← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 114

Sashe 12

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Hajiya laraba qawa ce ta qut da qut ta momy,saidai akwai banbancin halaye tsakaninsu,hajiya laraba macace mai kirki da mutunci qwarai da jan mutane a jiki,faran faran da rashin girman kai duk da arziqin da suke da shi,sanda ta isa da kayan ba qaramin murna ta nuna ba ta bubbuda tana cewa
"Kai ma sha Allah,wannan da gani aikin indo aisha ne ko?" Murmushi aysha tayi cikin jin kunya har fararen haqoranta na bayyana bata ce komai ba
"Sannunki da aiki,lallai hajiya sa'adatu na morar mai girki"
"Yauwa mama" ta amsa mata tana matsa yatsunta
"Gashi dukka su muslima tun shekaran jiya suka gudu gidan bikin suka barni a gidan saini kadai sai 'yan mazan,maza kuma kinsan ba zama suke ba,gidan babu dadi duk saini daya" ta fada sanda mai aikin mama ke aje mata kayan motsa baki,ruwa kawai ta zuba tasha tana sauraren maman data daga waya tana kiran yaronta,sai data gama wayar take dan jan ayshan da hira,bata da saurin sabo a wasu lokutan amma tayi qoqarin sakewa maman suna dan taba hira.

Sallamar matashin saurayin ce ta katse musu hirar da suke jefi jefi
"Banda abin ahmad kuma saika zauna,kasan amfani za'ayi da kayan,ka hanzarta don Allah ka miqa mata" ta fadi tana miqa masa muqullin mota bayan ta miqe ta nufi dakinta tana cewa
"Bari na baka wadan nan kudin ka kai mata,ni inajin sai wajen gobe zan samu shigowa qafar nan yau ta matsanta min" amsa mata yayi yana gyara zamanshi saman kujerar idanunsa kan aysha wadda ta gaidashi a sanyaye kamar yadda haka yanayinta yake,ya amsa mata yana tambayarta mommy,daga haka falon ya sake daukan shiru har mama ta fito ta sallameshi ya wuce.

Sam hanata tafiya maman tayi har sai data yi sallar isha'i ta kuma tilastata taci abinci,kyautar turare maman tayi mata da agogon hannu mai kyau kafimn su wuce,hannu biyu tasa ta karba tana mata godiya,hakanan aishatu ke burge maman saboda yanayin nutsuwarta da tarbiyyarta.

Suna gab da shiga unguwarsu wayarta ta soma ringing,da mamaki ta cirota daga jakarta tana duba mai kiran,saboda tasan bata da wani mai kiranta a irin wannan lokacin,bama wannan lokacin ba,da wuya ka zauna da ita kaji kira ya shigo wayarta,saboda bata da mai kiran nata bata da wanda ya damu da ita baya ga Aliya a cewarta,idan kaga kiran mommy kona asma'u cikin wayarta to qaruwarsu ce.

Ilai kuwa asma'un ke kiranta,tana shirin sallama saidai bata tsaya ta saurari sallamar ba bare ta amsa ta soma magana,da alamun bacin rai cikin muryarta
"Mommy tace min ta aikeki gidan mommy laraba,ki bar abinda kike ku sameni keda usama a meena event" qit ta kashe wayar daga haka,wayar aysha ta sauke daga kunnenta tana qoqarin maidawa cikin jakarta tace da usama
"Usama meena event center zamu je,kasan wajen?" Dariya ta bashi har ya dan murmusa cikin sautin murmushin nasa yace da ita
"Na sani mana aisha wanne dan kano ne baisan wajen ba....sai irinku kifin rijiya" itama murmusawar tayi,tana ganin meye hadinta da wajen me zata jeyi?,a yadda ma taji Aliya na fadin haduwar wajen tasan ba tsarar shigarta bane
"Amma me zamuyi a wajen?" Usama ya jeho mata tambayar
"Yaya asma'u tace muje,halan daukota zamuyi"
"Amma da motarta ta fita ai,me zamuyi a can"
"Ban sani ba nima usama" ta bashi amsa tana dan dafe kanta tare da maida kanta ga titi,ba ma'abociyar son doguwar magana bace sam,hakan yasa sau tari asma'u kan soketa da kalmar macijin sari ka noqe,taqi yarda har yau cewa a halittarta ne.

Ba wanda ya sake cewa komai har suka isa wajen taron,wajen adana motoci usama yayi parking sannan aysha ta soma kiciniyar kiran asma'u,jifa jifa tana bin wajen da kallo wanda yake da haske saidai ba tarwai ba,amma hakan bazai hanaka ganin yadda hadaddun maxa da mata ke kaikawo a wajen ba cikin ado da qawa.

Kusan sau biyar tana katsewa ba tare da asma'un ta dauka ba,sai ana shidan ta daga,shima kunnuwanta cike da kidan dake tashi daga cikin ainihim rufaffen dakin taron taje tsinto muryar asma'un
"Wai meye ne?" Abinda ta soma cewa kenan
"Muna wajen mun iso" tsaki ta doka
"Bana son qauyanci fa,daga zuwanku sai nabar abinda nake...ku jirani malama" daga haka kashe wayar,itama kashe tata wayar tayi sannan tace
"Ammm...usama tace muyi jiranta"
"To,bari na zaga nima nadan kama ruwa"
"Ba damuwa" ta furta tana bude data din wayarta,cikin qanqanin lokaci ta soma browsing tana duba abubuwa masu amfani dake da alaqa da karatunta.

Jira sukayi na tsahon awa biyu,har a sannan ba asma'u ba dalilinta
"Tayar motar nan kamar tayi faci aishatu,ko zaki fito na sauya wata kafin ta fito?"taji usama na fada saitin window din da take zaune
"Toh ba matsala"ta fadi tana maida wayarta jaka sannan ta bude murfin motar ta fito,idanunta ta sake sanyawa tana qarewa filin kallo,komawa tayi jikin motar ta jingina tana ci gaba da kallon wajen jifa jifa.

Cikin minti goma usama ya gama canza tayar yace ta koma ciki,amma sai tace ya barta anan saboda ta gaji da zaman cikin motar.

A gurguje yake takowa daga bangaren nasa zuwa bangaren anninsa,shigar baqaqen kaya yayi gaba daya har takalminsa hight top sai ratsin ja jifa jifa,agogon hannu yake daurawa hakan yasa sam bai lura da zeenart ba,qiris ya rage suyi gware,da sauri ya ja da baya yana ci gaba da daura agogonsa,yayin da zeenart ke qare masa kallo cike da sha'awa da burgewa,ya mata kyau sosai haka shigarshi ta burgeta matuqa
"ya khalipha badai fita zaka yi ba"murmushi ya saki kadan bayan ya dubeta yana ci gaba da gyara wuyan rigarsa
"Xan dan leqa dinner din wani abokin kasuwanci na"a shagwabe tana dan buga qafa tace
"Kai ya khalipha,amma ka sani already na hada maka dinner yana kan dining ko?"
"Dont mind,bazan jima ba zan dawo"
"Kayi alqawari?" Ta fada tana langabar da kai,murmushi ne ya qwace masa,yaran na bashi mamaki matuqa,wai sun mata baya ne?,ko sani ne basuyi ba saboda qanqantar shekaru?,ko sun sani takewa sukayi
"Nayi" kawai ya fada,binsa tayi suka jera har zuwa bangaren anni.

A parlour suka taddata kamar ko yaushe tana zaune saman kujera sanye da hijabi hannunta riqe da carbi,haka al'adarta take musamman da yake ba'a jima da gama sallar isha'i ba,amal ce zaune gefanta tana shan fruits,idanu suka hada ta sakar masa murmushi,bai iya disgi ba hakan ya sanya ya maida mata ya qarasa gefan anni ya zauna a qasan carfet kamar yadda al'adarsa take idan annin na sama bai zama a sama shima
"Ka fito khalipha"
"Eh anni na fito......ina su haidar ne?"murmushi annin ta saki tana dan tabe baki
"Nan yaci wanka ya fice,yace yaga alama saiya kawomin surukata har gida sannan zaka farka" murmushi ya saki shima yana shafa sumarsa cikin jin kunya,yasan jirwaye annin ke masa me kama da wanka,bai maida amsa ba yace
"Anni zan leqa wajen bikin mus'ab"
"Ikon Allah....lokacin har yayi kenan?"
"Eh wallahi...."
"To Allah ya sanya alkhairi,ka miqa masa saqon taya murnata"
"Zaiji in sha Allah...sai nadawo"
"Allah ya tsare hanya" amsawa yayi da amin sannan ya miqe zai fice,zeenart ce ta rufa masa baya,tsam amal ma ta miqe ta biyosu.

Gab da zasu isa jikin motocin ya jiyo muryar amal na tsaidashi,dakatawa yayi yana dubanta har ta qaraso,bata damu da zeenart dake wajen ba cikin shagwaba tace
"Yaya...amma nace ka kaini shopping kace baka da lokacin fita da dare..kuma...."
"Wannan uzuri ne daya kama dole...later ma fita ko" ya katsi qorafin data soma jerowa
"Yauwa yaya na na gode" ta fada cikin farincikin,tasan cikin ruwan sanyi ta rama abinda zeenart din tayi mata dazu na karbe girkin da ita tayi niyyar yiwa khaliphan.

Har motoci ukun da zasu fitan tare suka bar harabar gidan suna tsaye,sai da suka gama ficewa sannan zeenart taja tsaki tayi gaba zuwa cikin falon cikin gudu gudu sauri sauri,amal ta bita da harara sannan tabi bayanta suka shige ciki.

Ranta a bace ta hau step ta yiwa amarya sallama da niyyar sai gobe,don sam ba yanzu taso barin wajen ba,amma mommy ta katse mata hanzarinta ta kirata kan lallai ta biyo su aysha su dawo gida yanzu yanzu,saboda daddynsu ya dawo yana tambaya ta masa qaryar ta aikesu su duka gidan hajiya laraba.

Cikin takunshi dake nuna baiwar da Allah yayi masa ya hawo mazaunin ango da amaryan don ya shigo a makare,mus'ab din kuma yaqi karbar uzurinsa ya kafe lallai sai ya qaraso nan ya bada uzurinsa wajen amarya.

Sakkowa take a hankali saboda yanayin tsinin takalmin dake qafarta,dab da zasu gota juna idanunsa ya sauka a kanta,yanayin hade ranta abu na farko daya soma jan hankalinsa,tafiyar nutsuwa da adonta,da hanzari ya qarasa wajen ango suka gaisa sannan ya juya yace masa yana zuwa.
Chapter 12 · 0% Book details