Sashe 83
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fadin irin tashin hankalin ma da suka shiga bata baki ne,hankalin khalipha ya kuma tashi sanda ya koma dakin ya iske hajar riqe da cikinta tana faman kuka annin na riqeta,idanunta kan khalipha,tsananin tashin hankali yasa ya kasa qarasowa,yana jin sautin kukanta a kunnensa ya fice daga asibitin,duk inda ya samu kawai jefa qafarsa yake,tunani yake ina zai samu kudin nan da awa goma sha?,abinda bai taba ba a ranar shi yayi wato roqo,saidai ba wani abun azo a samu ba ya samu har dare ya soma tsalawa,kawai sai ya siyi abinda su anni dasu haidar zasu iyaci ya koma asibitin,ai kuwa suna zaune waje daya yunwa ta addabi kowa,hajar kuwa barci ya kwasheta,haka ya bude musu suka rufu suka cinye tas,yacewa anni zai wuce gida gobe zai dawo da kudin da yardar Allah,dubanshi kawai take tana kallonshi,har yau khalipha da sauranshi game da halayyar mutanen duniya,wadanda basusan taimako ba,wadanda basu san kowa ba sai kansu,basu damu da damuwar kowa ba sai tasu,son kawunanmu yayi mana yawa,idan dai kai daya zaka rayu to ba matsalarka bace kowa ma ya mutu,idan dai kai daya zaka tsira ba matsalarka bace kowa ya cutu,har kullum kowa burinsa yaga komai nashi yana tafiya masa daidai ba ruwanka da halin da dan uwanka zai shiga sanadiyyar wani abu daka aikata masa,bata sace masa gwiwa ba,ta bishi da fatan alkhairi,ya fice zuciyarsa cike fal da tausayin mahaifiyarsa kamar yadda itama tata zuciyar cike da tausayinta da qannenshi,a qafa ya daba har gida ya shige ciki ya kwanta,saidai cikin wannan daren duk iya satar bacci bai samu nasarar daukeshi ba,duk juyin da zaiyi anni da hajar dasu haidar be cikin ranshi,cikin daren ya yankewa kanshi dole ya dangana da wajen kawun nan nashi,yana kyautata zaton a wannan karon zasu dubi halin da hajar din ke ciki su tausaya musu.
Asubar fari bayan ya idar da sallah daga masallaci ya zarce gidan kawu hamza,duk da halin da suke ciki bai taba yarda sallah asuba ta kubce masa cikin jam'i ba,sanda ya ganshi fada ya soma balbaleshi da shi kafin ya saurara yaji abinda ke tafe dashi,sai daya gama tsaf sannan yace dashi
"To nidai yanzu bani da abinda zan baku ko qwandala kuwa,saboda nima kudin makarantar yara da zan biya nake nema,tunda yanzu babu maiyi mana dole na tashi ka nema da kaina" hakanan ya fito jiki ba qwari ya tunkari gidan kawu munzali,kawu habibu,kawu saminu
"Tabdi,amma bansan baka da hankali ba yaro sai yau,yanzu wake neman kudi wajen jama'a kowa tashi ta isheshi?"
"Ni ta kayqn sallar yara na nake,dama mahaifinka kedan tabukawa yanzu ko babu shi kaga dole mu tsaya mu share musu hawaye a madadinsa"
"Motar maryam ta lalace wata takeso na sauya mata,saidai ka jira nan da qarshen wani watan ina bin wani maqofcina akasuwa bashi ya yimin alqawarin zai bani,sai kazo ko rabi ne na bayar"
"Tashi ka bani waje,kun gama diga mana rashin mutunci wato sai yanxu kuka san damu" wannan shine ire iren kalaman daya gamu dasu a dukka gidajen,gida na qarshe daya je shine gidan kawu idris,bai taba tunanin zuwan ba amma zuciyarshi ta bashi qwarin gwiwar zuwan.
A falon gidan ya taddashi zaune shida ibrahim suna lissafin kudi,yana ganinsa ya miqe tsaye cikin hayagaga da hargowa
"Ubanka kazo yimin cikin gida?"kai ya girgixa masa
"ohhhh,uwar kace kenan ta sake turoka kazo ka qarashe cin mutuncin da baka gama yimin ba kenan ko?"
"Ba haka bane kawu kayi haquri,hajar ce a asibiti bata da lafiya sosai za'a yi mata aiki,to kudin aikin da suka fada din bamu dasu....."
"Shine kazo gamai indararo mai aikin banza ko,Allah yana bani ina watsarwa" ya fada yana ware hannayensa kamar mai shirin yin daquwa
"A'ah kawu,ka taimaka wallahi tana matuqar buqatar taimako tana jin jiki sosai kawu,ko bashi ne ka bani nizan biyaka daga biya in sha Allahu"
"Kaga kudaden nan?" Ya fada yana nuna daurin kudin dake gabanshi,har zuciyar khalipha ta soma sanyi ya gyada kai,sai ta jefeshi da mummunan furucin da har yau idan ya tuna sai yaji tsanarsa
"To ko ubanka dake kabari ne zai fito bai isa in bashi kudin nan ba,koshi yayi kadan ballantana kai,hajar kuwa tama mutu mana asara ta ce?,kai gwara ta mutu ma mun rage iri mun huta aurarwa" daga jajayen idanun sa khalipha yayi ya zubawa kawu su,wanda shi kansa sai daya tsorata da sauyawar da yayi lokaci daya,ji yayi idan ya qara minti daya a gidan zai iya mutuwa,ji yayi kamar kawun ya yuwa hajar baki mutuwar zatayi,tamkar iskar guguwa ya miqe ya fice wanda badan ibrahim yayi saurin matsawa ba tafiyar yaaji zaiyi dashi.
Yana fita yaci karo da motar kawun sanuwa wadda cikin gadonsu da suka wawashe suka kasafta ya siya,idamunshi suka sauka kan wani qaton dutse dake girke a gefe,baiyi wata wata ba ya cirashi yabi dukka gilasan motar ya fashesu tas ya kuma lallotseta ya qara gaba.
Asibitin kawai ya nufa don yaga halin da suke ciki,tun daga harabar asibitin yaji haka kawai gabanshi ya yanke ya fadi,qafafunsa sunyi sanyi,haka ya dinga takawa har dakin da aka kwantar da hajar.
Anni na tsugune gaban wani abu dake shimfide a gabansu,gefa haidar da mus'ab kowanne cikinsu kuka yake banda anni data zubawa abin ido,take qwaqwalwarsa ta gaya masa hajar ce ta tafi,haka ya dinga takowa kamar gunki yayi tsaye a kansu anni,sai a sannan ta lura da zuwanshi
"Yauwa khalipha,kamata mu tafi,hajar ta tafi ta huta,kaga hadonma har an dora wani a kai" anni ta fada tana miqewa tsaye,kallo daya yayi mata ya fuskanci ba cikin hayyacinta itama take ba,duk da bala'in da yayi masa yawa haka ya dinga kiran sunan Allah ya sami nutsuwar daya juya ya samo abun hawa suka sanya gawar hajar badon yana da kudin da zai biya mai taxin ba,cikinsu ba wanda yake cewa da danuwansa wani abu sai haidar da mus'ab dake faman kuka,annin ce ke yawan ce musu
"Ku daina kuka,hajar hutawa tayi", bayan mai motar ya saukesu ya buqaci kudinsa,sai a sannan ya tuna baida ko sisi
"kayi haquri bamu da abun biyanka,kayi haquri nayi kuskure daban gaya maka ba tun wuri"
"Babu komai....Allah ya jiqan rai yasa ya huta"daga kai khalipha yayi ya dubeshi,don baizaci jin haka daga bakinsa ba,ya shirya yaji jafa'i da alkaba'i daga bakinsa kaman yadda sauran mutane suke,cikin mamaki ya amsa ya dinga jera masa godiya,dama har yanzu akwai sauran mutane masu imani a duniya?,akwai mutane masu tausayi?
('Yan uwa ku duba halin da khalipha suke ciki,wallahi azim acikin al'ummarmu akwai mutane kwatankwacinsu sunfi dubu,wallahi wallahi muji tsoron Allah,mu tallafi marayu,muji tsoron haduwarmu da ubangiji,muji tsoro randa zamu tashi Allah ya tambayemu ya kayi da haqqin wane maqocinka ko makusancinka mu rasa amsar da zamu bawa ubangijinmu).
*DAURIN BOYE*
45
Haka khalipha yaje masallacin unguwar ya fada,aka hadu aka yiwa hajar sallah aka kaita gidanta na gaskiya,sai a sannan anni tayi kuka,irin kukan da tunda suka shiga wannan halin bata taba yarda tayi gaban yaranta ba saboda karta karya musu gwiwa,daya daga cikin aninda ya hadarwa khalipha kenan ciwon kanshi ya tashi,yayi jinya sosai,Allah ya taqaita musu wahala ya warke ba tare da an dauki dogon lokaci ba.
A wannan karon anni bata yarda ta sake zama haka ba,domin tana tsoron faruwar abinda ya faru a baya,sana'a ta kama wanda duka dai bai wuce wankau ba,abinka da bata saba duk,sanda tayin sai hannunta sun kumbura suyita ciwo,amma gobe haka zata sake yin wani,tun suna kumbura har suka daina,daga bisani ta samu aikatau na shara da wanke wanke a wani gida dake bayansu,aikine mai shegen yawa,duk randa taje ta dawo zaiyi wuya bata kwana sa zazzabi ba sabida yawan aikin da take tilliqa,gashi dama tunda hajar ta rasu bata qara lafiya ba,khalipha shi ya hanata zuwa saboda yanayin lafiyarta,haka ta haqura taci gaba da wankau da sauran sana'o'in hannu.
To tunda hajar ta mutu anni batayi cikakkiyar lafiya ba,sannu sannu sai ciwo itama ya kwantar da ita,hankalin khalipha yayi mugun tashi tamkar zai zauce,yana ganin kamar zasu rasa annin ne kamar yadda suka rasa hajar dinsu,suka shiga sintirin asibiti duk da basu dako sisi,hawan jini ne yayi mata mummunan kamu ya haifar mata da matsalar qoda,wanda tana buqatar ayi mata aiki,wanda indai akayi mata akan lokaci shikenan zata warke sumul kamar bata taba yiba,amma matuqar aka jinkirta tofa la shakka ciwon zai girmama ne ya zame mata wani abu na daban.
Shawara ta qarshe da khalipha ya yankewa kanshi shine su saida gidan da suke ciki abiya maqudan kudaden aikin,tunda yana da yaqinin idan ba hakan sukayi ba saidai annin ta mutu ta barsu kamar yadda hajar tayi.
Akan hanyarsa ta zuwa neman dillalan da zasu sayi gidansu ne ya tsinci jakar kudin daddy har ya zama sila na biyan kudin aikin anni,zuwan ibrahim kuwa da 'yan sanda kawu idris yaji labarin saida gidan ne,so yayi ya qullawa khalipha sharrin da za'a kaishi birsin,shi kuma ya samu damar saida gidan ya kora anni daga ciki.
Bayan samun lafiyar anni khalipha bai fasa saida gidan ba bisa shawarar anni,saboda babban abinda hankalinta ya karkatu akai shine ya samu ya koma karatu,saboda shine gatan duk wani dan adam,Allah ya taimakeshi sukayi masa tayi mai kyau suka karbi kudin,qaramin gida suka sami wanda daki daya ne ciki da falo da bandaki,sai dan mitsitsin tsakar gida suka siya,sai wani dakin a soro,sauran kudin kuwa suka cire wanda zasu fara sana'a dashi sannan ya musu duk wani kai kawon makaranta a ciki,gaba dayansu makarantun gwamnati suka koma,cikin qanqanin lokaci al'amuran suka soma dan daidaita,tunda a qalla suna da abincin da zasuci susha,sun dan sauya suturu ga makaranta sun koma islamiyya da boko,sannan anni na sana'o'inta sosao wanda Allah ya dubi maraicinsu ya soma sawa abun albarka.
Zuwan khalipha makarantar cikin qanqanin lokaci yayi suna yayi fice,sakamakon tarin baiwa da basirar da Allah ya bashi,bugu da qari kuma ya samu background mai kyau don makarantar da yayi a baya duka ba qananun makarantu bane,qoqarinsa har ya wuce tunani,sai aka kaishi ss3 kawai,don sunce da akwai ajin gaba dahaka ma can zasu kaishi.
Asubar fari bayan ya idar da sallah daga masallaci ya zarce gidan kawu hamza,duk da halin da suke ciki bai taba yarda sallah asuba ta kubce masa cikin jam'i ba,sanda ya ganshi fada ya soma balbaleshi da shi kafin ya saurara yaji abinda ke tafe dashi,sai daya gama tsaf sannan yace dashi
"To nidai yanzu bani da abinda zan baku ko qwandala kuwa,saboda nima kudin makarantar yara da zan biya nake nema,tunda yanzu babu maiyi mana dole na tashi ka nema da kaina" hakanan ya fito jiki ba qwari ya tunkari gidan kawu munzali,kawu habibu,kawu saminu
"Tabdi,amma bansan baka da hankali ba yaro sai yau,yanzu wake neman kudi wajen jama'a kowa tashi ta isheshi?"
"Ni ta kayqn sallar yara na nake,dama mahaifinka kedan tabukawa yanzu ko babu shi kaga dole mu tsaya mu share musu hawaye a madadinsa"
"Motar maryam ta lalace wata takeso na sauya mata,saidai ka jira nan da qarshen wani watan ina bin wani maqofcina akasuwa bashi ya yimin alqawarin zai bani,sai kazo ko rabi ne na bayar"
"Tashi ka bani waje,kun gama diga mana rashin mutunci wato sai yanxu kuka san damu" wannan shine ire iren kalaman daya gamu dasu a dukka gidajen,gida na qarshe daya je shine gidan kawu idris,bai taba tunanin zuwan ba amma zuciyarshi ta bashi qwarin gwiwar zuwan.
A falon gidan ya taddashi zaune shida ibrahim suna lissafin kudi,yana ganinsa ya miqe tsaye cikin hayagaga da hargowa
"Ubanka kazo yimin cikin gida?"kai ya girgixa masa
"ohhhh,uwar kace kenan ta sake turoka kazo ka qarashe cin mutuncin da baka gama yimin ba kenan ko?"
"Ba haka bane kawu kayi haquri,hajar ce a asibiti bata da lafiya sosai za'a yi mata aiki,to kudin aikin da suka fada din bamu dasu....."
"Shine kazo gamai indararo mai aikin banza ko,Allah yana bani ina watsarwa" ya fada yana ware hannayensa kamar mai shirin yin daquwa
"A'ah kawu,ka taimaka wallahi tana matuqar buqatar taimako tana jin jiki sosai kawu,ko bashi ne ka bani nizan biyaka daga biya in sha Allahu"
"Kaga kudaden nan?" Ya fada yana nuna daurin kudin dake gabanshi,har zuciyar khalipha ta soma sanyi ya gyada kai,sai ta jefeshi da mummunan furucin da har yau idan ya tuna sai yaji tsanarsa
"To ko ubanka dake kabari ne zai fito bai isa in bashi kudin nan ba,koshi yayi kadan ballantana kai,hajar kuwa tama mutu mana asara ta ce?,kai gwara ta mutu ma mun rage iri mun huta aurarwa" daga jajayen idanun sa khalipha yayi ya zubawa kawu su,wanda shi kansa sai daya tsorata da sauyawar da yayi lokaci daya,ji yayi idan ya qara minti daya a gidan zai iya mutuwa,ji yayi kamar kawun ya yuwa hajar baki mutuwar zatayi,tamkar iskar guguwa ya miqe ya fice wanda badan ibrahim yayi saurin matsawa ba tafiyar yaaji zaiyi dashi.
Yana fita yaci karo da motar kawun sanuwa wadda cikin gadonsu da suka wawashe suka kasafta ya siya,idamunshi suka sauka kan wani qaton dutse dake girke a gefe,baiyi wata wata ba ya cirashi yabi dukka gilasan motar ya fashesu tas ya kuma lallotseta ya qara gaba.
Asibitin kawai ya nufa don yaga halin da suke ciki,tun daga harabar asibitin yaji haka kawai gabanshi ya yanke ya fadi,qafafunsa sunyi sanyi,haka ya dinga takawa har dakin da aka kwantar da hajar.
Anni na tsugune gaban wani abu dake shimfide a gabansu,gefa haidar da mus'ab kowanne cikinsu kuka yake banda anni data zubawa abin ido,take qwaqwalwarsa ta gaya masa hajar ce ta tafi,haka ya dinga takowa kamar gunki yayi tsaye a kansu anni,sai a sannan ta lura da zuwanshi
"Yauwa khalipha,kamata mu tafi,hajar ta tafi ta huta,kaga hadonma har an dora wani a kai" anni ta fada tana miqewa tsaye,kallo daya yayi mata ya fuskanci ba cikin hayyacinta itama take ba,duk da bala'in da yayi masa yawa haka ya dinga kiran sunan Allah ya sami nutsuwar daya juya ya samo abun hawa suka sanya gawar hajar badon yana da kudin da zai biya mai taxin ba,cikinsu ba wanda yake cewa da danuwansa wani abu sai haidar da mus'ab dake faman kuka,annin ce ke yawan ce musu
"Ku daina kuka,hajar hutawa tayi", bayan mai motar ya saukesu ya buqaci kudinsa,sai a sannan ya tuna baida ko sisi
"kayi haquri bamu da abun biyanka,kayi haquri nayi kuskure daban gaya maka ba tun wuri"
"Babu komai....Allah ya jiqan rai yasa ya huta"daga kai khalipha yayi ya dubeshi,don baizaci jin haka daga bakinsa ba,ya shirya yaji jafa'i da alkaba'i daga bakinsa kaman yadda sauran mutane suke,cikin mamaki ya amsa ya dinga jera masa godiya,dama har yanzu akwai sauran mutane masu imani a duniya?,akwai mutane masu tausayi?
('Yan uwa ku duba halin da khalipha suke ciki,wallahi azim acikin al'ummarmu akwai mutane kwatankwacinsu sunfi dubu,wallahi wallahi muji tsoron Allah,mu tallafi marayu,muji tsoron haduwarmu da ubangiji,muji tsoro randa zamu tashi Allah ya tambayemu ya kayi da haqqin wane maqocinka ko makusancinka mu rasa amsar da zamu bawa ubangijinmu).
*DAURIN BOYE*
45
Haka khalipha yaje masallacin unguwar ya fada,aka hadu aka yiwa hajar sallah aka kaita gidanta na gaskiya,sai a sannan anni tayi kuka,irin kukan da tunda suka shiga wannan halin bata taba yarda tayi gaban yaranta ba saboda karta karya musu gwiwa,daya daga cikin aninda ya hadarwa khalipha kenan ciwon kanshi ya tashi,yayi jinya sosai,Allah ya taqaita musu wahala ya warke ba tare da an dauki dogon lokaci ba.
A wannan karon anni bata yarda ta sake zama haka ba,domin tana tsoron faruwar abinda ya faru a baya,sana'a ta kama wanda duka dai bai wuce wankau ba,abinka da bata saba duk,sanda tayin sai hannunta sun kumbura suyita ciwo,amma gobe haka zata sake yin wani,tun suna kumbura har suka daina,daga bisani ta samu aikatau na shara da wanke wanke a wani gida dake bayansu,aikine mai shegen yawa,duk randa taje ta dawo zaiyi wuya bata kwana sa zazzabi ba sabida yawan aikin da take tilliqa,gashi dama tunda hajar ta rasu bata qara lafiya ba,khalipha shi ya hanata zuwa saboda yanayin lafiyarta,haka ta haqura taci gaba da wankau da sauran sana'o'in hannu.
To tunda hajar ta mutu anni batayi cikakkiyar lafiya ba,sannu sannu sai ciwo itama ya kwantar da ita,hankalin khalipha yayi mugun tashi tamkar zai zauce,yana ganin kamar zasu rasa annin ne kamar yadda suka rasa hajar dinsu,suka shiga sintirin asibiti duk da basu dako sisi,hawan jini ne yayi mata mummunan kamu ya haifar mata da matsalar qoda,wanda tana buqatar ayi mata aiki,wanda indai akayi mata akan lokaci shikenan zata warke sumul kamar bata taba yiba,amma matuqar aka jinkirta tofa la shakka ciwon zai girmama ne ya zame mata wani abu na daban.
Shawara ta qarshe da khalipha ya yankewa kanshi shine su saida gidan da suke ciki abiya maqudan kudaden aikin,tunda yana da yaqinin idan ba hakan sukayi ba saidai annin ta mutu ta barsu kamar yadda hajar tayi.
Akan hanyarsa ta zuwa neman dillalan da zasu sayi gidansu ne ya tsinci jakar kudin daddy har ya zama sila na biyan kudin aikin anni,zuwan ibrahim kuwa da 'yan sanda kawu idris yaji labarin saida gidan ne,so yayi ya qullawa khalipha sharrin da za'a kaishi birsin,shi kuma ya samu damar saida gidan ya kora anni daga ciki.
Bayan samun lafiyar anni khalipha bai fasa saida gidan ba bisa shawarar anni,saboda babban abinda hankalinta ya karkatu akai shine ya samu ya koma karatu,saboda shine gatan duk wani dan adam,Allah ya taimakeshi sukayi masa tayi mai kyau suka karbi kudin,qaramin gida suka sami wanda daki daya ne ciki da falo da bandaki,sai dan mitsitsin tsakar gida suka siya,sai wani dakin a soro,sauran kudin kuwa suka cire wanda zasu fara sana'a dashi sannan ya musu duk wani kai kawon makaranta a ciki,gaba dayansu makarantun gwamnati suka koma,cikin qanqanin lokaci al'amuran suka soma dan daidaita,tunda a qalla suna da abincin da zasuci susha,sun dan sauya suturu ga makaranta sun koma islamiyya da boko,sannan anni na sana'o'inta sosao wanda Allah ya dubi maraicinsu ya soma sawa abun albarka.
Zuwan khalipha makarantar cikin qanqanin lokaci yayi suna yayi fice,sakamakon tarin baiwa da basirar da Allah ya bashi,bugu da qari kuma ya samu background mai kyau don makarantar da yayi a baya duka ba qananun makarantu bane,qoqarinsa har ya wuce tunani,sai aka kaishi ss3 kawai,don sunce da akwai ajin gaba dahaka ma can zasu kaishi.