← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 114

Sashe 58

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Katsam saiga anni a kitchen din ta shigo riqe da wani jug a hannunta,cikin ban girma aysha ta miqe ta amshi jug din daga hannunta tana shirin gaidata annin tace
"Aysha harkin tashi?"
"Ai hajiya ta jima a zaune a nan tana kallon aikin girki"kallonta annin tayi
"An tashi lafiya ya baqunta" kamar zata nutse haka taji,ita annin ke gaidawa,russunawa tayi sosai ta gaidata ta amsa tana jin dadi a ranta,kallon daya daga cikin masu aikin tayi
"Atika karbi jug din ki hadamin wani,kinsan ina gama cin abinci nake sha"
"Toh hajiya...da alama kinji dadin jikinki"
"Sosai ma...kedai Allah ya biyaki"
"Ameen hajiya" ta fada cikin farinciki
"Bari naje nadan watsa ruwa kafin sarakan baccin su tashi muyi break"
"A fito lafiya" aysha ta fada cikin girmamawa annin ta amsa sannan ta juya ta fice.

Inda ta tashi ta koma ta zauna tana kallon atika na yin wasu hade hade cikin jug din,ta gane me take hadawar saidai taga kamar akwai kura kurai a ciki,taso yin shuru sai kuma ta kasa
"Ko zaki dan aramin jug din kadan naga ko na iya hadawa?" Waiwayowa tayi tana duban ayshan tana murmushi
"Kai hajiya wannan hadin mutanen qauye mu muka fi saninshi ai,ina ku kuma ina qauye" murmushi tayi kawai tana saukowa daga saman kujerar da take kai ta nufi inda take
"Ba wanda bashi da qauye...duk wanda yace baida qauye ka tuntubi asalinsa" sosai zancan ya yiwa atika da sauran biyun dadi,basu zaci haja daga gareta va,sun saba ganin qyama da kallon banza daga gun duk baquwar fuskar data zo gidan,abinda ke kwantar musu da hankali da sake basu qwarin gwiwar zama da mutanen gidan shine basu taba jin ko ganin maganar banza ba daga wajensu

Cikin minti goma kacal ta gama hadawa,atika duka na kallonta cikin mamaki
"Kai hajiya....ya akayi kika iya wannan hadin kamar ma yafi nawa kyau?" Murmushi kawai ayshan tayi ba tare data bata amsa ba,kusan tasan magunguna sosai,saboda inna yelwa tayi sana'ar saidasu kala kala,kuma babu maiyin wahalar sai ita,wani lokaci ma ita ke shiga jeji ta sassaqo abinda ya kamata,ta gada ne itama daga wajen mijinta wato kakan ayshatu bayan rasuwarsa,wanda ya rasu ne tun kafin a haifi umminta.

Tana aje jug din rahama na shigowa cikin kitchen din,ta tsuke cikin shirt da dogon skert tana takawa dai dai,ganinta duk sai su atika suka nutsu,suka soma gaidata tana amsawa dai dai tare da cewa
"Ku samamin wani abun,duka abinda kuka dafa din yau bana jin cinshi" kai aysha ta daga tana dubanta cikin mamaki,a qalla an dafa abu yakai uku kuma duka tace babu na cinta a ciki?,idanunta ne ya sauka kan ayshan,ta dan kalleta na minti biyu,yanayin halittarta tayi mata sosai,ta yabawa tsarinta saidai tana kishinta
"Amaryarmu...ya da fitowa da safe haka?,ke daya kika bar angon naki?"
"Tare muka fito nina rakota saboda ta damu taga anni,komawa nayi in dauko wasu takardu dana manta" muryar khalipha ta ratso kitchen din a sanda take takowa zuwa kitchen din,cikin yadin kufta baqi wanda iyakar rigar qasan gwiwa sai dogon hannu da take da shi,aikin sarauta aka yi masa sosai wanda ya dace da hula dara dake kansa,ba qaramin kyau suka yi masa ba,sai ya tashi tamkar wani jinin sarauta,kwarjininsa ya qaru sosai,sunkui da kansu atika sukayi sannan suka rusuna suna gaidashi,ya amsa musu suka lalubi qofa suka fice,kitchen din ya rage saura su uku,hannyensa harde a qirji ya zubawa rahama ido,wanda a take ya ladabtar da ita,ta dauke kanta tana basarwa
"Princess" yayi qarfin hali fada yana duban aysha,sai tayi wuri wuri da ido cikin mamaki da tambayar kanta dawa yake,hakan sai yayi kama da kamar ta kada mishi idanunta ne a ganin rahama,hannunshi ya miqa mata yana cewa
"Muje muyi break anni tace na kiraki" dubanshi take,ta fuskanci abinda yake nufi,amma sai take jin ba zata iya ba,har yanzu kallonta yake yana fatan ta dago abinda yake nufi ko don rahaman,iya matakin da zai dauka a kanta kenan ta rage sawa rayuwarsa ido da matsanta masa,ganin ayshan nason karya plan din sai kawai ya saqalo tafin hannunta ya janyota zuwa kusa da shi tamkar zasu hade,sannan ya soma takawa ba shiri itama tabi sahunsa yana fadin
"Rahaman kike jin kunya....idan baquwarki ce toni ba baquwata bace...muje kici wani abu na lura bakison cin komai,bana son wannan baquntar taki fa" da idanu rahama ta bisu ranta na suya,bata taba sanin haka khalipha yake ba sai yau,ashe duk sauqin kanshi da take gani da sakin fuska ta wani fannin baida kirki,ita zaiwa haka?"qwalla ce ta cika mata ido tayi hanzarin maida ta,a hankali ta soma takawa tabi bayansu,ta fasa canza abun karin,zama taci ko meye.

Gab da zasu isa qofad da zata sadasu da ainihin falon taso ta zame hannunta,turasu yayi ita da shi cikin wani daki wanda sai da suka shiga taga store ne na kayan abinci,idanu ya tsareta da shi sannan ya soma cewa
"Na gaya miki tun ranar farko ni dake,karkiyi wani abu da zai saka baqin fuskar dake yawan zuwa gidan nan su dora ayar tambaya a kanki ko akanmu,ke matata ce wadda na aura saboda ina sonta,ta aureni auren 'yanci da soyayya kuma akan radin kanta,a haka kike a idon family na....kiyi qoqarin ci gaba da kasancewa a haka,bana son ki bada qofar zargi" kalma ta qarshe data shiga kunnen rahama kenan wadda tazo wucewa,tsai tayi tana jira ko zata sake jin wani abu,saidai ba abinda khaliphan ya sake cewa,illa handkherchief daya ciro daga aljihunsa ya miqawa ayshan yana cewa
"Goge hannunki da kyau,baki tsaya kin wanke ba muka fito,ga gefan fuskarki ma ya dan baci kadan" a sanyaye ta saka hannu ta karba ta goge duk inda yace din,gefan bakinta ne kawai bai gama goguwa da kyau ba,dole ya karba ya sake matsawa gabanta kadan yasa handkherchief din akan yatsanshi ya soma goge mata,numfashinsu ne ya soma gauraya da juna saboda kusancin da hakan ya kawo tsakaninsu,idanunta ta daga saita saukesu fes cikin na khaliphan,ja baya yayi da sauri kaman wanda aka jonawa shock,cikin aljihunsa ya saka handkherchief din sannan ya juya ya soma yunqurin ficewa,hakan ya sanya rahama qara wuta tabar wajen kafin su fito su cimmata.

Duk kowa na saman tebur din kusan kaman qarasowarsu ake jira,ja mata kujera yayi ta zauna kafin shima ya zauna,hakan ya yiwa anni dadi sosai,yayin da amal ta dauke ido zuciyarta kaman zata fito,rahama kam hararar khalipha take a fakaice,wanda ko giyar wake tasha tasan bata isa ta harareshi ba gaba da gaba,haidar ne ya soma gaidata sannan mus'ab,dukkansu ta amsa cikin fara'a da jin kunya,don dukkansu sun girme mata amma suke girmamata kamar itace gaba da su,shikam haidar ganin qimarta yake tun waccar rana a capteria,abinda tayi ya tabbatar masa ita din nutsatstsiyar macace,sai gata a amatsayin matar wanshi hakan ya masa dai dai,a nutse ake cin abincin babu yawan surutu kaman jiya,tsakiyar shurun muryar rahama ta ratso
"Ya kamata amarya ki fadi abincin da kika fiso tunda kin shigo cikin iyalin da kowanne lokaci ake daukar abincin da kowa yafiso a girka"
"Karki damu....abun mamaki duka choice din anni akan abinci irin na aysha ne...." Ta wutsiyar ido aysha take satar kallonshi,itadai tasan basu taba magana makamanciyar haka ba,hasalima koda za'a titsiyeta batasan choice din anni ba a yanzu,dan sauya fuska rahama tayi sannan tace
"Haba ya khalipha...ka barta ta fadi da kanta mana...,wai haka ne?"murmushi ta saki wanda dan fitar sautinsa yasa khalipha daga kai ya dubeta sannan ya maida kan plate din gabanshi yaci gaba da juya abincinsa
"haka ne"ta bata amsa a taqaice,kafada ta daga tana tabe baki
"sai kace mutuniyar qauye?...."
"Suba mutane bane?,abincin da suke ci duka yafi namu lafiya,mu kusan duk kame kame muke,ko a qarfi idan kija hada yaron qauye saiya kada na birni guda uku shi kadai" anni ta bawa rahama amsa tana murmushi tare da son nusashsheta,sosai amsar ta yiwa aysha dadi ta kuma qarawa anni qima da martaba a idonta,khalipha ma yaji dadin hakan,saboda baison aysha tayi wani abu da zaisa rahama ta dauki haske kan wani abu daya shafeta ko ya shafi rayuwarta,daga haka bata qara tankawa ba kowa yaci gaba da cin abincinsa.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*KO KUMA*

07067124863

*DB*

33

Bayan sun kammala break din hira ta balle,wanda kusan haidar da mus'ab ne suka hada rudun,sun saka rahama gaba sai cakar da ita suke,itakam tayi kicin kicin don bata son raini,nan ma saida khalipha ya tsawatar,qarshe tashi tayi ya basu waje,amal itama ta miqe tana sauka qasa don zuwa kitchen ta samu ruwan da zata sha.

Mus'ab kewa anni qorafin motarsa tare da roqarta ta bashi daya cikin wanda ya khalipha ya bata,wasa qasa yake maganar saboda yadda khalipha ke harararshi "Shikenan....a baiwa diyata dayar,kai kuma ka dauki daya,amma fa aro..." Ta qarashe fada tana dubanshi,dan tsalle yayi kadan saboda yasan ta fadi ne kawai qarshe dai ta zama tashin halak malak
"Yes my anni!.....thank you" hannunshi khalipha ya saka a aljihu ya ciro muqullan mota yana fadin
"Kin tunamin kuwa anni....ina haidar...idan kun samu lokaci ko zuwa dare ne kuje ku dauko motarta dake wancan gidan...wacce zata yi amfani da ita kenan anni?"
"A debosu duka ta dinga hawa wadda takeso ko 'yata" kunya ce sosai ta kama aysha da wani irin nauyi,ita dako rage hanya ba'a qaunar ayi mata a rayuwa yau ita ake cewa ta dinga hawa mota bama daya ba har guda biyu?,itakam wacce irin qauna mutanen ne ke mata ne
"Allah ya saka da alkhairi ya jiqan magabata ya qara lafiya..na gode"
"Amin...amma babu godiya saboda tamkar 'ya kike kema,ku bata muqullanta ta soma hawa duk sanda takeso" dan dubanta khalipha yayi sannan ya maida dubanshi ga anni yana miqewa
"Banjin ta iya driving...."
"Faduwa tazo dai dai da zama....sai na koya mata kawai" mus'ab yayi hanzarin fada,harara khalipha ya maka masa wadda ta sanyashi ya nutsu sannan ya dubi anni
"Zan fita amma bazan jima ba zan dawo"a dawo lafiya suka yi masa gaba dayansu.
Chapter 58 · 0% Book details