← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 114

Sashe 75

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saman doguwar kujera ta miqe abinta ta dora system din saman cinyarta ta kunnata,saida komai ya daidaita ta lalubo film din ta soma kalla,sosai hankalinta ta tafi kan film din dalili daya sanya bataji takun shigowarsa ba,ya hangi bayanta,saiya wuce bedroom din.

Tsayawa yayi yana kallon kayan data shirya din,komai a tsare daga gani kasan tasan me takeyi,a qa'idarshi bai tafiya da kaya idan tafiya ta sameshi amma wannan karon sai yaji bazai iya ignoring ba,maida jakar yayi ya zuge yana murmushi sannan ya sake dawowa falon.

A hankali ya taka ya tsaya a bayanta hannayenshi harde kamar yadda al'adar tsaiwarshi take,ya zubawa screen din system din ido yana kallon abinda take kallo daya dauke mata hankali haka,murmushi take saki lokaci lokaci saboda yadda film din ya tafi da ita,soyayya ce ake bugata sosai,ta tuna sanda hanan ke bata labarin film din,a sannan kallon shirme takewa hanan din da batawa kai lokaci,wani irin feeling naso da qauna taji yana shiha zuciyarta,yadda jaruman ciki ke tafi da soyayyarsu mai ratsa zuciyar masoya ce.

Miqa tayi tana ware hannayenta gami da fidda murmushi daga fuskarta sanda aka gama wani sin wanda hakan yasa ta dunguri khalipha dake tsaye a bayanta shima yana tayata kallon ba tare data sani ba,da hanzari ta waiwayo suka hada idanu,yadda ta ganshi a tsaye tasan ya jima a wajen,gabanta ya fadi kunya ta kamata,yanzu haka duk yaga yadda take appreciating film din,Allah ya rufa mata asiri ba wani film din banza take kalla ba,waskewa tayi tana tsaida film din tana son rufr system din,hannayensa ya saki yana zagayowa inda take,shi kansa film din yaji yana taba wani sashe na zuciyarsa,zai iya cewa tun wancan lokacin daya shude zuciyarsa ke a rufe,bai taba bada qofa ga wata ba bare yaji me ake ji koya dan dana irin abinda masu soyayya ke dan danawa,hannayensa yasa zai gyara qafafunta dake miqe don ya samu wajen zama,santala santalan qaurinta yabi da kallo wanda,cikin sauri ta tanqwashe qafarta tana dan hade rai,baice komai ba ya sanya hannunshi ya ya dauki system din ya janyo qaramin tebur gabansu ya aje samanta ya dannan play film din yaci gaba dayi,ji take ba zata iya zama su kalli film din tare ba,duk da bana badala bane amma soyayya ciki mai zafi ce akwai kunya,tana jin nauyinsa sosai saboda haka ta miqe da sauri,caraf ya kama tsintsiyar hannunta ya janyota baya wanda hakan yasa ta koma da baya ta zquna ba tare data shirya ba,har zaman datayi yafi na dazu kawo kusanci a tsakaninsu
"Zauna ki kalla abinki,ni tayaki kawai zanyi" ba yadda ta iya saboda yadda ya dabibayeta da idanunsa ta zauna din,tun tana a takure harta dan saki kadan fim din yaci gaba da garawa,ji tayi ba zata iya daurewa ba abun ya mata nauyi da yawa aka,ga zamanshi a gefanta dake qara raurawa zuciyarta,haka kawai zuciyarta taji kamar zata narke,saita rarumi system din ta soma yunqurin kasheta gaba days,a hankali ya dora hannunshi saman nata,dagowa tayi tana kallon qwayar idanunshi karo na farko,wani irin kallo yake binta dashi kamar wanda ke jin bacci,manyan idanunshi nan sun rusuna sun rage girma,wani abu taji yabtsirga mata saita soma yunqurin zame hannunta ta gudu tabar masa system din ma gaba daya amma yaqi bata space din yin hakan
"Kinsan me?" Ya fada cikin sanyi da taushi
"Indai kaga mutum na yawan kallon fina finan soyayya to aure yakeso" idanunta ta zare tana dubanshi,aure kaman yaya?,me yake nufi xai fassarata?
"Yaushe kika soma kalla humairaaa?" Ya kira sunanta da wani irin tune wanda ya qarawa zuciyarta bugu,saita kasa daurewa taci gaba da yunqurin zame hannunta amma duka a banza,tafin hannunshinya saka cikin nata yana murzawa a hankali yana ji cikin jikinsa kamar zai fita da control dinsa amma ya kasa tsaida kanshi,shi kansa baisan me yakeji haka cikin jiki da zuciyarsa ba
"Uhmm...tell me mana"
"Pls ya khalipha...ka sakarmin hannu" ta fada a narke kaman mai shirin sakin kuka,saidai kasalar daya saukar mata ya sanyata fidda sautin cikin wannan yanayin.

Sautin kidan da wayarshi ya dauka shiya dawo dashi,ya zame hannunshi daga nata a hankali ya soma laluben wayar,hakan ya bata damar miqewa ta fice daga falon zuwa dako cikin gudu gudu sauri sauri,binta yayi da kallo ta koma kamar qaramin yaron da aka biyo yakeson ya cimma mamanshi ya buya bayanta,mahmoud ne ke kiransa,sallama yayi bayan ya daga wayar
"Kana ina miscal kusan uku?"
"Da yaushe kenan?"
"Yanzu mana wannan ne kira na hudu dana yi maka fa" cikin mamaki ya daga wayar daga kunnenshi ya kalli screen din,tabbas ga alamun miscal nan ya nuna amma saiya dake
"To nidai banji ba"
"Kacemin kawai kana angonci,tunda ka dawo ba wanda yaji motsinka daga company" kalmar angoncin ita ta sashi sakin sihirtaccen murmushi,yana son yayi nazqri akanta amma surutun mahmoud ya hana,hakanan ya biye mishi suka tattauna maganganun dq zqsu tattauna,daga qarshe ya buqaci ko zai shigo company
"A'ah fa,gobe zanje legos"
"Kayi me a can?"
"Nida humairaaa ne"
"Honeymoon?" Ya tambaya cikin shaqiyanci
"Laifi ne?"
"Ko kadan na wajena,amma legos inaga ta muku kadan fa,ka manta tsohon tuzuru ne kai daya ga 'yammata kala kala?" Ya fadi cikin tsokana,dariya taso kubce masa ya danne abarsa,shi sam baima kai can inda mahmoud din yakai ba ko kadan a ransa
"Kaga sai da safe"
"A miqamin gaisuwa" bai saurareshi ba ya yanke kiran abinsa yana murmushi,yana juya maganar da sukayi da mahmoud,haka ya dinga juya maganar cikin ransa kamar dai tana so tayi masa tasiri,a nutse ya janyo system din tata zai kashe mata,babban hoton haidar ne aka screen din,cikin shigar qananun kaya,yayi kyau sosai suna diban kaman dashi qwarai fiye da mus'ab,haka kota fannin halayya,saiya tsaya yana duban hoton,tsaki ua danja,sai ya juya bayan system yaga irin ta haidar dince sak,tsaki yadanja wanda baisan dalilinsa ba,kasheta yayi ya hada da charger din ya nufi study room dinshi da ita ya ajeta a can.

Tunda ta shiga dakin take kwance rub da ciki saman gado a side din da yake kaman nata ne nan take kwanciya shi kuma daya side din tun sanda ya tasota daga falo ta dawo ciki,a hankali komai ke dawo mata cikin qwalqwalwarta,wani yanayi da batasan na neye ba yana bin jiki jini da zuciyarta,ta jima a haka kafin ta gyara kwanciyarta ta juyar da fuskarta daya sashen,hoton fuskar khalipha ta soma yi mata yawo,manyan idanunshi masu kyau da haske,kwantancen sajen fuskarshi daya zagaye haba zuwa qasan hancinsa,dogon hancinsa mai dan tudu kadan,pink din labbansa suma masu tudu kadan,cikakken gashin gira daya sake qawata fuskarshi da zara zaran eyelashes,fararen haqora,saita cure waje daya tana jin kunya na kamata,cusa kanta tayi cikin filo tana tuhunar kanta me ya kaita fasalta siffar da namiji idan ba rashin ta ido ba,murmushi ya qwace mata tana sake cusa kanta tsakanin filalluka,ita daya kamar wadda za'a kama.

41

Qarfe goma na safe suna tsaye harabar farfajiyar gidan,motoci hudu ne kowacce da drivernta suna jiran fitowar boss khalipha,daga ciki aysha ce tsaye zaune gaban anni riqe da kofin kunu mai dumi da qosai wanda tunda safe su atika suka shiga kitchen sukayishi da umarnin annin,ta tsare ayshan tana sha
"Maza ki shanye wannan na haunnunki,ayi tafiya ciki babu komai,zaki biyema wancan mai tsarin da abincin safe sai hantsi ya dubi ludayi" ta fadi tana duban ayshan cikin so qauna da tausayi,tana mata fatan wannan karon sauran matsalarta ta kawo qarshe,tana mata fata yau ta kasance cikin farinciki,ta tabbata batasan inda zasu ba da tuni zuwa yanzu hankalinta na a tashe ne,murmushi ayshan tayi ta dire cup din hannunta wanda ta tilastawa kanta ta shanye din kodom farincikin anni
"Yauwa koke fa" anni ta fada tana jin dadin yadda ta cika cikinta
"Na gode anni" ta fada kanta a qasa,tana qoqarin danne raunin xuciyarta,haka kawai umminta ta fado mata,kulawar data samu wajen anni a iya dan zaman da sukayi da ita bata taba ganin kwatankwacinta ba daga wajen umminta,ta lura sa sauyawar fuskar ayshan,batason ta fuskanci komai ko yanayinta ya sauya tun yanzu

hakan ya sanya tayi nufin bagarar da zancan
"Ayshatu sarkin godiya" murmushi suka saki a tare,sai shuru yadan ratsa falon,cikin haka takun takalman khalipha suka soma ratso falon,a hankali ta daga kai da niyyar satar kallonshi caraf ya kamata,tayi qoqarin dauke idonta daga kanshi amma kamar ya riqeta ne da wani mayen qarfe,yayi wani mugun kyau cikin suits kamar yadda suka zama sune kusan rabi da rabin rabin shigarsa,komai nashi daban yake cikin gayu tsafta da nutsuwa,da qyar ta qwaci ganinta ta dauke kanta.

Gaisawa sukayi da anni ya dora da tambayar lafiyarta,suna tsaka da haka rahama ta shigo parlour din dauke da kofunan tangaran biyu a hannunta qananu
"Ya khalipha ga coffe" ta fada cikin salo tana miqa mishi bayan ta zauna dab da aysha tana sin tantance rigar dake jikin ayshan,ayshan ce ta amsa takai hancinta ta shanshana,saita yamutsa fuska kadan tana dubanshi
"Zaka sha ne?" Tayi tambayar tana dan takure fuska da hancinta,saiya kashe mata idonshi daya sannan ya mata nuni da a'a,hakan ba qaramin dadi ya yiwa aysha ba,saita waiwaya tana duban rahama
"Sorry anty rahama,ya qoshi" ts fada qasa qasa ta yadda anni bata ankare ma da abinda ke faruwan ba,ba qaramin shaqa rahaman tayi ba,uwa uba kiranta anti da ayshan tayi,eh ta girmeta don sa'ar khaliphan ce,amma babu abinda ta tsana a duniya irin a qara mata shekaru ko a bayyana shekarun nata a duniya,mamaki take cikin ranta na yadda ayshan keyi a ayanzu,kishinta fiye dana baya ya cika ranta,bata taba tsammamin yarinyat xata iya canzawa haka lokaci guda ba kuma cikin qanqanin lokaci ba tare data cimma burinta ba.

Anni da khalipha na gaba aysha na baya ita da rahama data shirya wai zasu sauketa a asibiti tana son taga likita,tsaf ta karanci rahaman amma ta qyaleta don tasan meta taka,tunda tasan rahaman bata taba yarda ta fita ba mota ba,kuma koda motar ma ita tafi ganewa tayi driving da kanta,daga valcony anni ta tsaya tana musu Allah ta kiyaye ta koma ciki abinta su kuma sukayo gaba.
Chapter 75 · 0% Book details