← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 114

Sashe 77

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sun danyi nisa kadan taji yayi gyaran murya
"Ayishah" ya kirata sunanta wanda salon yadda sautin lafuzan ya fita tilas kowace ke ki juyo ki kalleshi,sunan yayi dadi da matuqar tsaruwa a bakinsa,saidai tayi mamakin yadda ya iya kiran sunan kai tsaye duk da sunan anninsa ne
"Duka wani dan adam da kika gani a arayuwarshi daya cimma nasara yana da nashi tarin qalubalen daya taba fuskanta,hakanan babu wani mutum daya a rayuwa da yau zaice bashi da wata damuwa ko matsala koda kuwa ya wadata da komai bai rasa lalura hakane?" Kai ta gyada tana yarda da kowanne lafazi dake fita daga bakinsa
"Hakane" ta furta cikin sanyi gabanta na faduwa,don batasan meye abu na gaba da zai fito daga bakinsa
"Dukkan nasara tana tare da qalubale,hakanan idan kanason cimma nasara saika jajirce kayi tafitar ruwa da duk wani qalubale da zaka fuskanta,ka dauki wannan qalubalen tamkar wani mataki ko tsani ne da zai maka jagora izuwa cimma nasararka"kai ta sake gyadawa tana jiran jin ko xaice wani abu,saidai babu abinda ya sake cewa har suka isa wata anguwa,saiya rage gudun motar tashi ya soma ga garawa cikin layin wanda baida kwalta,unguwar nada kyau dai dai misali,hakanan gine ginenta a tsare suke ba wani cunkuso ko hayaniya mai yawa wanda bata zaci haka ba,ta dauka yadda takeji ana cewa cunkus dakin tsumma ta zaci ko inama haka yake,saidata gama qarewa unguwar kallo har qofar gidan da suka tsaya sannan ta waiwayo ta dubeshi,ashe ita yake kallo shima,bayansa na jingine da sit din da yake zaune,sake kiran sunanta yayi karo na biyu wanda sai dayasa tsigar jikinta zubawa
"duk duniya mahaifiya qwaya tak Allah yake halittarma dan adam saboda muhimmancinta,ina da yaqinin duk wani da zaki samu a rayuwa ba zaki taba samun cikakken kwanciyar hankali nutsuwa da walwala ba matuqar kina tuna alaqar dake tsakaninki da mahaifiyarki,gidan mahaifyarki na kawoki,inaso ki samo soyayyar mahaifiyarki da kanki ba tare da kowa ya shiga tsakani ba....inason inga iya jarumtarki da kuma adadin yawan yanda kike sonta" tuni qwalla ta soma wanke mata fuska,tsoro da fargaba gami da rauni keson shigarta,saidai kalaman da khalipha yaci gaba dayi su suke son tsaida zuciyarta qyam waje guda su bata qwarin gwiwa
"Banason na sake ganin qwalla a fuskarki,aiki zakiyi tuquru saboda ki samawa kanki da zucuyarki salama" ya fada yana miqa mata handkherchief dinsa,amsa tayi sai kawai ta dorashi saman fuskarta ya manne a fuskar yana tsotse sabbin hawayen dake fitowa,yayin da qamshin dake tashi jikin handkherchief din ya dinga sanyaya mata zuciyarta,daga bisani ta zare handkherchief din,daidai lokacin da wasu yara dake sanye da kayan makaranta ke yunqurin shiga gidan da yace ya kawota din
"Basmah" ayshan ta furta tana dubansu,ganinsa yakai inda yaga tana kalla,saiya sauke glass din motar da sauri,cikin muryarshi mai taushi cike da nutsuwa yakirata
"Basmah" waiwayowa tayi tana dubanshi alamun baqunta da rashin sanin fuskarshi,takowa ta dinga yi bakin motar,sanda ta iso gab da window din motar idanunta ya fada kan na aysha,ihu ta saki tana zagayowa bangarenta,itama aysha balle murfin motar tayi da sauri ta fito suka rungume juna
"Anty indo!,wayyo anty indo kece?!,ummi ce tace kizo?" Kai ta kada tana shirin zubda wata qwallar
"Ba ita bace basma tsoron shiga nakeji" riqe hannunta tayi qyam
"Zo muje anty indo ni zan tayaki bawa ummi haquri,tunda kikazo har garinmu zata haqura,dama kinsan gidanmu anty indo?" Waiwayawa tayi ta dubi khalioha suka hada ido dashi,da ido ya bata qwarin gwiwa yana jijjiga mata kai tare dayi mata sign na tayi addu'a,gyada kai tayi ta soma takawa tana bin basmah dake faman jan hannunta tare da zuba mata surutu da tambayoyi kala kala,sai da suka isa bakin qofar gidan ta lura da sauran yaran,duka sun girma,suka zuba mata ido alamin sun ganeta amma ba wanda ya iya cewa komai saida basmah tace
"Anty indonmu ce fa,ku gaisheta" kaman a tsorace suke haka suka gaidata sannan suka bude dan madaidaicin gate din gidan suka saka kai ciko,yayin da khalipha ya fito daga cikin motar ya rufe,ya haye daman booth din motar ya tasa gidan a gaba bayan ya harde hannayensa a qirjinsa yana zaman jiran tsammani.
[26/02, 8:54 PM] +234 810 044 6653: 42

Ko ina na 'yar harabar gidan har zuwa cikin gidan fes yake,tasan za'a rina saboda tana da labarin yadda ummin nata keda matuqar tsafta,don har gorin tsaftar tata take mata abun dariya,donsu a wajensu gani suke tamkar wani iyayi ne kawai na naja'atu,ko tana son nuna cewa tafi kowa,ba zata zauna tayi rayuwa yadda tazo ta tars da sauran matan gidan nayi ba.

Ci gaba tayi da binsu har zuwa cikin falon gidan,falo ne mai dan yalwa wanda yake shima tsaf,sai qamshin girki dake fitowa daga kitchen din dake cikin falon
"Ummi!" Basma ta qwala mata kira sanda yaran kowannensun ya nemi wajen zama yana cire takalmansa da kayan makarantar dake jikinsu
"Ban hanaki wannan iskancin ba basma?,shekara goma sha biyar idan baki hankali ba bansan sai yaushe ba" muryar ummin dake kitchen ta ratso falon,sai aysha taso tanemi nutsuwarta ta rasa,tsoro da fargaba suka cikata
"Ummi kinyi baquwa ne fa?"
"Tohm,su zauna ina zuwa"ta fada daga kitchen din
"Ki xauna anty indo" basma ta fada tana nuna mata kujera,murmushin qarfin hali aysha tayi kawai,fiye da rabin hankalinta nakan kitchen din,haka ta dosana ta zauna gefan kujerar tana rarraba ido a falon,kitcheb basma ta shiga ta dauko mata ruwa da lemo,tana tajanta da hira saidai itasam aysha hankalinta ba'a jikinta yake ba.

Shudewar kusan minti goma sannan ta jiyo takun fitowa daga kitchen din,ummince ta bayyana cikin dinkin riga da zani na atamfa,kanta daure da dankwalin kayan wanda sokashi kawai tayi,miqewa tsaye zumbur aysha tayi idanunta akan ummin,zuciyarta kamar zata fito saboda tsabar bugawar da take
"Basma ina....." Maganar ummin ta maqale sakamakon hada idanu da sukayi da aysha,kallon kallo sukayi na tsahon mintina biyu,tuni hawaye ya cika idanun aysha,bata isa ta tsaidasu ba a irin wannan yanayin saboda haka ta barsu suka soma zuba,juyawa ummin tayi zata koma kitchen,cikin muryar kuka rauni da kuma karyewar zuciya ayshan ta soma magana kuka na rirriqe wasu kalmomin nata
"Karki koma don girman Allah ummi,karki sake juyamin baya ummi,ki tausayamin ki dubi 'yarki,ina sonki ummi bani da kamarki duk duniya,ina da buqatarki,inason in rayu dake,ina buqatar kulawar uwa,inason inji duminta a jikina kamar yadda kowanne yaro kejin haka" bata waiwayo ba sai taci gaba da takawa zata wuce kitchen din,da gudu aysha ta zube jakar hannunta ta bi bayantq,kafin takai ga shigewa kitchen din aysha ta cafki hannunta ta baya ta riqe gam,saita sulale ta duqa kan gwiwarta
"idan kika barni wa kika barwa ni ummi?"
"Ummi me anty indo tayi miki ke wai haka da bakya sonta,kome tayi miki ummi ta dade fa tana baki haquri yaci ki haqura,ki kalla fa kiga irin kukan da take..."
"Rufemin baki basma,uban ya baki damar sanya bakinki kan wannan maganar,har yaushe aka haifeki da kika isa saka bakinki!" Ummin ta fada cikin wata murya dake cike da fushi cakude da rauni daga boye a can qasanta
"Idan kina son salama a rayuwarki ki tashi ki tattara kibar gidan nan,bama gidan ba garin gaba daya nakeso ki bari" ta fadi still har yanzu ayshan na bayanta bata bari taga fuskarta ba,ta sabule hannunta ta shige kitchen din gami da rufe kanta a ciki.

Kuka sosai aysha ta saki har yana fidda sauti sosai ta duqe a wajen
"Don Allah ummi don Allah" shine abinda take iya fadi kenan,cikin bacin rai basma ta tako inda ayshan take tana qoqarin dagota
"Yi haquri anty indo ki tashi,kiyi tafiyarki anty indo tunda har bata sonki karki sake nemanta,tashi ki tafi Allah yaga zuciyarki" da sauri ummi data hada kanta da qofar wanda ita bata fito ba ita bata koma ciki ba ta daga kanta,cikin hanzari ta bude qofar kitchen din ta isa gabansu,hannun basma ta fincika sannan ta zabga mata mari,janta tayi har zuwa dakinsu ta turata ciki ta rufesu ita da basman baki daya,kasa tashi aysha tayi kuka take bilhaqqi,ta kusa a qalla minti goma sannan ta iya miqewa da qyar tana jin jiri na daukarta ta lalubi hanyar fita.

Tunda ya kafawa gidan ido bai dauke idanunshi ba,cikin jikinsa yake jin akwai matsala,da hanzari ya duro daga saman motar sanda ta fito daga gidan ya nufeta,kama hannayenta yayi jin yadda jikinta ke rawa sai ya hadata da qirjinsa ya lullubeta da dukka hannayensa yanajin yadda take nishin kuka bugun zuciyarta na sake yawa,a qalla minti biyar sukayi a haka sannan yaci gaba da takawa da ita a hankali zuwa bakin motar,gidan baya ya bude ya sakata shima ya shiga,har a sannan kuka take sosai,gorar ruwa mai sanyi ya dauko da handkherchief sannan ya sake komawa bayan gab da ita ya zauna yana fuskantarta yana kallon yadda takr kuka kaman babu gobe,ranshi ya soma baci,tausayinta ya sake ninka nada cikin ranshi,ko ba'a gaya masa ba yasan amsar data biyo baya,tsahon shekaru har yau bata haqura ba?,tsahon wannan zamanin har yau jiya iyau?
"La'ilaha ilallah,Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla,wa'anta taj'alil hazna iza shi'ita sahla" ya dinga fada cikin taushin murya da sanyi,a hankali itama ta kama suka dinga maimaitawa tare,sannu sannu kukan nata ya ragu,hawayen ya soma daukewa,sai ya bude gorar ruwan ya miqa mata,bata musa ba ta karba tasha,saidai ba wani abu dataji ya ragu na quncin da take ji,ta kusa minti goma tana zuqar ruwan da kadan da kadan,don da qyar yake wuce mata,daga bisani ta miqa masa robar,yasa hannu zai amsa yaji alamun jikinta ya dauki dumi,goshinta ya dafa dai yaji jijiyoyin kanta suna harbawa,hakan kan ya dauki zafi
"Zazzabi kike ji?" Ya tambayeta cikin tausayawa
"Kaina...ke ciwo"
"Ya salam" ya fada yana qarasa hade gap din dake tsakaninsu,wanda hakan ya bata damar jingina sosai da kafadarshi.

Wayarshi ya ciro cikin aljihun wandonsa ya kira wata lamba,ba'a wuce minti goma ba wani matashi ya iso,cikin wani yare da aysha ke kyautata zaton yarbanci ne sukayi magana da khalipha cikin girmamawa,ya shiga ya tads motar suka bar unguwar.

Lokaci lokaci yakan dora hannunshi saman goshinta yaji ya dumi jikinta yake,jin zazzabin na sake hawa yayi masa magana ya juya dasu xuwa asibiti,kafin ko suje asibitin har ta soma rawar dari.
Chapter 77 · 0% Book details