Sashe 34
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi suka sakarwa juna sannan suka tako zuwa cikin gidan tare,gab da zasu shige sashen dakin ayshan sukayi kacibus da asma'un sanye da kayan bacci zata shiga kitchen,da alama yunwa ce ta tasheta,don tana iya kaiwa azahar a daki tana kwance kurum kamar ruwa,har ta gota sai ta dawo da baya tana duban aliya
"a'ah....anzo shirye shiryen bikin ne?" Ta furta cikin siga ta izgilanci tana dariya dariya
"Ai gwara a bada himma...mai kwarmin ido da wuri yake fara kukansa ko?,duk da yake ma a qauye za'ayi komai,ta kwana gidan sauqi" ta qarashe tana dariya,da sauri aysha ta matsa hannun Aliya tana mata nuni da kada ta kulata kenan,aliyan ta fahimci haka,saboda haka ta watsawa asma'un kallon banza sannan tace
"Kinci sa'a cikin gidanku nake.....ki tareni a waje" ta fada a zafafe tana jan hannun aysha sukayi gaba
"Ba komai....duk nasan meke damunku" ta fada tana dariya tayi kitchen,iska ta furzar daga bakinta bayan sun shiga dakin ayshan,bata iya zama ba ta dubi aysha
"Har yau wannan mara mutuncin tana nan tana iskancin nan nata....abun ma kamar gaba yake sakeyi saboda rashin taka mata burki da bakyayi ko?" Murmushi aysha ta saki tana gyara ma aliyan wajen da zata zauna bawai don akwai datti ko kaya a wajen ba
"Karki damu.....duk abinda take ba shine a gaba na ba...saboda baki taba gani an gutsuri naman jikina saboda haka ba....hasalima qimarta nake gani har kwanan gobe....saboda jinin daddy ce ita....daraja ba qarya bace...ko a lahira wani yana cin darajar wani....karkuma ki manta cewa ni din ba kowa bace....face yarinyar da hatta mahaifiyarta ta gujeta"ta qarashe cikin karayar zuciya
"wannan ba hujja bace" aliya ta fada hannunta riqe da qugunta tana kada kai
"Manta da wannan.....zauna muyi hirar yaushe gamo" ta fada tana murmushi tamkar ba abinda ke damunta a rayuwa,saidai can qasar zuciyarta tana jin tafi kowa matsala a rayuwa
"Ba hirar yaushe gamo zamuyi ba aysha....mu tattauna maganar dake gabanmu" ta fadi tana zama,yayin da ayshan ta yiwa kanta mazauni itama kusa da ita.
Kaf babu abinda ta boye mata ta zayyana mata komai,shuru ne ya ratsa dakin yayin da aliya ke hadiyar yawu idanunta fes kan fuskar ayshan
"Aysha..." Ta kirata still tana kallonta
"Na'am" ta amsa tana dubanta
"Kin gamsu har cikin ranki zaki auri wannan mutumin zaki zauna da shi?" Tayi mata shigen tambayar da khaliphan ya taba yi mata,kai ta jinjina don ta tabbatar idan tace bata so tsaf aliya zata rusa komai,to idan ta rusa dinma me zata zauna taci gaba da yi cikin gidan?,meye amfanin zamanta?,a gaba wa zata hadu da shi?,gwara wannan ya nuna alamu na tausayi a gareta
"Shikenan....addu'a zamu ci gaba da yi Allah yasa kin dace...ina fata kuma asma'u idan ma tayi da niyyar mugunta mugun abinta ya koma mata kanta,auren mai kudi ba shine dacewa ba,aurwn mai kudi ba shine samun kwanciyar hankalin gidan aure ba,auren mai kudi bai cikin manyan jigon dake sawa a auri namiji,ni'ima ce da idan Allah yaga dama zaiwa wanda yaga dama bawai don yafi sonka cikin halittarsa ba,hasalima ba kowa ke dacewa kan hakan ba,amma sashin abu daya bana son kice zaki rage na hidimar biki da akewa kowacce diya mace budurwa,don kema ita ce....saboda haka zamuyi komai kamar yadda akeyi" dariya aysha tayi ta karyar da kai tana duban aliya
"Kiyi haquri sashin karki dora min abinda bazan iya ba,wallahi Allah bana sha'awar yin komai....kin manta cewa muhalli kawai zan sauya ba wani abu ba....ni haka nake ji a jikina bawai aure zanyi ba"
"Sai kuma kiyi..." Aliya ta fada tana tura dankwali gaban goshi,hakan da tayi ya sanya aysha qyale maganar don bata fiya son jayayya ba,saidai har cikin ranta bata jin tana buqatar yin wani abun.
Hira sosai suka sha da aliya,wanda tana yi tana jefo maganar biki da wani abun da za'a gudanar,itadai murmushi aysha take,komai ma ganinsa take kamar almara sani ne aliyan batayi ba take zancan wani biki,wayar aliyan ce ta fadi tunda ta sauka anijer din,bata kuma haddace lambar aysha ba,mamanta kuma itama bata gari bare ta aiko a karba mata lambar ta tura mata.
Sai qarfe uku aliya ta shirya tafiya,tare suka fito tana tako mata har wajen gate,daga can ta hango kamar shi,yana tsaye gaban mai saida agwaluma da goba irin masu turowa a baro din nan yana siya,kanta ta dauke har zasu gota shi taji ance
"Sannunku" tare suka waiwaya,ayshan ta saki dan qaramin murmushi
"Barka da yamma" ta furta a hankali,har yau bata sakewa da shi jinsa take kamar baqonta
"Barkanki..."ya amsa mata yana miqa mata ledar agwalumar daya siya mata a baqar leda
"Na gode,bari na dan raka qawata" ta fada bayan ta saka hannu biyu ta karba a mutunce
"A dawo lafiya...amma ai ba haka ake ba...bari ni nayi karambani....qawa ni suna na muhammad khalipha....nine sabon yayan aishatu" duban ayshan aliya tayi don bata gane me yake nufi ba
"Sabon yayanta da za'a daura musu aure...." Ya sake bata haske,qasan ransa yana dariyar yadda ta kasa gane zancan da farko
"Ohk....kacemin ango ne" ta furta cikin fara'a,sannan suka gaisa,nan suka barshi su kuma sukayi gaba,sosai aliya ta damqe hannun aysha
"Sashin....wannan kyau haka?....haka yake da kyau....ke ni kaman ma na san fuskarshi wallahi,kamar na taba ganinsa amma na manta a'ina....gaskiya kyakkyawa ne" itakam murmushi kawai tayi,don bata iya qare masa kallo bare ta rarrabe da kyansa ko muninsa
"Gaskiya kin dace...da alama sashin yana da kirki....saidai abinda ban gane ba....meye na wani cewa yayanki.....yana nufin a hakan zaku tafi wa da qanwa?" Ajiyar zuciya aysha ta saki
"Koma mene ni indai zai sanyani cikin ahalinsa,su zauna da ni zuciya daya su riqeni kamar daya daga cikinsu,na samu walwala da kwanciyar hankali magana ta qare" kai aliya take kadawa sannan ta dan dakata da tafiyar da take ta dubi aysha
"Ban yarda da wannan alaqar ta tafi a haka ba aysha....kisa a ranki aure zakiyi kamar kowa" murmushi tayi tana rausayar da kai bayan ta kallo gefe guda
"Nima ai ba kamar kowa bace aliya ki duba fa ki gani....ba wanda ya nemeni don zanyi aure...ban taba tattauna maganar dake damuna da kowa ba saike...kina nufin da ni 'yar gata ce...kina nufin da ana sona dukkan abinda ya faru din nan zai faru?" Ta qarashe tambayar idanunta cikin na aliya,da alamar akwai abunda ke taba ranta qwarai,kama hannunta aliyan tayi qasan zuciyarta cike fal da tausayinta
"Karki damu da kowa....karki damu da komai aysha...koba kowa mu muna tare...ki koma ki jirayi lokacin zuwa gyaran jiki....kin bar angonki kuma a tsaye,idan wata tazo wucewa kuma ta qyasa kanshi ba ruwa na,tsaf zata qwaceshi a hannunki da wannan sanyin naki" ta qarasa fada cikin sigar zolaya,dariya ta baiwa aysha har sai da tayi ta fito,har yau ba zata iya tantance wannan kyan da aliya ke fada ba
"Amma fa karki tsorata....don bai fiki kyau ba qawata" dariya sosai wannan karon ta baiwa ayshan,wanne kyau ne da ita?,yaushe ta samo kyan,mamaki take duk sanda aliya tace mata tana da kyau
"Ki gaida mama" suka qarke sallamar sanda wani mai napep yazo wucewa aysha ta tsaida mata shi suka tsadance yaja suka tafi.
A jingine ta sameshi jikin katangar qofar gidan hannayensa rungume a qirjinsa,ta saci kallonsa tana son gano kyan da aliya ke fada saidai hada idanun da sukai ya hana hakan tasiri,tana jin nauyin ya ganta tana kallonshi ba tsari hakan a wajenta,kauda kanta tayi sannan tayi gaba zata shige
"Da kin tsaya mun gaisa....wucewa zanyi daga aiken oga nake karyaga na jima ban dawo ba" bata ce komai ba ta dawo da baya,nesa dashi ta tsaya kamar yadda suka saba,a fakaice yake karantarta kamar yadda ya saba,yana mamakin halayenta sosai,sam.bata damu da wasu qyale qyale ba na rayuwa,tunda yake zuwa kulli yaumin cikin hijabi yake tadda ita,bata da yawan kazarniya ko rawar kai irin ta 'yammatan yanzu,bata da surutu bata da kallo,zai iya zuwa ya tafi baifi ta kalleshi sau biyu ba,shi dinma bawai ta kalli cikin qwayar idanunsa ba kai tsaye,dama ba wani hirar arziqi suke ba,yana zuwanne kawai saboda anni dake yawan cewa yaje din bai kamata ba,bataso tazo taqi sakewa da su,ya zamana bata saba da kowa ba
"Biki yanata qaratowa kinjini shuru ko?" Ya fada yana shafa sajen fuskarsa,ba abinda ta fada har ya gama jiran amsa ya dora
"Ina can ina fafutuka ne....duk abinda Allah ya hore zaki jini in sha Allahu...me dame zakiyi ne da bikin?,a ina zakiyi taki walimar?" Dan motsawa tayi kadan hannayenta rungume a qirjinta ta cikin hijabinta
"Karka matsa da yawa....qauye ma zan tafi a satin bikin" cikin mamaki yake dubanta
"Qauye kuma?.....me zakiyi a can?" Sai a sannan ta daga idanunta ta zubesu fes a kansa kafin ta sake janyesu ta maidasu qasa
"Can ne tushe na...kuma daga can nakeso a dauko ni....bani da inda yafi can" tayi shuru tana jiran jin me zaya fadi,gaba daya ta gama burgeshi,a wannan zamani da yawancin mutane ke bala'in gudu da qyamatar qauye....suke jin haushi da takaici idan an kirasu 'yan qauye,suke bata rai idan 'yan qauye sun rabesu,a sannan ita ta zabi ta nuna su a matsayin danginta,ta zabi kowa yaje ya ganta a cikinsu,take daga hannu tana gayawa duniya daga inda take
"Babu matsala.....duk da haka za'ayi abinda ya samu da yardar Allah....sakamin number wayarki don Allah koda buqatar kiran zai taso" ya fada yana miqa mata vivo dinsa da ya baiwa nasir dazu ya saka reza ya jijji mata ciwo,saika dauka tsabar dadewa ne ya saka ta qoqe,idanu ya zuba mata sanda ta amsa ko zaiga qyama daga gareta ko wani abu makamancin haka,saidai fuskarta na nan a yadda take ta soma jera masa lambobin,saura lamba biyu ta gama sakawa wayar ta dauke dif,yasan da faruwar hakan amma sai ya nuna kamar bai kula ba,cikin damuwa ta dago ta dubeshi
"Ta dauke wayar ko chargy ne babu?"
"Subhanallah....,dama yau tun safe take haka....miqo in gani,Allah yasa ta tashi,gashi oga zai iya kirana kowanne lokaci" ya karba yana cire batirin,ya sake maidawa ya kunna duk da yasan ba sake tashi zata yi ba,ai kuwa bata tashin ba,fuskarsa cike da damuwa yace
"a'ah....anzo shirye shiryen bikin ne?" Ta furta cikin siga ta izgilanci tana dariya dariya
"Ai gwara a bada himma...mai kwarmin ido da wuri yake fara kukansa ko?,duk da yake ma a qauye za'ayi komai,ta kwana gidan sauqi" ta qarashe tana dariya,da sauri aysha ta matsa hannun Aliya tana mata nuni da kada ta kulata kenan,aliyan ta fahimci haka,saboda haka ta watsawa asma'un kallon banza sannan tace
"Kinci sa'a cikin gidanku nake.....ki tareni a waje" ta fada a zafafe tana jan hannun aysha sukayi gaba
"Ba komai....duk nasan meke damunku" ta fada tana dariya tayi kitchen,iska ta furzar daga bakinta bayan sun shiga dakin ayshan,bata iya zama ba ta dubi aysha
"Har yau wannan mara mutuncin tana nan tana iskancin nan nata....abun ma kamar gaba yake sakeyi saboda rashin taka mata burki da bakyayi ko?" Murmushi aysha ta saki tana gyara ma aliyan wajen da zata zauna bawai don akwai datti ko kaya a wajen ba
"Karki damu.....duk abinda take ba shine a gaba na ba...saboda baki taba gani an gutsuri naman jikina saboda haka ba....hasalima qimarta nake gani har kwanan gobe....saboda jinin daddy ce ita....daraja ba qarya bace...ko a lahira wani yana cin darajar wani....karkuma ki manta cewa ni din ba kowa bace....face yarinyar da hatta mahaifiyarta ta gujeta"ta qarashe cikin karayar zuciya
"wannan ba hujja bace" aliya ta fada hannunta riqe da qugunta tana kada kai
"Manta da wannan.....zauna muyi hirar yaushe gamo" ta fada tana murmushi tamkar ba abinda ke damunta a rayuwa,saidai can qasar zuciyarta tana jin tafi kowa matsala a rayuwa
"Ba hirar yaushe gamo zamuyi ba aysha....mu tattauna maganar dake gabanmu" ta fadi tana zama,yayin da ayshan ta yiwa kanta mazauni itama kusa da ita.
Kaf babu abinda ta boye mata ta zayyana mata komai,shuru ne ya ratsa dakin yayin da aliya ke hadiyar yawu idanunta fes kan fuskar ayshan
"Aysha..." Ta kirata still tana kallonta
"Na'am" ta amsa tana dubanta
"Kin gamsu har cikin ranki zaki auri wannan mutumin zaki zauna da shi?" Tayi mata shigen tambayar da khaliphan ya taba yi mata,kai ta jinjina don ta tabbatar idan tace bata so tsaf aliya zata rusa komai,to idan ta rusa dinma me zata zauna taci gaba da yi cikin gidan?,meye amfanin zamanta?,a gaba wa zata hadu da shi?,gwara wannan ya nuna alamu na tausayi a gareta
"Shikenan....addu'a zamu ci gaba da yi Allah yasa kin dace...ina fata kuma asma'u idan ma tayi da niyyar mugunta mugun abinta ya koma mata kanta,auren mai kudi ba shine dacewa ba,aurwn mai kudi ba shine samun kwanciyar hankalin gidan aure ba,auren mai kudi bai cikin manyan jigon dake sawa a auri namiji,ni'ima ce da idan Allah yaga dama zaiwa wanda yaga dama bawai don yafi sonka cikin halittarsa ba,hasalima ba kowa ke dacewa kan hakan ba,amma sashin abu daya bana son kice zaki rage na hidimar biki da akewa kowacce diya mace budurwa,don kema ita ce....saboda haka zamuyi komai kamar yadda akeyi" dariya aysha tayi ta karyar da kai tana duban aliya
"Kiyi haquri sashin karki dora min abinda bazan iya ba,wallahi Allah bana sha'awar yin komai....kin manta cewa muhalli kawai zan sauya ba wani abu ba....ni haka nake ji a jikina bawai aure zanyi ba"
"Sai kuma kiyi..." Aliya ta fada tana tura dankwali gaban goshi,hakan da tayi ya sanya aysha qyale maganar don bata fiya son jayayya ba,saidai har cikin ranta bata jin tana buqatar yin wani abun.
Hira sosai suka sha da aliya,wanda tana yi tana jefo maganar biki da wani abun da za'a gudanar,itadai murmushi aysha take,komai ma ganinsa take kamar almara sani ne aliyan batayi ba take zancan wani biki,wayar aliyan ce ta fadi tunda ta sauka anijer din,bata kuma haddace lambar aysha ba,mamanta kuma itama bata gari bare ta aiko a karba mata lambar ta tura mata.
Sai qarfe uku aliya ta shirya tafiya,tare suka fito tana tako mata har wajen gate,daga can ta hango kamar shi,yana tsaye gaban mai saida agwaluma da goba irin masu turowa a baro din nan yana siya,kanta ta dauke har zasu gota shi taji ance
"Sannunku" tare suka waiwaya,ayshan ta saki dan qaramin murmushi
"Barka da yamma" ta furta a hankali,har yau bata sakewa da shi jinsa take kamar baqonta
"Barkanki..."ya amsa mata yana miqa mata ledar agwalumar daya siya mata a baqar leda
"Na gode,bari na dan raka qawata" ta fada bayan ta saka hannu biyu ta karba a mutunce
"A dawo lafiya...amma ai ba haka ake ba...bari ni nayi karambani....qawa ni suna na muhammad khalipha....nine sabon yayan aishatu" duban ayshan aliya tayi don bata gane me yake nufi ba
"Sabon yayanta da za'a daura musu aure...." Ya sake bata haske,qasan ransa yana dariyar yadda ta kasa gane zancan da farko
"Ohk....kacemin ango ne" ta furta cikin fara'a,sannan suka gaisa,nan suka barshi su kuma sukayi gaba,sosai aliya ta damqe hannun aysha
"Sashin....wannan kyau haka?....haka yake da kyau....ke ni kaman ma na san fuskarshi wallahi,kamar na taba ganinsa amma na manta a'ina....gaskiya kyakkyawa ne" itakam murmushi kawai tayi,don bata iya qare masa kallo bare ta rarrabe da kyansa ko muninsa
"Gaskiya kin dace...da alama sashin yana da kirki....saidai abinda ban gane ba....meye na wani cewa yayanki.....yana nufin a hakan zaku tafi wa da qanwa?" Ajiyar zuciya aysha ta saki
"Koma mene ni indai zai sanyani cikin ahalinsa,su zauna da ni zuciya daya su riqeni kamar daya daga cikinsu,na samu walwala da kwanciyar hankali magana ta qare" kai aliya take kadawa sannan ta dan dakata da tafiyar da take ta dubi aysha
"Ban yarda da wannan alaqar ta tafi a haka ba aysha....kisa a ranki aure zakiyi kamar kowa" murmushi tayi tana rausayar da kai bayan ta kallo gefe guda
"Nima ai ba kamar kowa bace aliya ki duba fa ki gani....ba wanda ya nemeni don zanyi aure...ban taba tattauna maganar dake damuna da kowa ba saike...kina nufin da ni 'yar gata ce...kina nufin da ana sona dukkan abinda ya faru din nan zai faru?" Ta qarashe tambayar idanunta cikin na aliya,da alamar akwai abunda ke taba ranta qwarai,kama hannunta aliyan tayi qasan zuciyarta cike fal da tausayinta
"Karki damu da kowa....karki damu da komai aysha...koba kowa mu muna tare...ki koma ki jirayi lokacin zuwa gyaran jiki....kin bar angonki kuma a tsaye,idan wata tazo wucewa kuma ta qyasa kanshi ba ruwa na,tsaf zata qwaceshi a hannunki da wannan sanyin naki" ta qarasa fada cikin sigar zolaya,dariya ta baiwa aysha har sai da tayi ta fito,har yau ba zata iya tantance wannan kyan da aliya ke fada ba
"Amma fa karki tsorata....don bai fiki kyau ba qawata" dariya sosai wannan karon ta baiwa ayshan,wanne kyau ne da ita?,yaushe ta samo kyan,mamaki take duk sanda aliya tace mata tana da kyau
"Ki gaida mama" suka qarke sallamar sanda wani mai napep yazo wucewa aysha ta tsaida mata shi suka tsadance yaja suka tafi.
A jingine ta sameshi jikin katangar qofar gidan hannayensa rungume a qirjinsa,ta saci kallonsa tana son gano kyan da aliya ke fada saidai hada idanun da sukai ya hana hakan tasiri,tana jin nauyin ya ganta tana kallonshi ba tsari hakan a wajenta,kauda kanta tayi sannan tayi gaba zata shige
"Da kin tsaya mun gaisa....wucewa zanyi daga aiken oga nake karyaga na jima ban dawo ba" bata ce komai ba ta dawo da baya,nesa dashi ta tsaya kamar yadda suka saba,a fakaice yake karantarta kamar yadda ya saba,yana mamakin halayenta sosai,sam.bata damu da wasu qyale qyale ba na rayuwa,tunda yake zuwa kulli yaumin cikin hijabi yake tadda ita,bata da yawan kazarniya ko rawar kai irin ta 'yammatan yanzu,bata da surutu bata da kallo,zai iya zuwa ya tafi baifi ta kalleshi sau biyu ba,shi dinma bawai ta kalli cikin qwayar idanunsa ba kai tsaye,dama ba wani hirar arziqi suke ba,yana zuwanne kawai saboda anni dake yawan cewa yaje din bai kamata ba,bataso tazo taqi sakewa da su,ya zamana bata saba da kowa ba
"Biki yanata qaratowa kinjini shuru ko?" Ya fada yana shafa sajen fuskarsa,ba abinda ta fada har ya gama jiran amsa ya dora
"Ina can ina fafutuka ne....duk abinda Allah ya hore zaki jini in sha Allahu...me dame zakiyi ne da bikin?,a ina zakiyi taki walimar?" Dan motsawa tayi kadan hannayenta rungume a qirjinta ta cikin hijabinta
"Karka matsa da yawa....qauye ma zan tafi a satin bikin" cikin mamaki yake dubanta
"Qauye kuma?.....me zakiyi a can?" Sai a sannan ta daga idanunta ta zubesu fes a kansa kafin ta sake janyesu ta maidasu qasa
"Can ne tushe na...kuma daga can nakeso a dauko ni....bani da inda yafi can" tayi shuru tana jiran jin me zaya fadi,gaba daya ta gama burgeshi,a wannan zamani da yawancin mutane ke bala'in gudu da qyamatar qauye....suke jin haushi da takaici idan an kirasu 'yan qauye,suke bata rai idan 'yan qauye sun rabesu,a sannan ita ta zabi ta nuna su a matsayin danginta,ta zabi kowa yaje ya ganta a cikinsu,take daga hannu tana gayawa duniya daga inda take
"Babu matsala.....duk da haka za'ayi abinda ya samu da yardar Allah....sakamin number wayarki don Allah koda buqatar kiran zai taso" ya fada yana miqa mata vivo dinsa da ya baiwa nasir dazu ya saka reza ya jijji mata ciwo,saika dauka tsabar dadewa ne ya saka ta qoqe,idanu ya zuba mata sanda ta amsa ko zaiga qyama daga gareta ko wani abu makamancin haka,saidai fuskarta na nan a yadda take ta soma jera masa lambobin,saura lamba biyu ta gama sakawa wayar ta dauke dif,yasan da faruwar hakan amma sai ya nuna kamar bai kula ba,cikin damuwa ta dago ta dubeshi
"Ta dauke wayar ko chargy ne babu?"
"Subhanallah....,dama yau tun safe take haka....miqo in gani,Allah yasa ta tashi,gashi oga zai iya kirana kowanne lokaci" ya karba yana cire batirin,ya sake maidawa ya kunna duk da yasan ba sake tashi zata yi ba,ai kuwa bata tashin ba,fuskarsa cike da damuwa yace