Sashe 67
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ana magariba suka isa gidan,ya sauketa shi ya wuce masallaci don yayi sallah,da sallama ta shiga falon,mutum biyun dake tsaye a falon aka rasa mai amsata,sai mummy ce tayi qarfin halin amsawa tana cewa cikin borin kunya
"Indo ce...maraba" sai ta dubi asma'u wadda ke tsaye,inda tasan aysha ce babu abinda zai tsaidata har tazo suyi tozali da juna,uwa uba kuma ga cartoon na kifi da nama da lantana ke fito mata da su wanda zata tafi dasu gida,don dama tuni hamid ya shafe wannan babin,yace abinci shine dole aci,wadan nan sai idan ta kama aci din,ita kuma bata iya jurewa sam,tunda ta saba a gidansu ko yaushe cikin ci suke,uwa uba kuma bata saba laluba abu taji babu ba
"Bari usama su gama sallah sai ya kaiki,wannan ciki da kwadayi yake gashinan saikiyita ci ai tunda na gidanki baya burgeki,banda abun hamid ma da ya barmiki motarki basai ya wani sauya miki sabuwa ba,dududu motar watan ta nawa ma..." Mummy ta waske don kar suji kunya wajen ayshan,ta wannan bangaren sai asma'un taji dadin waskewar da mummyn tayi,hakan ya sanyata ta dan saki jiki kadan,ta koma daya daga cikin kujerun ta zauna .
Aysha baiwar Allah ita sam bata ma fahimci komai ba,hakanan bata kawo wani abu cikin ranta ba banda ma mummyn tayi magana,fuskarta a sake ta soma gaida asma'un,amsawa tayi tana dage kai kaman dai yadda take mata a baya,saidai duk da hakan bai hanata satar kallon ayshan ba,mamaki da fargaba suna mamayarta,sauyin data soma gani tattare da ayshan,saita kwatanta da kanta,babu komai tattare da ita sai uban koma baya data fara cimmata,tana shirin yi qarkon kifi daga ruwa tana shirin komawa wuta,ba ita kadai ba,ita kanta mummyn a ankare take,saita kasa daina kallon ayshan,komai nata ya sauya,hatta da yanayin maganarta
"Anty asma'u ina yaya hamid?" Aysha ta tambaya bawai da wata manufa ba,da manufa daya,duk sai asma'un ta tsargu,tana ganin kaman ayshan tasan wani abu dake faruwa da ita
"Hamid dan albarka yana nan....baha qasar ne ma,yana dubai,dazu suka gama waya wai ya aiko a dauki motarta ya auno mata wata shine kika jini ina fadan almubazzarancin da yake,bayan ba komai motar tayi ba" biyayyar ajiyar zuciya asma'un ta saki,tasan inda don ta itace masifa zata hau ayshan dashi,wanda qila garin masifar ta tona asirin kanta bata ma sani ba
"Allah sarki....an gode Allah ya qara arziqi"
"Amin amin dai.....ke kuma daga aure miji ya kwashi jiki ya tafi cyprus har yau babu shi ba labarinsa,ya bazamaki makaranta kema kamar karatu aka kawo duniya,don yana ganin hadin asma'u ne ai bai kamata ya wulaqanta ki haka ba ko?,kema saikace ba mace ba,komai sai an miki ko an kwatanta miki?" Sallamar daddy ita ta katse wannan dogon sharhin na mummy,ganinsa ya sanya asma'u miqewa,hankalinsa na kan aysha,cikin walwala yake mata maraba bakinsa a bude,itama zamowa tayo cikin qauna da kulawa ta soma gaidashi,ya amsa cikin kulawa yana tambayarta mutanen gidan da karatunta tace komai lafiya
"Khalipha ana can dai karatu da business ya riqeshi,ai ma sha Allah har yau halayensa dana sanshi da su suna nan,kusan kullum sai ya kirani mun gaisa" kanta ta duqar tana murmushi,cikin ranta tana tambayar kanta me yasa yana neman kowa amma banda ita
"Au baki tafi ba?" Daddy Ya tambayi asma'u dake yana dubanta
"Eh usaman bai shigo ba"wayarshi ya ciro yana lalubar lambar usaman yana cewa
"Ai ya kamata ki koma haka,sha'anin zaman aure sai haquri,kowacce mace da tata jarrabawar"
"Haka yake fa,kowa da tashi,ga ayshan nan ita tunda ya ajeta bai sake dawowa ba,gwara ke yakan dawo gida,kuma dama haka masu kasuwanci a qasashen waje suke,kinganta aysha wai tana qorafi kan hamid ya fiye fita waje" murmushi kawai tayi,tasan mummyn ta jina da sanin wace ita,hakanan yanzu da wayewa da karantar mutane ta cikata saita sake yiwa halayyar mummyn fashin baqi ta sake karantarta sosai
"Neman halak yake,saiki qara haquri,wani ma wannan damar yake nema bai samu ba" sai kuma mummyn tayi shuru tana sin yiwa maganar fassara,tana jin kamar ayshan da biyu ta fadi haka,hankalin daddy bai kansu sai daya gama wayarshi
"Yana waje usaman" ya furta yana ciro kudi daga aljihunsa ya miqa mata
"Aci gaba da haquri,kinji dai me na gaya miki dazun ko?"
"Eh daddy na gode"
"To madalla,zan aiko alqasim ne idan kayan sunzo ya kawo miki,zama babu sana'a babu kyau,Allah ya wuce gaba"
"Amin daddy" ta fadi tana addu'a cikin ranta karya furta wata kalmar da zata sa aysha ta gane komai,haka sukai sallama aysha na mata ta gaida gida,da qyar ta amsa tana jin kishi da qyashin ayshan cikin ranta,batasan me yasa kamar ta fita sa'a ba a rayuwa,miqewa.mummy tayi ta bita bayan ta saka an kwashe mata kayan an bita da su ta barta ita da daddy a falon suna hira,hira suke sosai abinsu gwanin sha'awa,yana jin dadin yanayin daya ga ayshan,yasan cewa da ikon Allah ta sake samun ci gaba ne a rayuwarta,a duk sanda ya tuna yadda ya daukota daga qauye su saiyaji tausayinta,ya kuma sake binta da addu'ar ci gaba da samun dacewa a rayywarta,nan haidar ya samesu,shima ya shiga hirar tasu,sun jima kafin daga bisani suyi haramar tafiya,sai a sannan ta kuma ganin mummy,ta danqa musu tsarabar data yi musu daddy ya amsa yana murna bawai don baifi qarfin abun ba,a'ah,saidon yadda kyauta take da girma da kima koma kafi qafin abinda aka yi maka kyautar da shi,yayin da mummy ta karba kadaran kadaham,duk da cikin ranta tayi farinciki,don wata sarqa ce fashion sabuwar shigowa mai tsadar gaske,ko ita bata kai ga siyanta ba har yanzu,anni ce kuma ta bata tace ta bata a zuwan ita ta saya matan,da biyu kuma tayi hakan tasan saqon zaije yadda ya kamata har cikin jiki da zuciyar mummy,ya kuma je din.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Washe gari da safe suna breakfast anni ta dubi aysha
"Ni kuwa ayshatu jiya zuwa shekaran jiya kunyi magana da khalipha?" Daga kai tayi ta dubeta gabanta na faduwa,tunda ya tafi baifi sau biyu daya ya kirata,batasan me zata ce mata ba,bata so tayi wata magana kuma batasan me khaliphan yace da anni ba karta warware masa,saita gyada kai kawai
"ke kika sakarma khalipha har haka kenan ya jima bai waiwayo gida ba?"gabanta ne ya fadi,sai tayi qoqarin tattara nutsuwarta,ta hade hannayenta waje guda bayan ta aje spoon din hannunta
"Tunda ya zauna anni akwai uzuri,idan baida wani uzuri na tabbatar bazai zauna har haka ba,zai zo da zarar ya samu dama in sha Allahu,aci gaba dai dayi masa addu'a" sosai kalamanta da amsar data bata ta kwanta mata a rai,sake shiga ranta tayi,tana yaba nutsuwa hankali da kuma haqurinta,wanda hatta yaran 'yan uwanta da dangin mahaifinsu khalipha masu zuwa dama wadanda basa zuwa bata ga masu hankali da nutsuwarta ba
"In sha Allahu aishatu,Allah yayi muku albarka" duka suka amsa da amin.
Bayan ta kammala ita ta soma tashi,saboda yau takeson ta yiwa anni gyaran dakinta kamar yadda ta saba duk sanda tazo weekend din qarshen wata,abun na damun amal sosai,amma ba yadda ta iya,kuma ita din ba iya yi zata yiba,hakan ya sanya duk weekend ita kuma take tafiya wajen mamanta har sai ayshan ta koma makaranta.
Haidar ne ya sauke ajiyar zuciya yana duban anni
"Anni....nifa ya khalipha bana ganin yana kiran anty...anya ko da gaske ne abinda ta gaya miki kidai bincika"
"Na sani haidar,ina sane na tambaya din,babu wani cikinku da zai layancemin wani abu,na san halayen kowannenku dai dai gwargwado,amma zan sake tambayarta don na tabbatar din"
"Nikam anni kimin addu'a Allah ya bani matar aure kaman takwararki" haidar ya sake fada yana dan murmushi,itama murmushi tayi tana dubanshi
"Aysha tana da nagarta aliyu,nagarta mai yawa,tana da tarbiyya wadda dai daikun yara a yanzu keda irinta,duk da tarbiyyarta daga indallahi ce,ina maka fatan samun mace kamanta"
"Allah amin" ya amsa yana daga hannu,bata rai mus'ab yayi
"Nifa anni?"
"Kaima haka auta" ta fadi tana murmushi gami da shafa kanshi,sai ya saki dariya yana jin dadin annin ta mishi haka gaban aliyu don yaji haushi fadansu na sako da sako,saidai wannan karon dauke kai yayi kaman bai gani ba.
37
Ta kammala gyaran dakin anni tana shirin fitowa annin ta shigo
"Sannu da aiki ayshatu,Allah yayi ma rayuwarki albarka" sunkui da kai tayi tana murmushi ta amsa da amin,ko yaya annin ta gwada jin dadinta kota yabeta kan wani abu dadi take ji,saboda lafazi ne da bata saba jinsa ba a bakunan al'umma a kanta,cikin karamcin ma da suka yi mata batajin tana da abinda zata saka musu dashi
"Amm...aysha" waiwayowa tayi tana amsawa
"Kikace kuna waya da khalipha?" Kai ta gyada gabanta na faduwa
"Kin tabbata?" Kai ta sake gyadawa kawai ba tare data furta komai ba
"Shikenan jeki,Allah ya dafa mana"
"Amin" ta bata amsa tana ficewa,yayin da annin ta bita da kallo,ta sani cewa samun kaman ya aishan a wannn zamanin abune mai matuqar wahala,sosai take qaunar ayshan tare da fata da kuma addu'ar Allah ya nuna mata wani lokaci da take muradin gani.
Dakinta dake nan sashen anni ta koma tana jujjuya maganar cikin ranta,kaddai ace anni ta dago wani abu ne?,da wannan tunanin ta shiga wanka,bayan ta fito ta shirya,tana son ta debo wasu kayanta daga can sashen khalipha,wanda tunda ya tafi itama ta tafi bata sake leqa sashen ba koda wasa,muqullan ma tunda ta ajesu a locker bata sake bi ta kansu ba,bude locker din tayi ta dauki keys din ta fice zuwa sashen nasu.
"Indo ce...maraba" sai ta dubi asma'u wadda ke tsaye,inda tasan aysha ce babu abinda zai tsaidata har tazo suyi tozali da juna,uwa uba kuma ga cartoon na kifi da nama da lantana ke fito mata da su wanda zata tafi dasu gida,don dama tuni hamid ya shafe wannan babin,yace abinci shine dole aci,wadan nan sai idan ta kama aci din,ita kuma bata iya jurewa sam,tunda ta saba a gidansu ko yaushe cikin ci suke,uwa uba kuma bata saba laluba abu taji babu ba
"Bari usama su gama sallah sai ya kaiki,wannan ciki da kwadayi yake gashinan saikiyita ci ai tunda na gidanki baya burgeki,banda abun hamid ma da ya barmiki motarki basai ya wani sauya miki sabuwa ba,dududu motar watan ta nawa ma..." Mummy ta waske don kar suji kunya wajen ayshan,ta wannan bangaren sai asma'un taji dadin waskewar da mummyn tayi,hakan ya sanyata ta dan saki jiki kadan,ta koma daya daga cikin kujerun ta zauna .
Aysha baiwar Allah ita sam bata ma fahimci komai ba,hakanan bata kawo wani abu cikin ranta ba banda ma mummyn tayi magana,fuskarta a sake ta soma gaida asma'un,amsawa tayi tana dage kai kaman dai yadda take mata a baya,saidai duk da hakan bai hanata satar kallon ayshan ba,mamaki da fargaba suna mamayarta,sauyin data soma gani tattare da ayshan,saita kwatanta da kanta,babu komai tattare da ita sai uban koma baya data fara cimmata,tana shirin yi qarkon kifi daga ruwa tana shirin komawa wuta,ba ita kadai ba,ita kanta mummyn a ankare take,saita kasa daina kallon ayshan,komai nata ya sauya,hatta da yanayin maganarta
"Anty asma'u ina yaya hamid?" Aysha ta tambaya bawai da wata manufa ba,da manufa daya,duk sai asma'un ta tsargu,tana ganin kaman ayshan tasan wani abu dake faruwa da ita
"Hamid dan albarka yana nan....baha qasar ne ma,yana dubai,dazu suka gama waya wai ya aiko a dauki motarta ya auno mata wata shine kika jini ina fadan almubazzarancin da yake,bayan ba komai motar tayi ba" biyayyar ajiyar zuciya asma'un ta saki,tasan inda don ta itace masifa zata hau ayshan dashi,wanda qila garin masifar ta tona asirin kanta bata ma sani ba
"Allah sarki....an gode Allah ya qara arziqi"
"Amin amin dai.....ke kuma daga aure miji ya kwashi jiki ya tafi cyprus har yau babu shi ba labarinsa,ya bazamaki makaranta kema kamar karatu aka kawo duniya,don yana ganin hadin asma'u ne ai bai kamata ya wulaqanta ki haka ba ko?,kema saikace ba mace ba,komai sai an miki ko an kwatanta miki?" Sallamar daddy ita ta katse wannan dogon sharhin na mummy,ganinsa ya sanya asma'u miqewa,hankalinsa na kan aysha,cikin walwala yake mata maraba bakinsa a bude,itama zamowa tayo cikin qauna da kulawa ta soma gaidashi,ya amsa cikin kulawa yana tambayarta mutanen gidan da karatunta tace komai lafiya
"Khalipha ana can dai karatu da business ya riqeshi,ai ma sha Allah har yau halayensa dana sanshi da su suna nan,kusan kullum sai ya kirani mun gaisa" kanta ta duqar tana murmushi,cikin ranta tana tambayar kanta me yasa yana neman kowa amma banda ita
"Au baki tafi ba?" Daddy Ya tambayi asma'u dake yana dubanta
"Eh usaman bai shigo ba"wayarshi ya ciro yana lalubar lambar usaman yana cewa
"Ai ya kamata ki koma haka,sha'anin zaman aure sai haquri,kowacce mace da tata jarrabawar"
"Haka yake fa,kowa da tashi,ga ayshan nan ita tunda ya ajeta bai sake dawowa ba,gwara ke yakan dawo gida,kuma dama haka masu kasuwanci a qasashen waje suke,kinganta aysha wai tana qorafi kan hamid ya fiye fita waje" murmushi kawai tayi,tasan mummyn ta jina da sanin wace ita,hakanan yanzu da wayewa da karantar mutane ta cikata saita sake yiwa halayyar mummyn fashin baqi ta sake karantarta sosai
"Neman halak yake,saiki qara haquri,wani ma wannan damar yake nema bai samu ba" sai kuma mummyn tayi shuru tana sin yiwa maganar fassara,tana jin kamar ayshan da biyu ta fadi haka,hankalin daddy bai kansu sai daya gama wayarshi
"Yana waje usaman" ya furta yana ciro kudi daga aljihunsa ya miqa mata
"Aci gaba da haquri,kinji dai me na gaya miki dazun ko?"
"Eh daddy na gode"
"To madalla,zan aiko alqasim ne idan kayan sunzo ya kawo miki,zama babu sana'a babu kyau,Allah ya wuce gaba"
"Amin daddy" ta fadi tana addu'a cikin ranta karya furta wata kalmar da zata sa aysha ta gane komai,haka sukai sallama aysha na mata ta gaida gida,da qyar ta amsa tana jin kishi da qyashin ayshan cikin ranta,batasan me yasa kamar ta fita sa'a ba a rayuwa,miqewa.mummy tayi ta bita bayan ta saka an kwashe mata kayan an bita da su ta barta ita da daddy a falon suna hira,hira suke sosai abinsu gwanin sha'awa,yana jin dadin yanayin daya ga ayshan,yasan cewa da ikon Allah ta sake samun ci gaba ne a rayuwarta,a duk sanda ya tuna yadda ya daukota daga qauye su saiyaji tausayinta,ya kuma sake binta da addu'ar ci gaba da samun dacewa a rayywarta,nan haidar ya samesu,shima ya shiga hirar tasu,sun jima kafin daga bisani suyi haramar tafiya,sai a sannan ta kuma ganin mummy,ta danqa musu tsarabar data yi musu daddy ya amsa yana murna bawai don baifi qarfin abun ba,a'ah,saidon yadda kyauta take da girma da kima koma kafi qafin abinda aka yi maka kyautar da shi,yayin da mummy ta karba kadaran kadaham,duk da cikin ranta tayi farinciki,don wata sarqa ce fashion sabuwar shigowa mai tsadar gaske,ko ita bata kai ga siyanta ba har yanzu,anni ce kuma ta bata tace ta bata a zuwan ita ta saya matan,da biyu kuma tayi hakan tasan saqon zaije yadda ya kamata har cikin jiki da zuciyar mummy,ya kuma je din.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Washe gari da safe suna breakfast anni ta dubi aysha
"Ni kuwa ayshatu jiya zuwa shekaran jiya kunyi magana da khalipha?" Daga kai tayi ta dubeta gabanta na faduwa,tunda ya tafi baifi sau biyu daya ya kirata,batasan me zata ce mata ba,bata so tayi wata magana kuma batasan me khaliphan yace da anni ba karta warware masa,saita gyada kai kawai
"ke kika sakarma khalipha har haka kenan ya jima bai waiwayo gida ba?"gabanta ne ya fadi,sai tayi qoqarin tattara nutsuwarta,ta hade hannayenta waje guda bayan ta aje spoon din hannunta
"Tunda ya zauna anni akwai uzuri,idan baida wani uzuri na tabbatar bazai zauna har haka ba,zai zo da zarar ya samu dama in sha Allahu,aci gaba dai dayi masa addu'a" sosai kalamanta da amsar data bata ta kwanta mata a rai,sake shiga ranta tayi,tana yaba nutsuwa hankali da kuma haqurinta,wanda hatta yaran 'yan uwanta da dangin mahaifinsu khalipha masu zuwa dama wadanda basa zuwa bata ga masu hankali da nutsuwarta ba
"In sha Allahu aishatu,Allah yayi muku albarka" duka suka amsa da amin.
Bayan ta kammala ita ta soma tashi,saboda yau takeson ta yiwa anni gyaran dakinta kamar yadda ta saba duk sanda tazo weekend din qarshen wata,abun na damun amal sosai,amma ba yadda ta iya,kuma ita din ba iya yi zata yiba,hakan ya sanya duk weekend ita kuma take tafiya wajen mamanta har sai ayshan ta koma makaranta.
Haidar ne ya sauke ajiyar zuciya yana duban anni
"Anni....nifa ya khalipha bana ganin yana kiran anty...anya ko da gaske ne abinda ta gaya miki kidai bincika"
"Na sani haidar,ina sane na tambaya din,babu wani cikinku da zai layancemin wani abu,na san halayen kowannenku dai dai gwargwado,amma zan sake tambayarta don na tabbatar din"
"Nikam anni kimin addu'a Allah ya bani matar aure kaman takwararki" haidar ya sake fada yana dan murmushi,itama murmushi tayi tana dubanshi
"Aysha tana da nagarta aliyu,nagarta mai yawa,tana da tarbiyya wadda dai daikun yara a yanzu keda irinta,duk da tarbiyyarta daga indallahi ce,ina maka fatan samun mace kamanta"
"Allah amin" ya amsa yana daga hannu,bata rai mus'ab yayi
"Nifa anni?"
"Kaima haka auta" ta fadi tana murmushi gami da shafa kanshi,sai ya saki dariya yana jin dadin annin ta mishi haka gaban aliyu don yaji haushi fadansu na sako da sako,saidai wannan karon dauke kai yayi kaman bai gani ba.
37
Ta kammala gyaran dakin anni tana shirin fitowa annin ta shigo
"Sannu da aiki ayshatu,Allah yayi ma rayuwarki albarka" sunkui da kai tayi tana murmushi ta amsa da amin,ko yaya annin ta gwada jin dadinta kota yabeta kan wani abu dadi take ji,saboda lafazi ne da bata saba jinsa ba a bakunan al'umma a kanta,cikin karamcin ma da suka yi mata batajin tana da abinda zata saka musu dashi
"Amm...aysha" waiwayowa tayi tana amsawa
"Kikace kuna waya da khalipha?" Kai ta gyada gabanta na faduwa
"Kin tabbata?" Kai ta sake gyadawa kawai ba tare data furta komai ba
"Shikenan jeki,Allah ya dafa mana"
"Amin" ta bata amsa tana ficewa,yayin da annin ta bita da kallo,ta sani cewa samun kaman ya aishan a wannn zamanin abune mai matuqar wahala,sosai take qaunar ayshan tare da fata da kuma addu'ar Allah ya nuna mata wani lokaci da take muradin gani.
Dakinta dake nan sashen anni ta koma tana jujjuya maganar cikin ranta,kaddai ace anni ta dago wani abu ne?,da wannan tunanin ta shiga wanka,bayan ta fito ta shirya,tana son ta debo wasu kayanta daga can sashen khalipha,wanda tunda ya tafi itama ta tafi bata sake leqa sashen ba koda wasa,muqullan ma tunda ta ajesu a locker bata sake bi ta kansu ba,bude locker din tayi ta dauki keys din ta fice zuwa sashen nasu.