Sashe 20
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ke...kizo daddy na kira" ta tsinci muryar asma'u a tsakiyar kanta,batasan yaushe ta shigo wajen harta qaraso inda take ba,kanta ta daga tana duban asma'u dake sanye da fitted gown,kanta babu dankwali sai gashinta mai santsi dako yaushe ke cikin gyara yake matse a ribbom,kunneta maqale da earpiece wanda sanyashi ya zame mata kamar al'adarta,hakan kuma baya rasa nasaba da yawan jin kade kade da take da shi
"Tom" ta amsa tana tsaida karatunta
"Yauwa...idan mun shiga ki yiwa daddy godiyar mota" tana gama fada ta juya abinta ta wuce,sam ta mance wacce mota ma,sai data zo shiga cikin gidan data sake ganin motocin ta tuna,motocinsu ne da daddy ya musu alqawari ya kuma cikasu guda biyu ita da asma'un,tuni asma'u ta soma hawa tata,saidai ita ko lasisin zuwa kusa da motar bata samu ba bare ta hau ta tuqa,kasancewar a sanda motocin suka iso daddyn baya nan,tafiya ta kamashi na sati hudu,andai danqa mata muqullin ta riqe sau daya,bata juyashi sau biyu ba mummyn ta karba daga hannunta,daga ranar ba'a sake mata maganar ba,taga dai asma'u na hawa tata har makaranta sai data shiga da ita,ko sau daya bata sake tunawa da wani batun mota ba,bata a cikin lissafinta ko sau daya bare ta damu da lamarinta,bata manta ba a qauyensu ko jaki sai ta manta rabonta da hawanshi balle mota,tana can cikin uqubar data fi ta kurkuku,yaushe ma zata tuna da wani abu.
"Indon baffale" daddy ya fada a sanda ta gama gaidashi yana murmushi,sau tari yakan kirata da hakan Idan yana cikin nishadi ko yana son jefa murmushi bisa fuskar ayshan,duk da sunan yana da babban naqasu nashi na qashin kansa,amma har kwanan gobe tana farinciki da alfahari da shi,tunda ko babu komai DA UBA AKE ADO.
yadda daddyn ya maida yanayinshi kadai ya isa shaida maka cewa muhimmiyar magana ce zaiyi da su,hakan ya sanya kowa ya bashi hankali da nutsuwarsa a sanda ya soma magana
"Na godewa Allah daya nunamin lokacin da kuka kammala karatunku cikin nasara,ba shakka nayi alfahari da hakan yadda kuka kama kanku da mutuncinku,alhamdulillahi....toh,dukkaninku ina zaton ba wadda bata haure shekara a shirin ba...saboda haka abu na gaba da nakeson kowaccenku ta sani shine....aure nake da burin naga kunyi,a yanzu shine abinda ya rage muku,duk da ke indo bamuyi haka da ahalinki ba,munyi dasu zan maida musu dake a duk sa'ilin da aka kai wannan bigiren,amma na tabbatar da cewa ba zasu qi ko suyi jayayya da wannan batun da nake muku a yanzu ba,don suma ina da yaqinin shine hukuncinsu na gaba a kanki" a hankali taja hanci tana dauke tagwayen qwallar data ziraro daga idanunta,bata jin sun damu da rayuwarta bare suyi wani kyakkyawan tunani game da makomarta,ba wanda ya biyo sahunta tunda ta taho,ba wanda ya damu yasan inda take rayuwa,babu wanda ya damu da sanin wani hali taci gaba da kasancewa bayan barowarta mahaifarta,duk da tasan cewa basa maraba da hakan amma a qalla zata ji dadi idan wani ya bibiyeta da sunan ahalinta ne shi,ita dai tana godewa Allah da yaji qanta ya dubi rashin gata da galihu irin nata,ya jefo mata da daddy cikin rayuwarta a lokacin da take cikin tsananin buqatar matallafi,wanda zai jibanci lamuranta,bangon da zata dafa taji dadi
"Ammm....auta" ya kira asma'u
"Na'am daddy" ta amsa cikin fara'a
"Ina fatan kin samu wanda kikeso kun kuma daidaita kanku" kai ta kada cikin sauri
"Eh daddy...ka manta da hamid?...dan gidan alhj kutama?"
"Af....anyi haka,ja'ira ko kunyata bakiji ko?,ba zaki bari mamanku ta gaya min ba?" Fuskarta ta rufe da tafin hannunta tana dariya,shima dariya daddyn yayi kafin yace
"To ma sha Allah,babu damuwa,hamid ai dan gida ne,sananne ne...amma duk da haka zanyi bincike,zan nemeku daga baya ke da shi duka"
"Toh daddy" ta fada cikin murmushi,wani farinciki ke ratsata na daban,tana jin kadan ya rage mafarkinta ya tabbata,saura kadan ta shiga sahun manyan mata,wadanda za'a kira ko a nuna ace matar wane ce ko surukar wane ce,ahalin alhaji kutama ko qaramin yaro yasan nasibin da suke dashi bare babba,lallai zata tserewa sa'a nan kusa.
"Indo aisha.....kinsan hafiz?....hafiz yaron gidan IG...." Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci asma'u,ashe hafiz bai bar aysha ba,duk abinda ta fada mishi kan ayshan kenan bai masa tasiri ba,meke shirin faruwa?,lallai dole tayi wani abu,bai kamata aysha ta auri kwatankwacin wanda ita ta aura ba,har abada aysha na qasansu kuma zata ci gaba da tabbata a qasansu,ba zata yarda ko ta bari suyi gasa ko komanceceniyar jin dadin rayuwar gidan aure ba,yayin da qwaqwalwar ayshan ta tafi binciken mai sunan da daddy yake fadi,don ita harga Allah ta mance da babinsa
"Au hafiz daddy bai yarda ba?....kinji aysha ashe bai yarda da abinda kika gaya masa ba" ta fada cikin dariya dariya tana duban ayshan
"Kamar yaya?,me yake faruwa?" Daddyn ya fada fuskarsa na nuna alamun neman qarin bayani idanunsa tsakanin aysha wadda kanta ke qasa da asma'u
"Daddy kunyar aysha tayi yawa,dama na sani ba zata iya gaya maka ba,hafiz kafin yazo gareka ita ya soma samu yace yana so....to already akwai wanda takeso suka jima suna soyayya....infact sunma juna ma alqawarin aure,ta sanar masa shi kuma yace bai yarda ba,lallai shi ya ganta yana sonta,ba ruwansa da soyayyarta da wani tunda ba aure aka daura musu ba,tofa shine ya biyo ta wajenka" kai daddyn ke kadawa
"A'ah ba za'ayi haka ba....,ba yadda zanwa aysha auren tilas,shi wancan din ya sunanshi?,waye shi?" Tashin farko khalipha shine wanda ya fado ranta,babu wanda ayshan ta dace da shi irin khaliphan,ta tabbatar idan ta aureshi ayshan ta daina tarayya da ita cikin komai,tana da yaqinin bashi da qarfin da aysha zata samu jin dadin rayuwar aure makamanciyar tata ma bare irin tata,ba shakka yaron oga shine dai dai da aysha,qwarya tabi qwarya
"Sunansa muhammad abba"
"Ba komai...ki bani number dinsa,ni zan kirashi da kaina mu zauna nasan wayeshi" cikin sauri ta fiddo wayarta ta dauki wayar daddayn ta soma loda masa number khalipha.
Ji take kaman ba kanta ake maganar ba,tunda ita iya saninta dukkan maganganun da ke wanzuwa tsakanin daddyn da asma'u ba wanda tasan ya faru akanta,bata gane cewa da ita ake ba saida daddyn ya soma magana cikin tsokana
"Wannan kunyar indon baffale har yanzu bata ragu ba,fulatancinki na jikinki...kinje jami'a amma babu abinda ya ragu,yanzu badon Allah yasa ma'u tayi bayani ba na miki auren dole fa?" Ya qarasa maganar cikin sigar zolaya,wani sanyi taji yana ratsata a sanda ta fuskanci kanta ake dukka wadan nan maganganun,qwaqwalwarta ta tsaya da tuna komai bare ta samu abin fada,hakan ya sanya ta sake dunqulewa waje daya,yar dariya daddy yayi ga zatonsa tsabar kunya ke dawainiya da ita,kusan bata kuma gane meke gudana ba,daga qarshe dai ta fahimci daddy ya sallamesu,asma'u ta kama hannunta ta miqar tana zolayarta cikin kissa da kisisina,zolayar datake ganinta kamar a majigin kallon fina finai,saboda tsahon zamanta da rayuwarta da asma'un bata taba ganin murmushi kan fuskarta zuwa gareta ba,idan ko tayi murmushin to na mugunta ne ko cimma nasarar wani muradi a kanta
"Indon nan har yau daddy taqi ta waye wallahi,har yau indon qauye ce,na rasa ta yadda zan canza ta,tashi mu tafi karki nutse a wajen" ta ambata tana jan hannunta tana dariya,binta kawai tayi kamar wata shashasha har suka fice daga falon suka doshi nasu gefen.
_gaisuwa da godiya a gareku masoya na cikin grps namu na zafafa paid grp,da daurin boye grps_🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_
*WITSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA MAI BUQATAR WADAN NAN LITATTAFAI SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
(08030811300)
*DB*
14
Tun basu shiga bangaren nasu ba ta saki hannunta tana dubanta
"Gata nayi miki fa....ruwanki kibar batun a haka ruwanki ki warware,amma ina tabbatar miki koda kin warware kece a ciki" tana gama fadar haka tayi gaba abinta ta barta a tsaye a wajen tana qoqarin gayawa kanta abinda ke faruwa,sam ta kasa tabuka koma
Wai meye haka ke shirin faruwa da rayuwarta?,ya ilahi wanne laifi ta yiwa asma'u haka?.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun yana toilet yana brush yake jiyo sautin qarar wayarshi,mutum daya ce ke kiransa ta layi asma'u,cire wayar yayi daga chargy ya koma saman sofa ya zauna sannan yabi kiran,plashing ya mata kamar yadda ya saba sannan ya aje wayar gefanshi yana ci gaba da tura saqonnin da suka hanashi kowamawa bacci bayan sallar asuba ta cikin system dinsa,ba'a rufa minti guda ba cikakke ta biyo kiran.
"Yallabiya kin tashi lafiya"
"Lafiya yaron oga"ta amsa kaman yadda ta saba masa,duk da yau akwai sakewa sosai cikin muryarta babu cunkushewa
"Yasu daddy?"
"Shi yakeson ganinka ma" sam bai tsammaci jin maganar ba daga bakinta
"Allah yasa ba laifi nayi ba" ya furta yana maida wayar handsfree ya ajeta kusa da system din nashi yana ci gaba da aikinsa
"Lafiya qalau....zaka sameshi da daddare ne bayan sallar isha'i"
"To Allah ya kaimu" bata amsa ba ta katse kiran kawai.
Aikinsa yaci gaba da yi jifa jifa yana tambayar kansa dalilin kiran,sai ya tsaida aikin nashi ya lalubi wayarsa yana neman wata lamba,bugu hudu aka daga bayan sun gaisa ya bada sautun kayan gwanjo riga da wando da takalmi mai sauqin kudi,a ladabce ya amsa masa sukayi sallama,ya sauka ya masa transfer din kudin daya gaya masa.
"Tom" ta amsa tana tsaida karatunta
"Yauwa...idan mun shiga ki yiwa daddy godiyar mota" tana gama fada ta juya abinta ta wuce,sam ta mance wacce mota ma,sai data zo shiga cikin gidan data sake ganin motocin ta tuna,motocinsu ne da daddy ya musu alqawari ya kuma cikasu guda biyu ita da asma'un,tuni asma'u ta soma hawa tata,saidai ita ko lasisin zuwa kusa da motar bata samu ba bare ta hau ta tuqa,kasancewar a sanda motocin suka iso daddyn baya nan,tafiya ta kamashi na sati hudu,andai danqa mata muqullin ta riqe sau daya,bata juyashi sau biyu ba mummyn ta karba daga hannunta,daga ranar ba'a sake mata maganar ba,taga dai asma'u na hawa tata har makaranta sai data shiga da ita,ko sau daya bata sake tunawa da wani batun mota ba,bata a cikin lissafinta ko sau daya bare ta damu da lamarinta,bata manta ba a qauyensu ko jaki sai ta manta rabonta da hawanshi balle mota,tana can cikin uqubar data fi ta kurkuku,yaushe ma zata tuna da wani abu.
"Indon baffale" daddy ya fada a sanda ta gama gaidashi yana murmushi,sau tari yakan kirata da hakan Idan yana cikin nishadi ko yana son jefa murmushi bisa fuskar ayshan,duk da sunan yana da babban naqasu nashi na qashin kansa,amma har kwanan gobe tana farinciki da alfahari da shi,tunda ko babu komai DA UBA AKE ADO.
yadda daddyn ya maida yanayinshi kadai ya isa shaida maka cewa muhimmiyar magana ce zaiyi da su,hakan ya sanya kowa ya bashi hankali da nutsuwarsa a sanda ya soma magana
"Na godewa Allah daya nunamin lokacin da kuka kammala karatunku cikin nasara,ba shakka nayi alfahari da hakan yadda kuka kama kanku da mutuncinku,alhamdulillahi....toh,dukkaninku ina zaton ba wadda bata haure shekara a shirin ba...saboda haka abu na gaba da nakeson kowaccenku ta sani shine....aure nake da burin naga kunyi,a yanzu shine abinda ya rage muku,duk da ke indo bamuyi haka da ahalinki ba,munyi dasu zan maida musu dake a duk sa'ilin da aka kai wannan bigiren,amma na tabbatar da cewa ba zasu qi ko suyi jayayya da wannan batun da nake muku a yanzu ba,don suma ina da yaqinin shine hukuncinsu na gaba a kanki" a hankali taja hanci tana dauke tagwayen qwallar data ziraro daga idanunta,bata jin sun damu da rayuwarta bare suyi wani kyakkyawan tunani game da makomarta,ba wanda ya biyo sahunta tunda ta taho,ba wanda ya damu yasan inda take rayuwa,babu wanda ya damu da sanin wani hali taci gaba da kasancewa bayan barowarta mahaifarta,duk da tasan cewa basa maraba da hakan amma a qalla zata ji dadi idan wani ya bibiyeta da sunan ahalinta ne shi,ita dai tana godewa Allah da yaji qanta ya dubi rashin gata da galihu irin nata,ya jefo mata da daddy cikin rayuwarta a lokacin da take cikin tsananin buqatar matallafi,wanda zai jibanci lamuranta,bangon da zata dafa taji dadi
"Ammm....auta" ya kira asma'u
"Na'am daddy" ta amsa cikin fara'a
"Ina fatan kin samu wanda kikeso kun kuma daidaita kanku" kai ta kada cikin sauri
"Eh daddy...ka manta da hamid?...dan gidan alhj kutama?"
"Af....anyi haka,ja'ira ko kunyata bakiji ko?,ba zaki bari mamanku ta gaya min ba?" Fuskarta ta rufe da tafin hannunta tana dariya,shima dariya daddyn yayi kafin yace
"To ma sha Allah,babu damuwa,hamid ai dan gida ne,sananne ne...amma duk da haka zanyi bincike,zan nemeku daga baya ke da shi duka"
"Toh daddy" ta fada cikin murmushi,wani farinciki ke ratsata na daban,tana jin kadan ya rage mafarkinta ya tabbata,saura kadan ta shiga sahun manyan mata,wadanda za'a kira ko a nuna ace matar wane ce ko surukar wane ce,ahalin alhaji kutama ko qaramin yaro yasan nasibin da suke dashi bare babba,lallai zata tserewa sa'a nan kusa.
"Indo aisha.....kinsan hafiz?....hafiz yaron gidan IG...." Mummunar faduwar gaba ce ta ziyarci asma'u,ashe hafiz bai bar aysha ba,duk abinda ta fada mishi kan ayshan kenan bai masa tasiri ba,meke shirin faruwa?,lallai dole tayi wani abu,bai kamata aysha ta auri kwatankwacin wanda ita ta aura ba,har abada aysha na qasansu kuma zata ci gaba da tabbata a qasansu,ba zata yarda ko ta bari suyi gasa ko komanceceniyar jin dadin rayuwar gidan aure ba,yayin da qwaqwalwar ayshan ta tafi binciken mai sunan da daddy yake fadi,don ita harga Allah ta mance da babinsa
"Au hafiz daddy bai yarda ba?....kinji aysha ashe bai yarda da abinda kika gaya masa ba" ta fada cikin dariya dariya tana duban ayshan
"Kamar yaya?,me yake faruwa?" Daddyn ya fada fuskarsa na nuna alamun neman qarin bayani idanunsa tsakanin aysha wadda kanta ke qasa da asma'u
"Daddy kunyar aysha tayi yawa,dama na sani ba zata iya gaya maka ba,hafiz kafin yazo gareka ita ya soma samu yace yana so....to already akwai wanda takeso suka jima suna soyayya....infact sunma juna ma alqawarin aure,ta sanar masa shi kuma yace bai yarda ba,lallai shi ya ganta yana sonta,ba ruwansa da soyayyarta da wani tunda ba aure aka daura musu ba,tofa shine ya biyo ta wajenka" kai daddyn ke kadawa
"A'ah ba za'ayi haka ba....,ba yadda zanwa aysha auren tilas,shi wancan din ya sunanshi?,waye shi?" Tashin farko khalipha shine wanda ya fado ranta,babu wanda ayshan ta dace da shi irin khaliphan,ta tabbatar idan ta aureshi ayshan ta daina tarayya da ita cikin komai,tana da yaqinin bashi da qarfin da aysha zata samu jin dadin rayuwar aure makamanciyar tata ma bare irin tata,ba shakka yaron oga shine dai dai da aysha,qwarya tabi qwarya
"Sunansa muhammad abba"
"Ba komai...ki bani number dinsa,ni zan kirashi da kaina mu zauna nasan wayeshi" cikin sauri ta fiddo wayarta ta dauki wayar daddayn ta soma loda masa number khalipha.
Ji take kaman ba kanta ake maganar ba,tunda ita iya saninta dukkan maganganun da ke wanzuwa tsakanin daddyn da asma'u ba wanda tasan ya faru akanta,bata gane cewa da ita ake ba saida daddyn ya soma magana cikin tsokana
"Wannan kunyar indon baffale har yanzu bata ragu ba,fulatancinki na jikinki...kinje jami'a amma babu abinda ya ragu,yanzu badon Allah yasa ma'u tayi bayani ba na miki auren dole fa?" Ya qarasa maganar cikin sigar zolaya,wani sanyi taji yana ratsata a sanda ta fuskanci kanta ake dukka wadan nan maganganun,qwaqwalwarta ta tsaya da tuna komai bare ta samu abin fada,hakan ya sanya ta sake dunqulewa waje daya,yar dariya daddy yayi ga zatonsa tsabar kunya ke dawainiya da ita,kusan bata kuma gane meke gudana ba,daga qarshe dai ta fahimci daddy ya sallamesu,asma'u ta kama hannunta ta miqar tana zolayarta cikin kissa da kisisina,zolayar datake ganinta kamar a majigin kallon fina finai,saboda tsahon zamanta da rayuwarta da asma'un bata taba ganin murmushi kan fuskarta zuwa gareta ba,idan ko tayi murmushin to na mugunta ne ko cimma nasarar wani muradi a kanta
"Indon nan har yau daddy taqi ta waye wallahi,har yau indon qauye ce,na rasa ta yadda zan canza ta,tashi mu tafi karki nutse a wajen" ta ambata tana jan hannunta tana dariya,binta kawai tayi kamar wata shashasha har suka fice daga falon suka doshi nasu gefen.
_gaisuwa da godiya a gareku masoya na cikin grps namu na zafafa paid grp,da daurin boye grps_🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_
*WITSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA MAI BUQATAR WADAN NAN LITATTAFAI SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
(08030811300)
*DB*
14
Tun basu shiga bangaren nasu ba ta saki hannunta tana dubanta
"Gata nayi miki fa....ruwanki kibar batun a haka ruwanki ki warware,amma ina tabbatar miki koda kin warware kece a ciki" tana gama fadar haka tayi gaba abinta ta barta a tsaye a wajen tana qoqarin gayawa kanta abinda ke faruwa,sam ta kasa tabuka koma
Wai meye haka ke shirin faruwa da rayuwarta?,ya ilahi wanne laifi ta yiwa asma'u haka?.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun yana toilet yana brush yake jiyo sautin qarar wayarshi,mutum daya ce ke kiransa ta layi asma'u,cire wayar yayi daga chargy ya koma saman sofa ya zauna sannan yabi kiran,plashing ya mata kamar yadda ya saba sannan ya aje wayar gefanshi yana ci gaba da tura saqonnin da suka hanashi kowamawa bacci bayan sallar asuba ta cikin system dinsa,ba'a rufa minti guda ba cikakke ta biyo kiran.
"Yallabiya kin tashi lafiya"
"Lafiya yaron oga"ta amsa kaman yadda ta saba masa,duk da yau akwai sakewa sosai cikin muryarta babu cunkushewa
"Yasu daddy?"
"Shi yakeson ganinka ma" sam bai tsammaci jin maganar ba daga bakinta
"Allah yasa ba laifi nayi ba" ya furta yana maida wayar handsfree ya ajeta kusa da system din nashi yana ci gaba da aikinsa
"Lafiya qalau....zaka sameshi da daddare ne bayan sallar isha'i"
"To Allah ya kaimu" bata amsa ba ta katse kiran kawai.
Aikinsa yaci gaba da yi jifa jifa yana tambayar kansa dalilin kiran,sai ya tsaida aikin nashi ya lalubi wayarsa yana neman wata lamba,bugu hudu aka daga bayan sun gaisa ya bada sautun kayan gwanjo riga da wando da takalmi mai sauqin kudi,a ladabce ya amsa masa sukayi sallama,ya sauka ya masa transfer din kudin daya gaya masa.