Sashe 105
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Naja'atu" dukkaninsu suka waiwaya jin an ambaci sunan ummin,wani mutumine wanda aqalla zaikai shekara hamsin da biyar,gefanshi kuma khalipha ne tsaye suna dubansu,kuka ummin ta sake saki tana kauda kanta daga garesu baki daya,takawa mutumin yayi har zuwa inda take tsaye ya riqe hannayenta
"Idan kowa bai isa alfarnar garin nan,da wanda kabarinsa ke cikin wannan waje mai albarka sun isa su sanya ki amshi diyarki"
"Abban basma.....bana so...." Sai maganar tata ta harqe
"Bana son maganar da suka fada ta tabbata akan aisha,banason ta silata wani abu ya sameta" ta fada tana sake barkewa da kuka
"Dukkaninmu ba zamu fahimci abinda kike magana akai ba idan ba bayani kika yi mana ba"
"Ammm....abba,me zai hana mu samu wani waje su zauna a can" cewar khalipha,kai abban ya gyada masa sannan ya riqe hannun ummi naja'atu dake ta kuka.
Shuru kowannensu yayi kafin abba ya daga kai ya dubi aysha
"Khalipha ya cancanci zama yaji kowanne irin abu da naja'atu xata fada,fita kice ya shigo" a sanyaye aysha ta miqe don zuwa kiranshi,saidai duka hankalinta nakan ummin,gani take kaman kafin taje ta dawo xata rasa ummin,kamar kafin taje ta dawo ummin xata sauya ra'ayi,zata fasa fada mata komai,zata fasa karbarta,itama ummin nata idanun nakan ayshan,ita kadai tasan me take hadiyewa a haka harta dawo tare da khalipha,kujerar dake daura da aysha abba ya nuna masa yace ya zauna,da fari baiso zaman ba,saboda yana ganinnkamar wani sirri ne da bai shafi yaji ba,amma abba yace ko daya,miji shine babban sirri na farko wajen matarsa,haka ya zauna kanshi da idanuwanshi a qasa yana harhada cukurkudaddiyar rayuwarsu shida ayshan waje daya
"A ranar dana bar gidan baffale a daren ba'a kwana ba akace ana sallama da baffana,yana fita baifi minti biyar ba muka jiyo hayaniya cikin zauren gidanmu,sai gashi ya dawo yace na fito ana son magana dani,ban musa ba na miqe na fito,saidai wadanda na gani a wajen inda ya gaya min su sukazo tabbas bazan fito ba,gefe daya na samu na tsaya ina dubansu,dukkan yayye da qannem baffale ne mazan sai inna yelwa
"halaa ma dai bakasan abinda ya faru ba?"cewar saya daga cikin yayyen baffale yana gayawa baffana,kai ya jinjina yace kai nake sauraro
" to mudai muna da tantamar indo diyar baffale ce gaba dayanmu,tunda cikinta bai tashi bullowa ba sai da yabar garin nan gaba daya"nan fa ran baffanmu ya baci sosai,duk haqurinshi kuwa,saidai ya hadiye yana dubansu kawai
"Me kukeson ku gayamin,nafi ku sanin wace naja"
"Ai ka tsaya malam duka na wannan ba,abu daya shine zai tabbatar mana da aisha jinin baffale ce kuma jininku" shuru kowa yayi nida baffa gaba daya muna sauraronsu,inna yelwa ce ciki izgili nuna isa da taqama tace
"Daga nan har shekaru goma dai dai da rana daya idan naja ta koda kalli indo kota sake ta nemeta toba jininmu bace,ba baffale ne mahaifinta ba,matuqar jininmu ce to babu ita babu ita,ba ruwanta da ita jininta zasu kula da ita..." Ban tsaya na qarasa saurarenta ba kawai na juya cikin gida na barsu nan da baffa na,maganar ta inna yelwa ta yimin ciwo qwarai,sharrin zina ba abinda ya kaishi muni,na shiga bacin rai sosai a sannan,na sake tsanar inna yelwa da ahalin gidanta gaba daya.
Ana tsaka da wannan saiga inna sailuba,qawar inna yelwa ce sosai,saidai ikon Allah Allah ya hada jinina da ita tana qaunata qwarai,batasan aurena ya mutu ba saboda ba'a garin take auren ba,saidaga bisani tazo ta biyo ta yimin jaje tare da nuna rashin jin dadinta akan aninda inna yelwa tayi,ranar sai gata hankalinta a tashe,ban taba ganinta cikin tashin hankali ba irin ranar,ita take gayan maganar data sake sakawa na janye jikina da.aysha,na nuna mata qyama,na farko ta gayamin inna yelwa ashe ta rabani da baffale tasa aka sanya qiyayyar juna atsakaninmu,har ya mutu yana ambatona yana neman gafarata,sannan yanzu kuma sunyi wani shiri saboda basa son hada jini dani,duk ranar dana yiwa aysha wani kallo na tausayi ko jin qai a ranar ba zata sake kwana a duniya ba,saboda suna da yaqinin babu uwar da zata daurewar azabar da suka shirya suna gana mata iri iri,banso na rasa aisha diyar dana fara samu a duniya,tilas na koyawa kaina kyararta da tsangwarta,duk da a sannan na shaidawa baffa na kafin rasuwarshi yayi addu'a sosai da rubutu,idan baki manta ba mero na baki wani rubutu kisha waina tsari,shike aikawa meron ya bata yace ta baki,koya manta wani lokaci da kaina nake dauka na aika a zuwan baffa ne ya bayar,duk halin da kike ciki aysha ina sane labari yana zuwarmin,na hana 'yan uwana su daukoki kosu karboki ne gudun kada wannan abun da suja qulla har a lokacin yana nan ya zama silar barinki duniya,silar barina qauyenmu bazan iya zama ina nuna miki qiyayya sauran jama'a na nuna miki ba,sai naga gwara nayi aure a nesa,gwara nayi nesa dake,wataqila idan bakya ganina zaki haqura dani,wataqila abinda kike ji cikin zuciyarki zai ragu,kullum ta Allah sai nayi kuka akanki aysha,sai nayi kuka saboda tausayinki,kullum addu'a nake Allah yasanya duk randa zamu hadu wannan mugun abun ya warware,haduwarmu a nan zuciyata ta bani yaqinin duk wani mugun abu bai isa yayi tasiri a waje mai tsarki irin wanna ba,ki yafemin aysha....dukkan abinda ya faru ya farune bawai don ina sane ba ko inajin dadin faruwar hakan....."sai kuka ya qwace mata(a nan ina nemawa wadda ke cikin halin tsana da kyarar mahaifiyarta kamar aysha addu'a,ku sanyata a addu'a Allah yaye mata ya karkato mata da hankalin mahaifiyarta).
Rungumeta aysha tayi itama ummin ta rungumeta tsam suna kuka,sai khalipha ya kasa dauka ya miqe a hankali ya fice daga wajen,ganin haka ya sanya abba miqewa shima ya basu waje.
08030811300
57
Dukkan abinda ya faru a rayuwar aysha daga wanda ta bashi lbr kama da wanda ya faru yanzu ya dinga tariya cikin kwanyarsa,jinjina kai kawai yake,sai yaji yana son magana da anni wadda satin da zasu zo ta gama tata umarar ta wuce dubai inda ruqayya da take aure saboda haihuwa da tayi,shima yana saka ran daga nan can zasu wuce da aysha suga juna,don bata taba ganinta ba,ta kuna takura tana son ganin nata.
Suna soma magana da annin ayshan ta fito,saita koma gefa daya tana kallonshi hannayenta sarqafe da juna,wani iri so nashi da qimarshi na hauhawa cikin zuciyarta,sai yanzu ta fahimci shiya shirya komai,shiya shirya haduwarta da mahaifiyarta kamar yadda ya biya musu umara suma ya biya musu donsu hadu a nan,wanne irin mutum ne shi wanda bai gajiya da alkhairi?,wanne irin so yake mata da har kullum yake bibiye da lamuranta da dukkan mutumin daya rabeta yana aikin faranta musu?,bata dawo daga duniyar tunani ba saidaya miqa mata waya yana cewa zasuyi magana da anni,ta amshi wayar zata kai kunneta can qasa yace
"Ki rage wannan kallon da kikemin idan baso kike ki qarasa zautani ba" murmushi ta saki mai sanyi wanda yasa kumatunta lobawa,saiya shagala da kallonta sanda suke magana da anni,harta gama ta miqo masa bai sani ba
"Nima zaka zautani dinne?" 'Yar qaramar dariya ya saki yana karbar wayar
"Na gode,kin rama munyi one one ko?" Ya fadi yana dage mata gira,wani murmushin ta sake saki
"To yaya?,komai yayi normal?" Ya fada yana wara hannayenshi,kai ta gyada,sai hawaye ya soma bin fuskarta
"Ashe haka uwa take sa dadi ya khalipha?"kai ya shiga girgiza mata
"nooo...kuka kuma dai?,ashe zaki sanya na fasa barinki ki kwana wajenta da nayi niyya" idanu ta fiddo tana share hawayen
"Da gaske zaka barni?" Girarsa ya daga
"Yes,kwana daya zakiyi,amma kiyi alqawarin tanadarmin dukkan wani farinciki a sanda kika dawo ko?" Bata gane me yake cewa ba,saidai tunda yace zai barta ta kwana wajen umminta ya gama mata komai,haka kuwa akayi,ya dauki abba suka wuce nasu masaukin,suka bar uwar da diyarta suka kwana babu bacci suna hira
"Bansan irin qaunar da basma take miki ba,tun daga ranar da kikazo naqi kulaki ta daina walwala har yau" murmushi aysha tayi
"Ki barta,zanyi magana da ita da kaina gobe zan kirata" ranar haka suka kwana dungurgur a zaune aysha na bata labarin yadda ta rayu,kuka wiwiwi ummin ta dinga yi,ta rasa inda zata dora ranta,tayi alqawarin yafewa inna yelwa ne aduk sanda ta gane kurenta ta nemi afuwa banda haka data yi mata Allah ya isa,ta kuma nemi Allah ya fitar mata da haqqinta,ranar ko masallaci basu sake komawa ba,haka suka kwana tare,duk wani motsin ummin aysha na biye da ita,ko hijabinta bata bari ta dauka da kanta,yayin da ummin kebin ayshan da kallo duk inda ta motsa,tausayinya na ratsata,ta goge qwalla a boye tafi sau nawa,itakanta a karan kanta idan ta tuna yadda tabar ayshan tun batasan kanta ba sai taji dama ta tariyo baya ta goge komai,me yasa tabar musu 'yarta bayan tasan basa qaunarta?,me yasa bata tafi da 'yarta ba kome zasu ce suce,da duk wani shiri nasu bayi tasiri ba,data rayu da 'yarta tasan gatan uwa,saidai qaddara ta riga fata,hakanan bawa baya iya gujewa qaddararta,mai yiwuwa data tafi da ita din da a yau ayshan bata samu khalipha ba,da wataqila bata samu matsayin da take dashi na rayuwa ba a yanzu.
"Idan kowa bai isa alfarnar garin nan,da wanda kabarinsa ke cikin wannan waje mai albarka sun isa su sanya ki amshi diyarki"
"Abban basma.....bana so...." Sai maganar tata ta harqe
"Bana son maganar da suka fada ta tabbata akan aisha,banason ta silata wani abu ya sameta" ta fada tana sake barkewa da kuka
"Dukkaninmu ba zamu fahimci abinda kike magana akai ba idan ba bayani kika yi mana ba"
"Ammm....abba,me zai hana mu samu wani waje su zauna a can" cewar khalipha,kai abban ya gyada masa sannan ya riqe hannun ummi naja'atu dake ta kuka.
Shuru kowannensu yayi kafin abba ya daga kai ya dubi aysha
"Khalipha ya cancanci zama yaji kowanne irin abu da naja'atu xata fada,fita kice ya shigo" a sanyaye aysha ta miqe don zuwa kiranshi,saidai duka hankalinta nakan ummin,gani take kaman kafin taje ta dawo xata rasa ummin,kamar kafin taje ta dawo ummin xata sauya ra'ayi,zata fasa fada mata komai,zata fasa karbarta,itama ummin nata idanun nakan ayshan,ita kadai tasan me take hadiyewa a haka harta dawo tare da khalipha,kujerar dake daura da aysha abba ya nuna masa yace ya zauna,da fari baiso zaman ba,saboda yana ganinnkamar wani sirri ne da bai shafi yaji ba,amma abba yace ko daya,miji shine babban sirri na farko wajen matarsa,haka ya zauna kanshi da idanuwanshi a qasa yana harhada cukurkudaddiyar rayuwarsu shida ayshan waje daya
"A ranar dana bar gidan baffale a daren ba'a kwana ba akace ana sallama da baffana,yana fita baifi minti biyar ba muka jiyo hayaniya cikin zauren gidanmu,sai gashi ya dawo yace na fito ana son magana dani,ban musa ba na miqe na fito,saidai wadanda na gani a wajen inda ya gaya min su sukazo tabbas bazan fito ba,gefe daya na samu na tsaya ina dubansu,dukkan yayye da qannem baffale ne mazan sai inna yelwa
"halaa ma dai bakasan abinda ya faru ba?"cewar saya daga cikin yayyen baffale yana gayawa baffana,kai ya jinjina yace kai nake sauraro
" to mudai muna da tantamar indo diyar baffale ce gaba dayanmu,tunda cikinta bai tashi bullowa ba sai da yabar garin nan gaba daya"nan fa ran baffanmu ya baci sosai,duk haqurinshi kuwa,saidai ya hadiye yana dubansu kawai
"Me kukeson ku gayamin,nafi ku sanin wace naja"
"Ai ka tsaya malam duka na wannan ba,abu daya shine zai tabbatar mana da aisha jinin baffale ce kuma jininku" shuru kowa yayi nida baffa gaba daya muna sauraronsu,inna yelwa ce ciki izgili nuna isa da taqama tace
"Daga nan har shekaru goma dai dai da rana daya idan naja ta koda kalli indo kota sake ta nemeta toba jininmu bace,ba baffale ne mahaifinta ba,matuqar jininmu ce to babu ita babu ita,ba ruwanta da ita jininta zasu kula da ita..." Ban tsaya na qarasa saurarenta ba kawai na juya cikin gida na barsu nan da baffa na,maganar ta inna yelwa ta yimin ciwo qwarai,sharrin zina ba abinda ya kaishi muni,na shiga bacin rai sosai a sannan,na sake tsanar inna yelwa da ahalin gidanta gaba daya.
Ana tsaka da wannan saiga inna sailuba,qawar inna yelwa ce sosai,saidai ikon Allah Allah ya hada jinina da ita tana qaunata qwarai,batasan aurena ya mutu ba saboda ba'a garin take auren ba,saidaga bisani tazo ta biyo ta yimin jaje tare da nuna rashin jin dadinta akan aninda inna yelwa tayi,ranar sai gata hankalinta a tashe,ban taba ganinta cikin tashin hankali ba irin ranar,ita take gayan maganar data sake sakawa na janye jikina da.aysha,na nuna mata qyama,na farko ta gayamin inna yelwa ashe ta rabani da baffale tasa aka sanya qiyayyar juna atsakaninmu,har ya mutu yana ambatona yana neman gafarata,sannan yanzu kuma sunyi wani shiri saboda basa son hada jini dani,duk ranar dana yiwa aysha wani kallo na tausayi ko jin qai a ranar ba zata sake kwana a duniya ba,saboda suna da yaqinin babu uwar da zata daurewar azabar da suka shirya suna gana mata iri iri,banso na rasa aisha diyar dana fara samu a duniya,tilas na koyawa kaina kyararta da tsangwarta,duk da a sannan na shaidawa baffa na kafin rasuwarshi yayi addu'a sosai da rubutu,idan baki manta ba mero na baki wani rubutu kisha waina tsari,shike aikawa meron ya bata yace ta baki,koya manta wani lokaci da kaina nake dauka na aika a zuwan baffa ne ya bayar,duk halin da kike ciki aysha ina sane labari yana zuwarmin,na hana 'yan uwana su daukoki kosu karboki ne gudun kada wannan abun da suja qulla har a lokacin yana nan ya zama silar barinki duniya,silar barina qauyenmu bazan iya zama ina nuna miki qiyayya sauran jama'a na nuna miki ba,sai naga gwara nayi aure a nesa,gwara nayi nesa dake,wataqila idan bakya ganina zaki haqura dani,wataqila abinda kike ji cikin zuciyarki zai ragu,kullum ta Allah sai nayi kuka akanki aysha,sai nayi kuka saboda tausayinki,kullum addu'a nake Allah yasanya duk randa zamu hadu wannan mugun abun ya warware,haduwarmu a nan zuciyata ta bani yaqinin duk wani mugun abu bai isa yayi tasiri a waje mai tsarki irin wanna ba,ki yafemin aysha....dukkan abinda ya faru ya farune bawai don ina sane ba ko inajin dadin faruwar hakan....."sai kuka ya qwace mata(a nan ina nemawa wadda ke cikin halin tsana da kyarar mahaifiyarta kamar aysha addu'a,ku sanyata a addu'a Allah yaye mata ya karkato mata da hankalin mahaifiyarta).
Rungumeta aysha tayi itama ummin ta rungumeta tsam suna kuka,sai khalipha ya kasa dauka ya miqe a hankali ya fice daga wajen,ganin haka ya sanya abba miqewa shima ya basu waje.
08030811300
57
Dukkan abinda ya faru a rayuwar aysha daga wanda ta bashi lbr kama da wanda ya faru yanzu ya dinga tariya cikin kwanyarsa,jinjina kai kawai yake,sai yaji yana son magana da anni wadda satin da zasu zo ta gama tata umarar ta wuce dubai inda ruqayya da take aure saboda haihuwa da tayi,shima yana saka ran daga nan can zasu wuce da aysha suga juna,don bata taba ganinta ba,ta kuna takura tana son ganin nata.
Suna soma magana da annin ayshan ta fito,saita koma gefa daya tana kallonshi hannayenta sarqafe da juna,wani iri so nashi da qimarshi na hauhawa cikin zuciyarta,sai yanzu ta fahimci shiya shirya komai,shiya shirya haduwarta da mahaifiyarta kamar yadda ya biya musu umara suma ya biya musu donsu hadu a nan,wanne irin mutum ne shi wanda bai gajiya da alkhairi?,wanne irin so yake mata da har kullum yake bibiye da lamuranta da dukkan mutumin daya rabeta yana aikin faranta musu?,bata dawo daga duniyar tunani ba saidaya miqa mata waya yana cewa zasuyi magana da anni,ta amshi wayar zata kai kunneta can qasa yace
"Ki rage wannan kallon da kikemin idan baso kike ki qarasa zautani ba" murmushi ta saki mai sanyi wanda yasa kumatunta lobawa,saiya shagala da kallonta sanda suke magana da anni,harta gama ta miqo masa bai sani ba
"Nima zaka zautani dinne?" 'Yar qaramar dariya ya saki yana karbar wayar
"Na gode,kin rama munyi one one ko?" Ya fadi yana dage mata gira,wani murmushin ta sake saki
"To yaya?,komai yayi normal?" Ya fada yana wara hannayenshi,kai ta gyada,sai hawaye ya soma bin fuskarta
"Ashe haka uwa take sa dadi ya khalipha?"kai ya shiga girgiza mata
"nooo...kuka kuma dai?,ashe zaki sanya na fasa barinki ki kwana wajenta da nayi niyya" idanu ta fiddo tana share hawayen
"Da gaske zaka barni?" Girarsa ya daga
"Yes,kwana daya zakiyi,amma kiyi alqawarin tanadarmin dukkan wani farinciki a sanda kika dawo ko?" Bata gane me yake cewa ba,saidai tunda yace zai barta ta kwana wajen umminta ya gama mata komai,haka kuwa akayi,ya dauki abba suka wuce nasu masaukin,suka bar uwar da diyarta suka kwana babu bacci suna hira
"Bansan irin qaunar da basma take miki ba,tun daga ranar da kikazo naqi kulaki ta daina walwala har yau" murmushi aysha tayi
"Ki barta,zanyi magana da ita da kaina gobe zan kirata" ranar haka suka kwana dungurgur a zaune aysha na bata labarin yadda ta rayu,kuka wiwiwi ummin ta dinga yi,ta rasa inda zata dora ranta,tayi alqawarin yafewa inna yelwa ne aduk sanda ta gane kurenta ta nemi afuwa banda haka data yi mata Allah ya isa,ta kuma nemi Allah ya fitar mata da haqqinta,ranar ko masallaci basu sake komawa ba,haka suka kwana tare,duk wani motsin ummin aysha na biye da ita,ko hijabinta bata bari ta dauka da kanta,yayin da ummin kebin ayshan da kallo duk inda ta motsa,tausayinya na ratsata,ta goge qwalla a boye tafi sau nawa,itakanta a karan kanta idan ta tuna yadda tabar ayshan tun batasan kanta ba sai taji dama ta tariyo baya ta goge komai,me yasa tabar musu 'yarta bayan tasan basa qaunarta?,me yasa bata tafi da 'yarta ba kome zasu ce suce,da duk wani shiri nasu bayi tasiri ba,data rayu da 'yarta tasan gatan uwa,saidai qaddara ta riga fata,hakanan bawa baya iya gujewa qaddararta,mai yiwuwa data tafi da ita din da a yau ayshan bata samu khalipha ba,da wataqila bata samu matsayin da take dashi na rayuwa ba a yanzu.