Sashe 24
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan daya daga cikin kujerun ta tsaya tamkar mai tsoron wani abu,idanunta zube saman teburin dake gabansu
"Salamu alaikum" ta furta cikin muryarta mai sanyi wadda ta soma rawa rawa alamun ko yaushe tana iya sakin kuka,kujerar da take tsaye kusa da ita ya tura mata idanunshi a kanta yana karantarta,ta fuskanci me yake nufi ga kuma nauyi da taji idanunsa sun mata a kanta,hakan ya sanya bata jaa ba ta matsa kusa da ita ta zauna tana curewa waje daya kamar zai cutar da ita,sai data zauna din sannan ya amsa mata sallamar
"Suna na muhammad khalipha...kefa?" Ya tambaya yana maida vivo dinsa aljihun gaban rigarsa
"Aishatu...." Idanunsa ya dan lumshe kadan sannan ya budesu saboda girman da darajar sunan da yake gani,sunan anninshi ne hakan ya sanya yake ganin qimar duk mai sunan da shi sunan kansa,gyaran murya yayi bayan ya hade yatsunshi waje guda
"Ban sani ba...ko kina da masaniya kan abinda yake faruwa...abinda 'yar uwarki tayi da abinda ke shirin faruwa a garemu gaba daya,da amincewarki?..da saninki?...ko da sa hannunki?"
"Ina mai baka shawarar ka bijirewa auren aishah,saboda bakasan wacece ita ba....sanin wace ita ya sanya asma'u shirya abinda ta shirya din" ta fada kanta tsaye,rauni da dakiya na tarayya cikin zuciyarta lokaci guda,abinda bata taba zaton yana haduwa cikin zuciyar dan adam cikin lokaci daya ba,idanu ya tsira mata cike fal da mamakin wacce iriyar mutum ce ita?,a yadda tayi maganar ya tabbata da shi matsoracin namiji ne babu abinda zai hanashi miqewa ya nemi arcewa,bai taba gamo da mutumin dake baiwa mutane shawarar su gujeshi ba komai girman laifin da yake aikatawa ba,amma fuskarta kawai ta karantar da shi akwai wani lamari mai girma dake cin zuciyarta wanda bazaiso yanke hukunci ba sai yasan meye shi,idanunshi ya janye daga kanta ya saki ajiyar zuciya bayan ya sarqafe yatsunsa na hagu da dama waje guda.
"Sannunku masoya" muryar asma'u cikin sautin amon dariya yayi kutse cikin nazarin da kowannensu ya fada,a tare suka daga kai suka dubeta ba tare da kowannensu yace komai ba
"Yaron oga an samu damar bullowa kenan?....hakan yayi kyau" ta qara fada cikin dariya dariyar da tafi gama fa izgili
"Allah ya barku tare,musha biki" ta kuma fadi tana dai dariyar izgilanci
"Ammm....yaron oga....ina muku fatan alkhairi fa a auren da zakuyi....saidai ina fatan ta gaya maka cewa ita din ba jinin gidan nan bace....sannan yana da kyau ka shirya zuwa qauyensu ka gano tushenta....don kada ma ta yaudareka tace maka nan ce mahaifarta ko daddy na shi ya haifeta ni sistern ta ce...na barku lafiya" ta fada tana ficewa daga lambun,yanayin kwalliyarta kawai ya isa ya gaya maka cewa hamid ne yazo,khalipha shi ya fara dauke idanunsa zuciyarsa na tafasa,yana jin kaman ya tashi ya nunawa asma'u true colour dinsa,yana jin kaman ya hukunta asma'u a wajen,mahaifinta shi ya fado masa a rai,tunashin da yayi shi ya katse masa dukkan wani hanzari nasa,tilas ya tattara duk wani fushi da bacin rai daya taso masa ya lanqwameshi ta hanyar sakin ajiyar zuciya mai tsaho,yana mamakin yadda ta zamto jinin daddy 'yarsa tsatsonsa,ba shakka Allah dama ya fadi yana fitar da rayayye daga matacce ya kuma fitar da matacce daga rayayye,wani bari na zuciyarsa yaci gaba da tausarsa da danneshi yana gaya masa cewa AKWAI LOKACI.....
Idanunsa ne suka sauka kan fuskar aysha wadda tuni ta jiqe da hawaye,bakinsa ya bude zaiyi magana ta daga hannunta da sauri ta dakatar da shi
"Har abada tushena shine abun alfahari na koda kuwa wa na zama cikin doron qasa....har abada inason iyaye na komai lalacewarsu sune silar zuwa na duniya....har abada dangina sune dangina bani da makwafinsu da zan sauya su da su komai girman sabani ko rashin fahimta,ni aisha har abada ina son qauye ina taqama da shi saboda shine asalin kowanne dan adam koshi waye saidai idan shi din ya zama kaza ce ci ka goge bakinka" wadannan kalamai su suka sauka cikin kunnuwan khalipha da asma'u dake shirin ficewa a wajen,kamar zata tanka saita tuna hamid data bari yana jiranta kada ranshi ya baci yayi tafiyarsa,hakan ya sanya ta waiwayowa ta kalleta da niyyar bata gargadi,sai kuma tayi rashin sa'a idanun ayshan bai kanta ta sanyasu tsakiyar tafin hannunta kamar mai qayyade adadin jijiyoyin dake kaiwa hannun nata jini da dawo da shi,dole ta juya ta fice ba tare data samu damar maida raddi ba.
Wani irin abu shi ya shiga kaiwa da kawowa cikin zuciyarsa idanunshi a kanta,karon farko da ya yiwa wata mace kallon qurilla tsahon girmansa
"Bana buqatar sanin ko ke wace ce?....ki riqe tarihin rayuwarki naki ne."jiqaqqun idanunta da suka jiqa har gashin idanunta suka qara fito da tsahonsu da baqinsu
"Ya zama dole kasan wace aysha matuqar zaka karbi aure na....rashin sanin wace ce ni ya ta'allaqa ne da hukuncin daka yanke wa karbar aurenmu"
"Kinsan waye daddy kuwa a wajena?,kinsan me ya taba yiwa rayuwata?"
"Kamar yadda bakasan waye ba a wajena da abinda ya yiwa tawa rayuwar yake kuma kan yi mata....indai haka ne dole kasan wace ni" ta fada hawayen idonta naci gaba da zuba.
"Suna na aishah umar sanda,hafaffiyar wani qauye cikin qaramar hukumar takai dake jihar kano takai,mahaifiyata sunanta naja'atu,mahaifina cikakken bafulata ni ne,hakan ya sanya sunansa na asali ya bata saidai a kirashi da baffale,mahaifiyata kuwa 'yar manoma ce amma dukkansu mazauna qaramar hukumar takai ne,duk da irin wakaci ka tashin dake faruwa tsakanin manoma da makiyaya amma haka Allah ya qaddara aurensu,saidai irin abubuwan dana dinga gani bayan an haifeni na soma girma nasan cewa ba qaramin kai ruwa rana akayi da iyayen baffana ba kafin su yarda ya auri ummi na.
Ni kadai mahaifina ya haifa har ya rasu,nayi wata iriyar rayuwa daga tashina zuwa girmana,wanda tunda na girman baisan wani abu waishi qauna tausayi ko jin qai ba,bansan soyayya ba,bansan lallashi ba,bansan kula ba,rana tsaka na tashi na girma na gani a matsayin 'YAR TSAKAR GIDA,da wahala na budi ido,da bauta na saba,da bin umarni ko hani nake aiki koda yaushe,babu mai cemin sannu,babu me cemin na gode,babu me cewa me yake damunki,babu mai cewa me kikeso meye bakya so?,mahaifiyata ta bar gidan ta barni da qananun shekaru,ta barni tun bani da wayo sanin ciwon kaina,bana ce ga abinda ya faru ba don bani da masaniya,a hannun kakata inna yelwa ta barni,saidai kuma hakan a baki kawai yake,mahaifina yana da yayye uku qanne hudu,dukkansu cikin gidan suke suda matansu da 'ya'yansu,duk cikinsu babu mai mace daya,daga mai biyu sai mai uku,ga tarin yara da suke da shi,tunda na tashi nafi kowa rashin gata cikin gidan,kusan a tsakar gida nake qare rayuwata,hakanan duk wani aikin wahala na gidan yana wuya na,nice lungun baba auwalu,nice lungun baba sani,nice lungun baba salisu,nice na baba rabi'u,khamisu tasi'u,sabi'u,babu wanda ban gararamba a lungunsa yaransu na zaune,kuma ban isa nayi kuskure ko inyi ba dai dai ba,yadda akeso haka zanyi komai sauqi komai wuya,ba ruwansu da zafi sanyi rani da damina,kuma kakata tana kallo,asali ma sai na lura da babu abinda ya shafeta,ita kanta idan ta kama sai ta jani ta daka iya son ranta,duk cikin jikokinta ni tafi tsana,duk wanda zai hukunta ni koda hukuncin yafi girman abinda na aikata din ba damuwarta bane,saidai ta tayasu ma da jifana da miyagun kalmomi kala kala
"Shegiya ta gado baqin hali irin na gidansu uwarta naja,tur da jinin gidan saluhu,jinin fitsara jinin kafirar zuciya" wannan kalmar tun ban fahimtar me take nufi har nazo na ganeta,na kuma haddace ta ta zauna daram a kaina,bansan me nayi musu ba,bansan wanne girman laifi ne dani cikin gidan ba da kowa bai qaunata,yaqi jinina,tsangwamar bata tsaya iya cikin gidanmu ba,koda sauran mutane sai suke min abinda suka ga dama ganin bani da wani tsayayye wanda zai tsayan,ko cikin yara sa'anni na ina cin duka,kyara da tsangwama,musamman daya zamto nafi kowa qazanta na kuma fi kowa rashin gata,a lokacin mahaifina yana raye,bashi da abin cewa duk da cewa shima na lura bai wani damu dani sosai ba,yafi nuna kulawa ga sabuwar matarsa mai suna kuluwa,zuwan kuluwa gidan sai ya sake zama tamkar sabuwar babin azaba ne a tare da ni,yar kulawar da baba na ke nunawa kaina sai na rasa,ta janye hankalinsa tsaf,hakanan hatta da kakata ta koma qarqashin iko da mulkin kuluwa,a da babana kan zauna dani mu danyi hira,yakan yawaita cemin na yafe masa,zuwan kuluwa gidan da komawar inna yelwa qarqashin ikonta sai ya haddasa sababbin jam'iyyu kala kala a gidanmu da kuma kishin bal bal mai azabar zafi a tsakanin faccalolin,nidai a sannan bani ga tsuntsu bani ga tarko,ta rayuwata nake,duk inda na tattala ta sai anga an rushe,walau baba kuluwa ko sauran faccalolinta,kowa yagata yake figata yake,ina da son tsafta,ina son karatu kaman me,ina son gayu amma duka sun gagareni,duk da kaf cikin yaran gidan babu wanda ya damu da karatun saini daya,walau arabi ko boko,kuma babu wandaya matsanta musu kan hakan,son karatu na sai ya zama kamar wani sanabe ne ko iyayi ne a ganinsu da ganin ina nuna ai ni nafi kowa,hakan yasa aka qara qaimin datsemi duk wata qofa ta ilimi,tun sallar asuba idan na tashi nake bauta cikin gidan ba wanda ya damu da tsaftata ci na sha na suturata ko karatuna har dare ya shiga sannan ya maida haqarqarina na kwanta,da qyar nake samun sauran abinci naci ko sau biyu ne kacal a rana,haka zan hada guntu guntunsu duk lalacewarsa naci,watarana na kwana tsakar gida gefan dakin inna yelwa,watara na na kwana gefan turken awaki idan ta koreni daga qofar dakinta,watarana kuma ta barni daga cikin dakin nata amma daga bakin qofa komai sanyi komai damuna,kayan sawata kuwa a wani tsohon kwandon qarfe na shara suke,idan damina ta sauka haka zasuyita jiqewa ina matsewa ina shanyawa,dama gashi ba cikakken wanki suke samu ba.
Wani abu da Allah ya doramin shine son mahaifiyata da qulafucinta,saidai abinda ya soma girgixa hankalina fiye da dukkan abinda yake faruwa dani shine...." Tsinkewa maganar tayi daga harshenta,saboda wani daci da abu mai tauri daya riqe mata maqoshi,kuka nason kufcemata,aduk sanda ta tuna wannan gefan na rayuwarta bata iya jurewa
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
"Salamu alaikum" ta furta cikin muryarta mai sanyi wadda ta soma rawa rawa alamun ko yaushe tana iya sakin kuka,kujerar da take tsaye kusa da ita ya tura mata idanunshi a kanta yana karantarta,ta fuskanci me yake nufi ga kuma nauyi da taji idanunsa sun mata a kanta,hakan ya sanya bata jaa ba ta matsa kusa da ita ta zauna tana curewa waje daya kamar zai cutar da ita,sai data zauna din sannan ya amsa mata sallamar
"Suna na muhammad khalipha...kefa?" Ya tambaya yana maida vivo dinsa aljihun gaban rigarsa
"Aishatu...." Idanunsa ya dan lumshe kadan sannan ya budesu saboda girman da darajar sunan da yake gani,sunan anninshi ne hakan ya sanya yake ganin qimar duk mai sunan da shi sunan kansa,gyaran murya yayi bayan ya hade yatsunshi waje guda
"Ban sani ba...ko kina da masaniya kan abinda yake faruwa...abinda 'yar uwarki tayi da abinda ke shirin faruwa a garemu gaba daya,da amincewarki?..da saninki?...ko da sa hannunki?"
"Ina mai baka shawarar ka bijirewa auren aishah,saboda bakasan wacece ita ba....sanin wace ita ya sanya asma'u shirya abinda ta shirya din" ta fada kanta tsaye,rauni da dakiya na tarayya cikin zuciyarta lokaci guda,abinda bata taba zaton yana haduwa cikin zuciyar dan adam cikin lokaci daya ba,idanu ya tsira mata cike fal da mamakin wacce iriyar mutum ce ita?,a yadda tayi maganar ya tabbata da shi matsoracin namiji ne babu abinda zai hanashi miqewa ya nemi arcewa,bai taba gamo da mutumin dake baiwa mutane shawarar su gujeshi ba komai girman laifin da yake aikatawa ba,amma fuskarta kawai ta karantar da shi akwai wani lamari mai girma dake cin zuciyarta wanda bazaiso yanke hukunci ba sai yasan meye shi,idanunshi ya janye daga kanta ya saki ajiyar zuciya bayan ya sarqafe yatsunsa na hagu da dama waje guda.
"Sannunku masoya" muryar asma'u cikin sautin amon dariya yayi kutse cikin nazarin da kowannensu ya fada,a tare suka daga kai suka dubeta ba tare da kowannensu yace komai ba
"Yaron oga an samu damar bullowa kenan?....hakan yayi kyau" ta qara fada cikin dariya dariyar da tafi gama fa izgili
"Allah ya barku tare,musha biki" ta kuma fadi tana dai dariyar izgilanci
"Ammm....yaron oga....ina muku fatan alkhairi fa a auren da zakuyi....saidai ina fatan ta gaya maka cewa ita din ba jinin gidan nan bace....sannan yana da kyau ka shirya zuwa qauyensu ka gano tushenta....don kada ma ta yaudareka tace maka nan ce mahaifarta ko daddy na shi ya haifeta ni sistern ta ce...na barku lafiya" ta fada tana ficewa daga lambun,yanayin kwalliyarta kawai ya isa ya gaya maka cewa hamid ne yazo,khalipha shi ya fara dauke idanunsa zuciyarsa na tafasa,yana jin kaman ya tashi ya nunawa asma'u true colour dinsa,yana jin kaman ya hukunta asma'u a wajen,mahaifinta shi ya fado masa a rai,tunashin da yayi shi ya katse masa dukkan wani hanzari nasa,tilas ya tattara duk wani fushi da bacin rai daya taso masa ya lanqwameshi ta hanyar sakin ajiyar zuciya mai tsaho,yana mamakin yadda ta zamto jinin daddy 'yarsa tsatsonsa,ba shakka Allah dama ya fadi yana fitar da rayayye daga matacce ya kuma fitar da matacce daga rayayye,wani bari na zuciyarsa yaci gaba da tausarsa da danneshi yana gaya masa cewa AKWAI LOKACI.....
Idanunsa ne suka sauka kan fuskar aysha wadda tuni ta jiqe da hawaye,bakinsa ya bude zaiyi magana ta daga hannunta da sauri ta dakatar da shi
"Har abada tushena shine abun alfahari na koda kuwa wa na zama cikin doron qasa....har abada inason iyaye na komai lalacewarsu sune silar zuwa na duniya....har abada dangina sune dangina bani da makwafinsu da zan sauya su da su komai girman sabani ko rashin fahimta,ni aisha har abada ina son qauye ina taqama da shi saboda shine asalin kowanne dan adam koshi waye saidai idan shi din ya zama kaza ce ci ka goge bakinka" wadannan kalamai su suka sauka cikin kunnuwan khalipha da asma'u dake shirin ficewa a wajen,kamar zata tanka saita tuna hamid data bari yana jiranta kada ranshi ya baci yayi tafiyarsa,hakan ya sanya ta waiwayowa ta kalleta da niyyar bata gargadi,sai kuma tayi rashin sa'a idanun ayshan bai kanta ta sanyasu tsakiyar tafin hannunta kamar mai qayyade adadin jijiyoyin dake kaiwa hannun nata jini da dawo da shi,dole ta juya ta fice ba tare data samu damar maida raddi ba.
Wani irin abu shi ya shiga kaiwa da kawowa cikin zuciyarsa idanunshi a kanta,karon farko da ya yiwa wata mace kallon qurilla tsahon girmansa
"Bana buqatar sanin ko ke wace ce?....ki riqe tarihin rayuwarki naki ne."jiqaqqun idanunta da suka jiqa har gashin idanunta suka qara fito da tsahonsu da baqinsu
"Ya zama dole kasan wace aysha matuqar zaka karbi aure na....rashin sanin wace ce ni ya ta'allaqa ne da hukuncin daka yanke wa karbar aurenmu"
"Kinsan waye daddy kuwa a wajena?,kinsan me ya taba yiwa rayuwata?"
"Kamar yadda bakasan waye ba a wajena da abinda ya yiwa tawa rayuwar yake kuma kan yi mata....indai haka ne dole kasan wace ni" ta fada hawayen idonta naci gaba da zuba.
"Suna na aishah umar sanda,hafaffiyar wani qauye cikin qaramar hukumar takai dake jihar kano takai,mahaifiyata sunanta naja'atu,mahaifina cikakken bafulata ni ne,hakan ya sanya sunansa na asali ya bata saidai a kirashi da baffale,mahaifiyata kuwa 'yar manoma ce amma dukkansu mazauna qaramar hukumar takai ne,duk da irin wakaci ka tashin dake faruwa tsakanin manoma da makiyaya amma haka Allah ya qaddara aurensu,saidai irin abubuwan dana dinga gani bayan an haifeni na soma girma nasan cewa ba qaramin kai ruwa rana akayi da iyayen baffana ba kafin su yarda ya auri ummi na.
Ni kadai mahaifina ya haifa har ya rasu,nayi wata iriyar rayuwa daga tashina zuwa girmana,wanda tunda na girman baisan wani abu waishi qauna tausayi ko jin qai ba,bansan soyayya ba,bansan lallashi ba,bansan kula ba,rana tsaka na tashi na girma na gani a matsayin 'YAR TSAKAR GIDA,da wahala na budi ido,da bauta na saba,da bin umarni ko hani nake aiki koda yaushe,babu mai cemin sannu,babu me cemin na gode,babu me cewa me yake damunki,babu mai cewa me kikeso meye bakya so?,mahaifiyata ta bar gidan ta barni da qananun shekaru,ta barni tun bani da wayo sanin ciwon kaina,bana ce ga abinda ya faru ba don bani da masaniya,a hannun kakata inna yelwa ta barni,saidai kuma hakan a baki kawai yake,mahaifina yana da yayye uku qanne hudu,dukkansu cikin gidan suke suda matansu da 'ya'yansu,duk cikinsu babu mai mace daya,daga mai biyu sai mai uku,ga tarin yara da suke da shi,tunda na tashi nafi kowa rashin gata cikin gidan,kusan a tsakar gida nake qare rayuwata,hakanan duk wani aikin wahala na gidan yana wuya na,nice lungun baba auwalu,nice lungun baba sani,nice lungun baba salisu,nice na baba rabi'u,khamisu tasi'u,sabi'u,babu wanda ban gararamba a lungunsa yaransu na zaune,kuma ban isa nayi kuskure ko inyi ba dai dai ba,yadda akeso haka zanyi komai sauqi komai wuya,ba ruwansu da zafi sanyi rani da damina,kuma kakata tana kallo,asali ma sai na lura da babu abinda ya shafeta,ita kanta idan ta kama sai ta jani ta daka iya son ranta,duk cikin jikokinta ni tafi tsana,duk wanda zai hukunta ni koda hukuncin yafi girman abinda na aikata din ba damuwarta bane,saidai ta tayasu ma da jifana da miyagun kalmomi kala kala
"Shegiya ta gado baqin hali irin na gidansu uwarta naja,tur da jinin gidan saluhu,jinin fitsara jinin kafirar zuciya" wannan kalmar tun ban fahimtar me take nufi har nazo na ganeta,na kuma haddace ta ta zauna daram a kaina,bansan me nayi musu ba,bansan wanne girman laifi ne dani cikin gidan ba da kowa bai qaunata,yaqi jinina,tsangwamar bata tsaya iya cikin gidanmu ba,koda sauran mutane sai suke min abinda suka ga dama ganin bani da wani tsayayye wanda zai tsayan,ko cikin yara sa'anni na ina cin duka,kyara da tsangwama,musamman daya zamto nafi kowa qazanta na kuma fi kowa rashin gata,a lokacin mahaifina yana raye,bashi da abin cewa duk da cewa shima na lura bai wani damu dani sosai ba,yafi nuna kulawa ga sabuwar matarsa mai suna kuluwa,zuwan kuluwa gidan sai ya sake zama tamkar sabuwar babin azaba ne a tare da ni,yar kulawar da baba na ke nunawa kaina sai na rasa,ta janye hankalinsa tsaf,hakanan hatta da kakata ta koma qarqashin iko da mulkin kuluwa,a da babana kan zauna dani mu danyi hira,yakan yawaita cemin na yafe masa,zuwan kuluwa gidan da komawar inna yelwa qarqashin ikonta sai ya haddasa sababbin jam'iyyu kala kala a gidanmu da kuma kishin bal bal mai azabar zafi a tsakanin faccalolin,nidai a sannan bani ga tsuntsu bani ga tarko,ta rayuwata nake,duk inda na tattala ta sai anga an rushe,walau baba kuluwa ko sauran faccalolinta,kowa yagata yake figata yake,ina da son tsafta,ina son karatu kaman me,ina son gayu amma duka sun gagareni,duk da kaf cikin yaran gidan babu wanda ya damu da karatun saini daya,walau arabi ko boko,kuma babu wandaya matsanta musu kan hakan,son karatu na sai ya zama kamar wani sanabe ne ko iyayi ne a ganinsu da ganin ina nuna ai ni nafi kowa,hakan yasa aka qara qaimin datsemi duk wata qofa ta ilimi,tun sallar asuba idan na tashi nake bauta cikin gidan ba wanda ya damu da tsaftata ci na sha na suturata ko karatuna har dare ya shiga sannan ya maida haqarqarina na kwanta,da qyar nake samun sauran abinci naci ko sau biyu ne kacal a rana,haka zan hada guntu guntunsu duk lalacewarsa naci,watarana na kwana tsakar gida gefan dakin inna yelwa,watara na na kwana gefan turken awaki idan ta koreni daga qofar dakinta,watarana kuma ta barni daga cikin dakin nata amma daga bakin qofa komai sanyi komai damuna,kayan sawata kuwa a wani tsohon kwandon qarfe na shara suke,idan damina ta sauka haka zasuyita jiqewa ina matsewa ina shanyawa,dama gashi ba cikakken wanki suke samu ba.
Wani abu da Allah ya doramin shine son mahaifiyata da qulafucinta,saidai abinda ya soma girgixa hankalina fiye da dukkan abinda yake faruwa dani shine...." Tsinkewa maganar tayi daga harshenta,saboda wani daci da abu mai tauri daya riqe mata maqoshi,kuka nason kufcemata,aduk sanda ta tuna wannan gefan na rayuwarta bata iya jurewa
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_