← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 114

Sashe 18

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tunda tayi sallama hirar tata ta koma eh da A'ah,kusan ahmad ya saba da wannan halayya tata har baya damuwa,yakan ce bai taba ganin mace mara magana ba irinta,itakam saidai tayi murmushi,sun jima suna hira saidai magana ta qarshe daya gaya mata ta sanyata cikin matsananciyar faduwar gaba da fargaba har ta kasa amsa masa
"Aysha ina son a tambaya min daddy izinin zuwa wajenki,inaso na kafa gwamnatina sosai,na gaji da bulayi ta layin waya".

Sosai take jin tsoro da fargaba suna shigarta,kaman tayi tsaurin ido ko?,haka take ji zuciyarta na gaya mata,saidai wace hujja ta riqa da zata dakatar da ahmad din?,kan wannan batun sukayi sallama da ita,bai damu da jin cikakkiyar amsa daga bakinta ba,tunda ya sani magana wuya take mata.

*_BAYAN SATI DAYA_*

Xaune take dai dai cikin dakin nata gabanta cike da tarin litattafai,karatu take tuquru saboda jarabawa dake doso su.

Kiran mummy sa'adah ne ya shigo wayarta,a mamakance take kallon wayar don iya saninta indai tana cikin gidan masu aikin gidan take aikowa suyi kiranta,don ita ba ma'abociyar zaman falon gidan bace,zaiyi wuya ka sameta a falon indai ba wani abun zata yiwa mummyn daddy ko asma'u ba.

" kizo falon daddy yana nemanki"
"Toh" ta amsa,ta aje wayar cikin sanyin jiki,don tunda take zata iya irga shigarta falon daddyn,hijab ta lalubo cikin kayanta ta zura ta fice.

Yana zaune yana kallon labarai tare da shan coffe,yayin da mummy ke hakimce zaune a gafensa tana amsa wayar halimatu babbar diyarta,shi kadai ya amsa sallamar ta samu guri gefe daya ta zauna har mummy ta gama amsa waya.

"Aysha...na kira ki ne kan maganar ahmad yaron wajen hajiya laraba......sunxo sun sameni kan na bashi daman zuwa wajenki,yaya kike gani?" Ya qarashe maganar yana duban asma'u dake shigowa falon"shiru tayi kanta a qasa,rashin sabo kunya gami da tsoro suka baibayeta,shiru ya ratsa falon,yayin da agefe guda takaici ya kama asma'un,har yaushe ahmad ya soma son aysha?,yarinyar na nufin zata auri wani mai abun hannu kenan kamar ita?,sam ba zata taba bari hakan ta faru ba,sam ayshan bata cancanci shiga familyn alhj uba ba,don ta sani cewa ko su ba zasu nuna musu arziqi ba,ganin har lokacin bata ce komai ba ya sanya daddy yace
"Naga alamun kamar ba zaki sake kiyi magana sosai ba,bayan ke da asma'u duk daya kuke a wajena....shikenan kije ki duba ki gani?,idan har kin aminta da shi saiki sanarmin,ko ki sanarwa mummynku idan ma kina jin kunya saita sanarmin sarkin kunya,tashi kije koda wani abun?" kanta a qasa cikin kunyar tata ta kada kai alamun a'ah sannan ta miqe ta fice tana cewa sai da safe,duban asma'u daddy yayi
"Auta...ya akayi?" Cikin shagwaba kamar wata qaramar yarinya tace
"Daddy motata....daddy wahalar dani kawai takeyi,daddy ina buqatar canji"
"Motarki ko motarku keda aisha" mummy tayi saurin cewa don kada asma'un ta kwaba musu,itakam har ga Allah ma ta manta wai da wata aysha aka basu motar
"Yanzun ya kikeso ayi" ta samu abinda takeso,hakan ya sanya ta sake shagwabewa
"Daddy...canzata mukeso ayi mana"
"Amma baki fadi haka ayshan na nan muji nata ra'ayin ba" ranta ya baci a take,gani take kamar a yanzu aysha tafi matsayi a wajen daddyn fiye da ita,komai zaiyi tsakaninshi da ita sai ya sako ayshan,ko misali zai mata da wuya ya tsallake kan ayshan
"Banda abin daddy....ai kasan kunya gareta,ko tana nan dinma babu abinda zata ce"
"To mummyn yara" ya fada yana murmushi,shiru yayi na dan sakanni sannan yace
"Shikenan....yanzu kinsan abinda za'ayi?" Kai ta kada cikin zumudi
"Akwai wani abu da nake jira nan da qarshen watan nan,idan har komai yamin yadda nakeso,na muku alqawarin motoci ke da ayshan kowa tashi daban...kinga sai ku daina sharing haka nan" sosai albishir din ya faranta ranta,saidai ra gefe guda kuma baqin ciki nason hana murnar tata tasiri jin cewa wai ita da aysha za'a siyawa motar,bayan ita tazo ta roqi alfarmar
"Qwace goruba a hannun kuturu bazaiyi wuya ba" ta raya hakan a ranta,hakan data tuna ya sanyata warewa sosai ta yiwa daddy godiya cikin farinciki,sannan tayi musu sallama ta fice.

Saidai bata wuce dakinta ba,dakin mummyn ta koma ta zauna bakin gado tana jiranta bayan ta kunna t.v plasma tana kallo cikin tashar zee world,tasan lallai mummyn zata dawo ta shirya kafin ta koma dakin daddyn,awa guda cur kuwa saiga mummyn ta shigo,duban asma'un tayi cikin tana ciro kayan bacci
"Ya akai?,me kike har yanzu a nan baki kwanta ba?"
"Mummy....magana nakeso muyi"
"Uhmmm...ina jinki"
"Mummy....ya za'ayi ahmad din mummy laraba ya rasa yarinyar da zaice yana so da aure sai aysha?,haba mummy,wannan ai abun ayi daku ne cikin da'irar qawayenku,kuma wallahi wasu ma sai sun zageki suga kaman kin cutata masa saboda ba yaronki bane zako hadashi da wancan yarinyar da duniya bako daya ta juya mata baya ta rasa mai tallafarta sai mu"
"Na rigaki wannan hasashen,na kuma yi maganin matsalar....lokaci kawai nake jira,don duk wanda keda jibi da ni bazan taba bari ya aureta ba,bazan ce kada tayi aure ba,amma taje can ta samu dai da ita,dai dai ruwa dai dai qurji,amma familyn alhj baba ai ya tsere ma sa'anta"
"Yauwa mummy....ashe kema kin fahimci hakan...ammm sannan mummy....zancan siya mana mota tare" sai ta marairaice murya
"Mummy wallahi daddy yana saidamin mutunci ko cikin qawayenki mummy....ya za'ayi a dinga mana abu iri daya nida 'yar ruqo fisabilillahi mummy,ina laifin ya hada kudin motocin biyu ya siya min qwaya daya 2019?"
"Kina westing time dinki ne kan wannan maganar,kin riga da kin sani tunda har yayi niyyar saiya babu wata hujja da zata dakatar da shi,wancan issue din zan iya kuma zan maganinsa cikin ruwan sanyi wannan kam saidai kiyi haquri" kamar zata saki kuka tace
"Please mummy mana...ni kadaice fa kuma haka ya kamata naci gaba da kasancewa,mummy bai kamata na dinga abu iri daya da yarinyar riqon gidanmu ba,duk halaccin da muka yi mata kuma saita dinga shiga rayuwata haba mummy ki duba ki gani mana?"
"Alright,zanyi wani abu a kai,amma banso ki nuna masa komai koda ya riga daya siyo motocin"
"Thats my mom,shi yasa ko yaushe nake cewa nafi kowa sa'ar mummy a duniya"
"Uhummm,da yake nayi accepting duk abinda kike so ko?"
"Noooo mummy...duk abinda nazo da shi ai dai dai na fadi,kuma ci gaban 'yar autarki ne ko?" Ta fada tana rungume mummyn ta bayanta
"Naji ni barni na shirya wuce kije ki kwanta"
"Ok mummy,gud nyt"
"Allah ya bamu alkhairi".

Tana ratsa falon tana murmushi,duk plan dinta ya tafi yadda ta tsara yadda takeso,a rayuwa tana haushin aysha,ji take ayshan ta kai mata ko ina ta tsare mata wani abu,duk da azahiri babu wani abu da ayshan ta tsare mata,kyau irin na ayshan da sanyin hali nagarta da haquri sune abubuwan da suka tsonewa asma'un ido ba tare data san da hakan ba,a karan kanta tana ganin ayshan bata mallaki komai ba bare tayi hassada da ita,ita din ita keda komai,ita ta mallaki komai.

*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*

*DB*

13

*_BAYAN SATI BIYU_*

"Daddy game da maganar ahmad da aysha" mummy sa'adah ta fadi tana lanqwasawa daddy hular da zai fita da ita
"Uhmmm...ina jinki...tace wani abu ne?"
"Eh....maganar gaskiya yarinyar nan daddy sai nake ga kaman bata sonshi...bata fito kai tsaye ta furta ba....saidai yanayinta yadda ya nuna tana cikin damuwa,kasan kawaici irin nata ba zata fito kai tsaye ta fada ba" shiru daddyn yayi kadan yana nazari....yayin da mummy keci gaba da taimaka mishi yana shiryawa,bakinta fal da addu'ar Allah yasa zancan nata ya samu gurbi,don maganar gaskoya ba zata so ace dan hajiya larabar ya auri ayshan ba,ko don kare qimarsu a idanun sauran qawayensu
"Bari naje na dawo...sai muyi maganar"
"Shikenan.....amma dai gaskiya daddy kar muyi abinda zamu cutar da yarinyar,kaga tamkar amana ce a wajenmu"
"In sha Allah" yace mata.

Tana zaune cikin kujerun roba dake tsakiyar flowers din da aka qawata gidan da su,cikin kwanakin duk ta takure kanta saboda jarabawa,hakan ya sanya bata da wani cikakken lokacin kanta,tana jin bata da wani gata daya wuce karatun shi yasanya ba zatayi wasa da damarta ba,ta sani cewa duk randa ta kammala karatunta zaiyi wuya idan ba qauyensu zata koma ba,don bata ga wani dalili da zai ci gaba da zaunar da ita cikin gidan ba tana zame musu nauyi bayan duka dimbin halaccin da sukayi tsawon shekaru suna yi mata,don haka ba zatayi wasa da damarta ba,zata tsaya tsayin daka taga ta samu abinda ta samu wanda zata tsira da shi koda ta komawa can din.

Ko kadan bata ji tahowarshi ba saboda yadda hankalinta yayi gaba,daddyn shi ya soma ganota,a nutse ya karanceta,sai yaga ta rame din,wanda yake a badini karatun da take tuquru ne ya kawo hakan,bai mata magana ba ya wuce ganin tayi nisa cikin karatun ta.

Qarar bude get da fitar motar daddyn ita ta dawo da ita,ganin ya riga daya fice saita maida kanta taci gaba da karatunta.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶

Qarfe sha biyu na rana yayi sallama da anninsa a filin tashi da saukan jirgin saman malam aminu kano,wadda zata wuce saudiyya don yin umara,shi da sulaiman da farouq suka rakata suka juyo,kan hanyarsu ta komawa company ya bawa drivansu umarnin su wuce jami'ar bayero don yiwa wani abokinsa zuwan na zata,Dr mansur amini ne da har gobe khalipha baya mance halaccinsa a gareshi,hakan ya sanya yake matuqar girmamashi.

Duk inda motocin su suka ratsa sai idanu sunyi kansu saboda kyau da yadda suke daukar idanu,guri na musamman suka aje motocin nasu,yana yunqurin fitowa ya hango tahowarta daga nesa,cikin hanzari ya maida qafarshi tare da rufe murfin motar,ta cikin baqin gilashin motar ya zuba mata idanu har tazo ta wuceshi bata sani ba,su uku ne ita da wasu yammata kamarta da alama qawayenta ne,sai data wuce sannan ya fito suka nufi office din DR kai tsaye.
Chapter 18 · 0% Book details