki da ita kan maganar aysha,tilas ta haqura,aka dauki yayarta daya yayar daddy daya,qawayenta biyu,qawayen asma'un biyu,abun mamakin shine sanda suka fita da amaryar akwai motoci kusan guda takwas,saidai biyu ne kawai nasu saura dangin hamid ne mata,wanda a qa'ida su zasu shiga su fito da amarya amma suka qame cikin mota ba wadda ta tako waje har aka saka asma'un cikin motar aka soma tafiya.

Qarfe tara na dare ayarin motocinsu khalipha da abokanshi suka shigo gidan,daga inda take zaune tana iya jiyo qararsu da maganganu sama sama,duka duka ba'a fi mintuna goma sha biyar ba taji motocin sun sama ficewa daga gidan,cikar mintuna ashirin taji dif alamun babu kowa a harabar gidan.

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*KO KUMA*

07067124863

*DB*

30

Annin na xaune saman kujerun falon tana nunawa magajiya da larai masu aikinta guraren dake buqatar gyaran,ko kadan bata iya zama cikin qazanta duk taron da akayi sai taga gidan ya daidaita take samun sukuni,amal ce ta ukunsu tare suke gyaran falon,duk da cewa dauriya ce kawai take nunawa,ita kadai tasan ya take ji cikin zuciyarta,tana amfani da shawarar sayyada ne kawai qawa a gareta,yau khalipha yayi aure ya auri wata ba ita ba?.

Sallamarshi ta sanya anni daga kai cikin mamaki tana amsawa idanunta a kansu,tun kafin ta qaraso jikinta ya bata ayshan ce,amal dake duqe tana goge glass din center table ta dago da hanzari jin muryarshi tana binsa da kallo itama,gabanta yayi mummunar faduwa ganin mace biye da shi,sai tayi sauri ta koma taci gaba da aikinta,saidai rabin hankalinta da dukkan kunnenta na inda suke.

Miqewa annin tayi har suka iso inda take,ta kama hannunta tana yunqurin zaunar da ita saman kujera,qasan carfet ayshan ta sulale ta zauna,da sauri anni tace
"A'ah...tashi mana,ya zaki zauna a qasa?" Bata damu da wannan ba ta soma gaida annin cike da tsantsar nutsuwa,har a sannan bata bude fuskarta ba bate annin ta ganta,cikin kulawa anni ta amsa sannan ta maida kallonta kan khalipha dake zaune dai dai saman kujera,gajiyar da yayi na bayyana qarara
"Lafiya khalipha,me ya fito daku cikin wannan daren?" Yan aikin dake falon ya kalla sannan yayi gyaran murya,jiyowa sukayi suna dubanshi ya musu inkiya da su wuce,duka suka fice daga falon har amal wadda ta aje duster din hannunta ta haura saman anni,saidai kasa wucewa tayi ta tsaya daga can step din qarshe yadda zata iya jin duk abinda ke faruwa daga parlour din.

"Ta zabi zama a nan anni"shiru annin tayi tana duban ayshan cike da mamakin yadda taqi nata gidan ta zabi zama tare da su,sannan ta daga kai ta dubi khalipha
"Anya khalipha....ita da kanta ta zabi haka?"
"Gata nan anni ki tambayeta,Allah bani nace ba..." Ya fada yana dan bata fuska alamun da gaske yake
"Aysha....yaya zaki qi gidan da akayi donminki?..." Shuru ayshan tayi,tana kunya da nauyin annin duk da bata taba ganinta ba
"Shikenan kuje ku huta...zuwa safiya saimu gaisa tunda naga diyar tawa kunyata take ji" ta fada tana murmushi,harga Allah taji dadin hakan,kodon zaman kadaici da yadda takeson ayshan ta dauketa kamar mahaifiya ta kuma saba da ita,daya daga cikin masu aikin ta kira tace takai ayshan wani dako a bata duk abinda take buqata,a nutse ayshan ta tashi tabi bayanta tabar khaliphan da annin a falo.

"Khalipha anya kuwa babu takura ga yarinyar nan?"
"Ina shiga gidan abinda tace min kenan anni"
"Shikenan saida safe ma tattauna,jeka kaima ka huta nima tashi zanyi" amsa mata yayi sannan ya miqe yana ficewa daga falon,shima burinsa kawai ya samu waje ya huta,don har yanzu ciwon kan bai sake shi ba.

A sanyaye ta juya tabar wajen zuwa dakin anni dake sama hawaye nabin kuncinta,kenan a gidan matar khakiohan zata zauna?,anya kuwa zata iya ci gaba da zama da su?,anya ko burinta zai cika?,da wannan tambayoyin amal ta qarasa dakin ta samu waje ta zauna tana qoqarin controlling hawayenta.

Yana shiga dakin kayan jikinsa kawai ya fidda ya shige toilet,haka ya sakarwa kansa ruwa idanunshi na rufe ruwan na kwaranya tun daga saman kashi zuwa qafafunshi,sanyin ruwan na ratsashi yana masa dadi a jiki saboda zafin da ake dan tabawa kwana biyu,sai a sannan ya soma jin qwaqwalwarsa na komawa kan saitinta,nauyin daya dinga ji saman kanshi da qirjinsa na sauka,nutsuwa ta soma ratsashi,ya jima sosai qasan shower din sannan ya fito ya tsane jikinsa ya sauya kaya kawai yabi lafiyar gado,don hatta shafa'i da wuturin ma ya kasa yi yau,hannunshi saman kanshi yana shafawa kadan kadan,yana son hana kanshi yin kowanne tunani burinsa kawai bacci yayi awon gaba da shi.
Chapter 52 · 0% Book details