Sashe 86
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari da daddare ma ya sake daukarta suka fita,wani katafaren shago dake saida tufafi irin na igbo da yoruba ta rakashi,sai ya nade hannu yace ta zabi duk abinda taga ya dace,ga zatonta yana nufin shi zata zabarwa,haka tayi ta maza ta zaba mishi kaya masu kyau da quality,harshi kansa mai shagon ma mamakin tasan kan kayanne?,murmushi kawai tayi,inda daga qarshe ta daukawa anni wasu kaya da suka burgeta sosai,dubanta kawai yayi baiga abinda ta dauka ba,saiya karbi accnt num din wajen ya musu transfer fiye da kudin siyayyarsu,tana gaba yana biye da ita a baya,ya bude mata murfinm motar cikin jin nauyin yadda yake matan ta shiga ta zauna,don ko yaranshi bai bari su bude matan shi da kanshi yake hakan,sai daya rufe murfin motar sannan ya koma cikin shagon.
Tsahon mintina goma cikakku aka sake kawo wata ledar sannan ya shiga aka tada motar suka bar wajen.
Nesa dashi kadan ta kwanta,saboda tana tuna yadda suka kwana jiya,batasan yadda akayi ta kwana a jikinsa ba,saida suka tashi sallar asuba sannan ta ganta cikin jikinsa kanta kwance saman qirjinsa,hakanan shima ya shirya yana dan dubanta,gefe daya shima ya kwanta idanunsa lumshe,yana tuna baccin da sukayi mai nauyi jiya wanda ya jima rabonshi da bacci mai nauyi irinsa,da haka bacci ya kwashesu.
Qarfe sha daya na safe suna tsaye cikin airphort,aysha na gefan khalipha,tayi kyau cikin baqar abaya,kusan shigar baqi tayi komai nata har gilashin fuskarta,wanda hakan ya sake bayyana kyau da hasken fatarta,kota ina khalipha gani yake kamar kowa ma kallonta yake saboda kyan data yi masa,dalili kenan daya sanya yaranshi suka karesu a dabarance ta yadda ayshan ba zata fuskanci me yake nufi ba,daidai lokacin da asma'u itama ke tsaye cikin tashin hankali suna sa'insa da daya daga cikin ma'aikatan wajen,kano takeson komawa a yau amma ana gaya mata cewa ticket ya qare,tana jin kuma ya zama dole ta koma a yau din,sakamakon kayanta da abba ya auno mata daga china donta fara business da suka zo,tazo clearance amma tag number dinta ya fadi,kuma ta tabbatar koda kayanta zasu fitan sai taci wuya,shi yasa take gaggawar komawa ta sanar da abba,don ta saka rai da kayan,hakanan ta gama bazawa qawaye da sauran jama'a,kada mu su rainata su dauka qarya take.
Ganin da gaske suke saidai ta bi jirgin gobe ya sanyata cikin bacin rai da qunaquni ta soma takawa zata bar wajen,duk abinda ke faruwa khalipha na ankare,gab da zata gotasu ya dan taka kadan ya matsa inda zata iya ganinshi
"Mrs dan gote" ya fadi hannayensa harde a qirjinsa kamar yadda yake al'adarsa ce,waiwayowa tayi taga wace matar dan goten,sai suka hada ido da khalipha,ta fuskanci da ita yake don ita yake kallo yana murmushi,gabanta ya fadi,kwarjininsa suka cikata,wani kyau taga ya qara mata fiye da yadda ta sanshi a baya
"Ki nemi taimako wajen madam,kamar akwai kujera daya data rage sai tasa a baki kawai" ya fada cikin idont care tune,hararashi taso yi saboda wani takaici daya taso mata,kamar ita zata nemi taimako wajen aysha Allah ya sawwaqe,aisai ta rainata ma,har abada bata jin zata iya yin hakan,sai kawai ta soma takawa zata bar wajen,dai dai sanda idanunta ya hango mata aysha dake zaune idanunta kan wayarta,gabanta ne ya fadi ta tsura mata ido tana kallonta kafin daga bisani ta dauke kai ta wuce,tana fita ta kira abba,saidai ya gaya mata zaiyi iyakar iyawarsa,baida mutane a wajen amma zai gwada,kashe wayar kawai tayi cikin bacin rai,asara ce tasan zasu tafka ta koda kayan sun fito,bata da wani babba data sani da zai shige mata gaba saidai abban,kuma shima yadda yake mata bayani kamar abun zaija lokaci.
Zuciyarta ta bata shawarar ta koma wajen khalipha,to amma itakam gaskiya bata son tayi abinda mutuncinta zai zube,don haka sai ta koma can wani waje da zata iya hangosu,idanunta na gano mata aysha,ta dubi securityn dake tare dasu,haushi da baqinciki gami da takaici ya dinga sakko mata,ba shakka aysha ba itace ta cancanci wannan matsayin ba,ita asma'u ita ta dace dashi,ayshan da batasan dadin komai ba,batasan wani gata ba,bata san so ko qiyayya ba,bata damu da komai ita ta samu wannan bigiren daya kamata ace ita ke ciki?,aysha da masu irin hamid suka dace,ya akayi ma wai ta hadasu ne da khalipha?,ya akayi bata qyaleta ta zabi wani daban da kanta ba,anya ma ba ta san cewa waye ainihin khalipha ba?,anya ba bincike tayi a kansa ba shi yasa tayi laqwas ta qyale har akayi auren?.
Tana zaune tana karanta wannan wasiqar jakin har lokaci ya fara nisa,ta duba agogon wayarta,ba shakka.nan da wasu mintuna jirgin da zai nufi kano zai tashi
"Kije kawai asma'u,ai itama tasan kinfi qarfin roqar duk wani abu daga gareta,koda kin roqa dinma aiku kuka fara mata alfarma kafin tayi muku,banda ku da tunu yanzu qila tana can cikin wani mawuyacin halin da ba'asan ma wanne iri bane,kai gaba daya ma auren nata ai kece silarshi,da wannan shawarar da zuciyarta ta bata ta miqe ta doshi inda aysha ke zaune khalipha na dan tsaye daga bayanta yana amsa waya,bayan ya gama ya tsaya siyen ticket qwaya daya daya rage ta internet.
Tana gab da isowa wajen aysha ta daga kanta saboda gajiya da tayi da danna wayar,tayi haka ne saboda nauyin kallon da khalipha ke binta dashi,sam baya jin kunyar ma yaranshi dake tsaye a wajen,murmushi ta jefi asma'un dashi cikin fara'a tace
"Ah,anty asma'u?,kema kin shigo legos kenan?,hala keda ya hamid ne?ku bata wuri sisterna ce" tayi magana dasu wanda ada basu da niyyar matsawa,fuska a dinke ta qaraso wajen,sai taji kaman ayshan tana sane da tace tare da hamid suke magana ta gaya mata a fakaice
"Zuwa nayi na tafi da kayana da nayi order daga china,so an samu dan minor problem kuma hamid bai qasar bare yayi magana a sakar min,so ban sani ba ko mijinki nada wanda zaima magana akan hakan saboda yau nakeson komawa gida"murmushi ta saki ganin yadda take magana kai tsaye cikin isa isa,amma kona komai tasan ta isa dinne shi yasa harta tako ta nemi alfarma a wajenta,tasan halin asma'un tsaf ciki da bai,ba kowane zata nemi alfarma a wajensa ba saboda tsabar jin kanta da takeyi
"shikenan minti daya" ta fada tana miqewa,a hankali take takawa inda khaliphan ke tsaye yana danne danne da waya ahannunsa,yayin da asma'un ta bita da kallo tana qarewa shigarta kallo,ko hasidin iza hasada yaga aysha yasan ta canza,yanzu classic aysha ce,ba irin ayshan daka sani a baya ba,gefanshi ta qaraso wanda kaman yana ankare dama da tahowarta din yana jin tsaiwarta ya waiwayo yana dubanta bayan ya zuba mata dukkan idanunshi da sukayi mata nauyi,batasan me yasa yake tasiri haka a kanta ba,saita dan sadda kai
"Asma'un kika zo nemawa alfarma?" Ya tambayeta ta wata irin siga da bata gane meye cikin ranshi ba,bata ankara ba taji ya saqalo hannunta cikin nashi cikin wani salo ya soma takawa tilas tabishi.
Gaban asma'un suka tsaya sannan ya soma magana cikin muryarshi mai cike da izza da kwarjini
"Kin nemi alfarma but bata hanyar data kamata ba,yanayin yadda kika yi mata magana baiyimin ba,baya ga haka ma banajin yaron oga zai iya komai akan hakan,dadai ogan nashi yana nan wataqila saiya roqa miki shi,ko kawai ta jirayi dawowar mai gidan nata,may be ma he can do morethan i can" daga kai aysha tayi da sauri tana kwabe fuska tana dubanshi tana girgiza kai,sai yaga tayi mishi kyau sosai,girarshi ya dage mata alamin baiga wani kuskure da yayi ba,yatsansa ya saka yadan taba girarta data tattareta waje daya can qasa yace
"You r beautiful" sai ta saki fuskar tata daga tattaretan da tayi ta koma yi masa kallon mamaki,tuni asma'u dake zaune wani abu ya yunquro mata,sun wani tsaya gabanta suna mata soyayya sai kace kansu aka saukar da wahayinta,dadin abun tun kafin ayi d'aran akai kwand'i,yaushe ma suka fara son junansun,taso ta miqe tabar wajen bayan ta gaggaya musu magana saidai kuma ta tabbatar idan tayi hakan ta barar da damarta,tasan da biyu khalipha ke gaya mata magana saboda babu kalar wulaqancin da itama bata yi masa ba.
Murya can qasa kamar mai rada aysha tayi masa magana don batason asma'u taji
"Kayi mata wannan alfarmar domin girman Allah" wata kasala sosai sautin furucinta ya haifar masa dashi,wanda hakan ya sanyashi lumshe idanunsa ya bude duka lokaci guda
"Taci darajar aisha" kunya taji tadan kamata saita basar,wayarshi ya ciro
"Morning boss" daga daya bangaren kakkaurar muryar ta cika wayar khaliphan
"Morning ahmad mun tashi lpy"
"Lpy lau boss....boss kayi wuyar gani,koda yake manya dama haka kuke irinmu saida haquri kafin mu samu ganinku" murmushi khaliphan ya dan fidda mai sauti
"Kullum qorafinka kenan,bayan daka tashi nemana kasan yadda za'ayi ka hadu dani ai.....ba wannan ba,akwai wata yarinya.....ya sunanta ma yake?" Ya qarashe da low tune yana duban aysha da alama tambayarta yake ta gaya mishi,kunya ta sauko ta rufe ayshan,yana nufin yace ya manata sunan asma'un?,saita gaya masa kawai tana dakewa,bata yarda ta dubi asma'un ba ta share kawai,bayani ya masa bai qarasa bama ahmad din ya tsaidashi kan cewa ba matsala,yanzu za'a duba kayan nata ai tafi qarfin komai,dai dai sanda ya qare wayar lokacin tashinsu yaui,saboda haka ya maida wayar aljihunsa yana cewa
"Saiki gaya mata ta wuce ta tafi gida....mtsweeww,kome mijinta keyi oho" taji duk abinda ya fada,duk yadda ranta yakai ga baci haka ta hadiye,don a yadda ta karanci khaliphan tsaf zai fasa abinda yayi niyya,wanda hakan yana dai dai da tayi asara ne kota jira har daddy yayi mata cuku cuku,hakanan ta miqe tabi bayansu
47
_ga full 47 nan nayi editing na qara yawanshi,banson numbers din littafin yayi yawa,idan na samu damar qara wani anjima zaku jini in sha Allahu_
Cikin jirgin ma daga kujerarsa saita aysha,hakan ya bashi damar samun kusanci sosai da ita,yayin da asma'u ke zaune can baya,duk wani motsinsu idanunta na kai,yana sane yake sake narkewa ayshan,yayin da kunya ta cikata,gaba daya khaliphan ya canza tun daga zuwansu legos zuwa yau.
Tsahon mintina goma cikakku aka sake kawo wata ledar sannan ya shiga aka tada motar suka bar wajen.
Nesa dashi kadan ta kwanta,saboda tana tuna yadda suka kwana jiya,batasan yadda akayi ta kwana a jikinsa ba,saida suka tashi sallar asuba sannan ta ganta cikin jikinsa kanta kwance saman qirjinsa,hakanan shima ya shirya yana dan dubanta,gefe daya shima ya kwanta idanunsa lumshe,yana tuna baccin da sukayi mai nauyi jiya wanda ya jima rabonshi da bacci mai nauyi irinsa,da haka bacci ya kwashesu.
Qarfe sha daya na safe suna tsaye cikin airphort,aysha na gefan khalipha,tayi kyau cikin baqar abaya,kusan shigar baqi tayi komai nata har gilashin fuskarta,wanda hakan ya sake bayyana kyau da hasken fatarta,kota ina khalipha gani yake kamar kowa ma kallonta yake saboda kyan data yi masa,dalili kenan daya sanya yaranshi suka karesu a dabarance ta yadda ayshan ba zata fuskanci me yake nufi ba,daidai lokacin da asma'u itama ke tsaye cikin tashin hankali suna sa'insa da daya daga cikin ma'aikatan wajen,kano takeson komawa a yau amma ana gaya mata cewa ticket ya qare,tana jin kuma ya zama dole ta koma a yau din,sakamakon kayanta da abba ya auno mata daga china donta fara business da suka zo,tazo clearance amma tag number dinta ya fadi,kuma ta tabbatar koda kayanta zasu fitan sai taci wuya,shi yasa take gaggawar komawa ta sanar da abba,don ta saka rai da kayan,hakanan ta gama bazawa qawaye da sauran jama'a,kada mu su rainata su dauka qarya take.
Ganin da gaske suke saidai ta bi jirgin gobe ya sanyata cikin bacin rai da qunaquni ta soma takawa zata bar wajen,duk abinda ke faruwa khalipha na ankare,gab da zata gotasu ya dan taka kadan ya matsa inda zata iya ganinshi
"Mrs dan gote" ya fadi hannayensa harde a qirjinsa kamar yadda yake al'adarsa ce,waiwayowa tayi taga wace matar dan goten,sai suka hada ido da khalipha,ta fuskanci da ita yake don ita yake kallo yana murmushi,gabanta ya fadi,kwarjininsa suka cikata,wani kyau taga ya qara mata fiye da yadda ta sanshi a baya
"Ki nemi taimako wajen madam,kamar akwai kujera daya data rage sai tasa a baki kawai" ya fada cikin idont care tune,hararashi taso yi saboda wani takaici daya taso mata,kamar ita zata nemi taimako wajen aysha Allah ya sawwaqe,aisai ta rainata ma,har abada bata jin zata iya yin hakan,sai kawai ta soma takawa zata bar wajen,dai dai sanda idanunta ya hango mata aysha dake zaune idanunta kan wayarta,gabanta ne ya fadi ta tsura mata ido tana kallonta kafin daga bisani ta dauke kai ta wuce,tana fita ta kira abba,saidai ya gaya mata zaiyi iyakar iyawarsa,baida mutane a wajen amma zai gwada,kashe wayar kawai tayi cikin bacin rai,asara ce tasan zasu tafka ta koda kayan sun fito,bata da wani babba data sani da zai shige mata gaba saidai abban,kuma shima yadda yake mata bayani kamar abun zaija lokaci.
Zuciyarta ta bata shawarar ta koma wajen khalipha,to amma itakam gaskiya bata son tayi abinda mutuncinta zai zube,don haka sai ta koma can wani waje da zata iya hangosu,idanunta na gano mata aysha,ta dubi securityn dake tare dasu,haushi da baqinciki gami da takaici ya dinga sakko mata,ba shakka aysha ba itace ta cancanci wannan matsayin ba,ita asma'u ita ta dace dashi,ayshan da batasan dadin komai ba,batasan wani gata ba,bata san so ko qiyayya ba,bata damu da komai ita ta samu wannan bigiren daya kamata ace ita ke ciki?,aysha da masu irin hamid suka dace,ya akayi ma wai ta hadasu ne da khalipha?,ya akayi bata qyaleta ta zabi wani daban da kanta ba,anya ma ba ta san cewa waye ainihin khalipha ba?,anya ba bincike tayi a kansa ba shi yasa tayi laqwas ta qyale har akayi auren?.
Tana zaune tana karanta wannan wasiqar jakin har lokaci ya fara nisa,ta duba agogon wayarta,ba shakka.nan da wasu mintuna jirgin da zai nufi kano zai tashi
"Kije kawai asma'u,ai itama tasan kinfi qarfin roqar duk wani abu daga gareta,koda kin roqa dinma aiku kuka fara mata alfarma kafin tayi muku,banda ku da tunu yanzu qila tana can cikin wani mawuyacin halin da ba'asan ma wanne iri bane,kai gaba daya ma auren nata ai kece silarshi,da wannan shawarar da zuciyarta ta bata ta miqe ta doshi inda aysha ke zaune khalipha na dan tsaye daga bayanta yana amsa waya,bayan ya gama ya tsaya siyen ticket qwaya daya daya rage ta internet.
Tana gab da isowa wajen aysha ta daga kanta saboda gajiya da tayi da danna wayar,tayi haka ne saboda nauyin kallon da khalipha ke binta dashi,sam baya jin kunyar ma yaranshi dake tsaye a wajen,murmushi ta jefi asma'un dashi cikin fara'a tace
"Ah,anty asma'u?,kema kin shigo legos kenan?,hala keda ya hamid ne?ku bata wuri sisterna ce" tayi magana dasu wanda ada basu da niyyar matsawa,fuska a dinke ta qaraso wajen,sai taji kaman ayshan tana sane da tace tare da hamid suke magana ta gaya mata a fakaice
"Zuwa nayi na tafi da kayana da nayi order daga china,so an samu dan minor problem kuma hamid bai qasar bare yayi magana a sakar min,so ban sani ba ko mijinki nada wanda zaima magana akan hakan saboda yau nakeson komawa gida"murmushi ta saki ganin yadda take magana kai tsaye cikin isa isa,amma kona komai tasan ta isa dinne shi yasa harta tako ta nemi alfarma a wajenta,tasan halin asma'un tsaf ciki da bai,ba kowane zata nemi alfarma a wajensa ba saboda tsabar jin kanta da takeyi
"shikenan minti daya" ta fada tana miqewa,a hankali take takawa inda khaliphan ke tsaye yana danne danne da waya ahannunsa,yayin da asma'un ta bita da kallo tana qarewa shigarta kallo,ko hasidin iza hasada yaga aysha yasan ta canza,yanzu classic aysha ce,ba irin ayshan daka sani a baya ba,gefanshi ta qaraso wanda kaman yana ankare dama da tahowarta din yana jin tsaiwarta ya waiwayo yana dubanta bayan ya zuba mata dukkan idanunshi da sukayi mata nauyi,batasan me yasa yake tasiri haka a kanta ba,saita dan sadda kai
"Asma'un kika zo nemawa alfarma?" Ya tambayeta ta wata irin siga da bata gane meye cikin ranshi ba,bata ankara ba taji ya saqalo hannunta cikin nashi cikin wani salo ya soma takawa tilas tabishi.
Gaban asma'un suka tsaya sannan ya soma magana cikin muryarshi mai cike da izza da kwarjini
"Kin nemi alfarma but bata hanyar data kamata ba,yanayin yadda kika yi mata magana baiyimin ba,baya ga haka ma banajin yaron oga zai iya komai akan hakan,dadai ogan nashi yana nan wataqila saiya roqa miki shi,ko kawai ta jirayi dawowar mai gidan nata,may be ma he can do morethan i can" daga kai aysha tayi da sauri tana kwabe fuska tana dubanshi tana girgiza kai,sai yaga tayi mishi kyau sosai,girarshi ya dage mata alamin baiga wani kuskure da yayi ba,yatsansa ya saka yadan taba girarta data tattareta waje daya can qasa yace
"You r beautiful" sai ta saki fuskar tata daga tattaretan da tayi ta koma yi masa kallon mamaki,tuni asma'u dake zaune wani abu ya yunquro mata,sun wani tsaya gabanta suna mata soyayya sai kace kansu aka saukar da wahayinta,dadin abun tun kafin ayi d'aran akai kwand'i,yaushe ma suka fara son junansun,taso ta miqe tabar wajen bayan ta gaggaya musu magana saidai kuma ta tabbatar idan tayi hakan ta barar da damarta,tasan da biyu khalipha ke gaya mata magana saboda babu kalar wulaqancin da itama bata yi masa ba.
Murya can qasa kamar mai rada aysha tayi masa magana don batason asma'u taji
"Kayi mata wannan alfarmar domin girman Allah" wata kasala sosai sautin furucinta ya haifar masa dashi,wanda hakan ya sanyashi lumshe idanunsa ya bude duka lokaci guda
"Taci darajar aisha" kunya taji tadan kamata saita basar,wayarshi ya ciro
"Morning boss" daga daya bangaren kakkaurar muryar ta cika wayar khaliphan
"Morning ahmad mun tashi lpy"
"Lpy lau boss....boss kayi wuyar gani,koda yake manya dama haka kuke irinmu saida haquri kafin mu samu ganinku" murmushi khaliphan ya dan fidda mai sauti
"Kullum qorafinka kenan,bayan daka tashi nemana kasan yadda za'ayi ka hadu dani ai.....ba wannan ba,akwai wata yarinya.....ya sunanta ma yake?" Ya qarashe da low tune yana duban aysha da alama tambayarta yake ta gaya mishi,kunya ta sauko ta rufe ayshan,yana nufin yace ya manata sunan asma'un?,saita gaya masa kawai tana dakewa,bata yarda ta dubi asma'un ba ta share kawai,bayani ya masa bai qarasa bama ahmad din ya tsaidashi kan cewa ba matsala,yanzu za'a duba kayan nata ai tafi qarfin komai,dai dai sanda ya qare wayar lokacin tashinsu yaui,saboda haka ya maida wayar aljihunsa yana cewa
"Saiki gaya mata ta wuce ta tafi gida....mtsweeww,kome mijinta keyi oho" taji duk abinda ya fada,duk yadda ranta yakai ga baci haka ta hadiye,don a yadda ta karanci khaliphan tsaf zai fasa abinda yayi niyya,wanda hakan yana dai dai da tayi asara ne kota jira har daddy yayi mata cuku cuku,hakanan ta miqe tabi bayansu
47
_ga full 47 nan nayi editing na qara yawanshi,banson numbers din littafin yayi yawa,idan na samu damar qara wani anjima zaku jini in sha Allahu_
Cikin jirgin ma daga kujerarsa saita aysha,hakan ya bashi damar samun kusanci sosai da ita,yayin da asma'u ke zaune can baya,duk wani motsinsu idanunta na kai,yana sane yake sake narkewa ayshan,yayin da kunya ta cikata,gaba daya khaliphan ya canza tun daga zuwansu legos zuwa yau.